10/05/2025
SANARWA:
Isar da sakon Allah Madaukakin sarki da Manzon Allah (S.A.W) ga Al'ummar Musulmin duniya
10/05/2025
SANARWA:
29/03/2025
Manzon Allah (SAW) ya ce, “Duk wanda bai bar maganganun karya, da munanan ayyuka, da munanan maganganu ga mutane ba, To Allah ba ya bukatar barin cinsa da shansa (Azumi)”. [Sahih al-Bukhari 6057]
27/03/2025
Manzon Allah (S.A.W) ya ce: "Kada ku kyamaci junanku, kada ku yi ma junanku hassada, kuma kada ku guje wa juna. Ya ku bayin Allah, ku kasance 'yan'uwa! Hakika Ba ya halatta ga musulmi ya ki magana da dan'uwansa (Muslim) fiye da darare uku." [Al-Adab Al-Mufrad 398]
24/03/2025
Nana A’isha (R.A) ta ce: “Ya Manzon Allah (S.A.W), me zan yi addu’a idan na kasance a daren lailatul qadri?” Sai Manzon Allah (S.A.W) ya ce: “Ki ce, Ya Allah, Kai mai yawan afuwa ne, kana son yin afuwa, ka gafarta mani”. [Tirmidhi 3513]
21/03/2025
19/03/2025
Manzon Allah ﷺ ya ce: “Allah mai Girma da daukaka ya ce: “Ni ne Mai rahama (ar-Rahman) Ni ne na halicci zumunta kuma na samar da sunan daga sunana, Hakika duk wanda ya kulla zumunta to zan kulla alaka da shi, kuma zan yanke alaka da duk wanda ya yanke zumunta".
[Sunan Abu Dawud]
16/03/2025
Manzon Allah (S.A.W) Yace: "Ina rantsuwa da wanda raina ke hannunSa! Ba za ku shiga Aljanna ba har sai kun yi imani, kuma ba za ku yi imani ba har sai kun so junanku. Shin in ba ku labarin wani al'amari wanda idan kuka aikata shi za ku so junanku? Ku yada sallama a tsakanin juna." [Sahih Muslim]
15/03/2025
Manzon Allah (S.A.W) Yace: "Wanda duk yayi kira zuwa ga shiriya, to yana da lada kwatankwacin ladan wanda s**a bi shi, ba tare da tauye wani abu daga ladansu ba, haka zalika wanda duk yayi kira zuwa ga bata, to yana da zunubi kwatankwacin zunubin wadanda s**a bi shi, ba tare da an rage komai daga zunubansu ba."- [Sahih Muslim - 2674]
14/03/2025
Manzon Allah (S.A.W) Yace: "ku tseratar da kawunanku daga shiga wuta da bayar da rabin dabino na sadaka, idan ba ku sami rabin dabino ba, to ku furta kalma mai daɗi ga ƴan'uwanku". [Sahih Bukhari]
12/03/2025
Manzon Allah (S.A.W) Yace: "Dabi'u guda biyu Allah baya tattarasu ga mumini, sune rowa da mummunar dabi'a". (Sahih Bukhari)