Sayyadi Sunusi Yusuf Khalifa

Sayyadi Sunusi Yusuf Khalifa

Share

Isar da sakon Allah Madaukakin sarki da Manzon Allah (S.A.W) ga Al'ummar Musulmin duniya

10/05/2025

SANARWA:

29/03/2025

Manzon Allah (SAW) ya ce, “Duk wanda bai bar maganganun karya, da munanan ayyuka, da munanan maganganu ga mutane ba, To Allah ba ya bukatar barin cinsa da shansa (Azumi)”. [Sahih al-Bukhari 6057]

27/03/2025

Manzon Allah (S.A.W) ya ce: "Kada ku kyamaci junanku, kada ku yi ma junanku hassada, kuma kada ku guje wa juna. Ya ku bayin Allah, ku kasance 'yan'uwa! Hakika Ba ya halatta ga musulmi ya ki magana da dan'uwansa (Muslim) fiye da darare uku." [Al-Adab Al-Mufrad 398]

24/03/2025

Nana A’isha (R.A) ta ce: “Ya Manzon Allah (S.A.W), me zan yi addu’a idan na kasance a daren lailatul qadri?” Sai Manzon Allah (S.A.W) ya ce: “Ki ce, Ya Allah, Kai mai yawan afuwa ne, kana son yin afuwa, ka gafarta mani”. [Tirmidhi 3513]

21/03/2025
19/03/2025

Manzon Allah ﷺ ya ce: “Allah mai Girma da daukaka ya ce: “Ni ne Mai rahama (ar-Rahman) Ni ne na halicci zumunta kuma na samar da sunan daga sunana, Hakika duk wanda ya kulla zumunta to zan kulla alaka da shi, kuma zan yanke alaka da duk wanda ya yanke zumunta".
[Sunan Abu Dawud]

16/03/2025

Manzon Allah (S.A.W) Yace: "Ina rantsuwa da wanda raina ke hannunSa! Ba za ku shiga Aljanna ba har sai kun yi imani, kuma ba za ku yi imani ba har sai kun so junanku. Shin in ba ku labarin wani al'amari wanda idan kuka aikata shi za ku so junanku? Ku yada sallama a tsakanin juna." [Sahih Muslim]

15/03/2025

Manzon Allah (S.A.W) Yace: "Wanda duk yayi kira zuwa ga shiriya, to yana da lada kwatankwacin ladan wanda s**a bi shi, ba tare da tauye wani abu daga ladansu ba, haka zalika wanda duk yayi kira zuwa ga bata, to yana da zunubi kwatankwacin zunubin wadanda s**a bi shi, ba tare da an rage komai daga zunubansu ba."- [Sahih Muslim - 2674]

14/03/2025

Manzon Allah (S.A.W) Yace: "ku tseratar da kawunanku daga shiga wuta da bayar da rabin dabino na sadaka, idan ba ku sami rabin dabino ba, to ku furta kalma mai daɗi ga ƴan'uwanku". [Sahih Bukhari]

12/03/2025

Manzon Allah (S.A.W) Yace: "Dabi'u guda biyu Allah baya tattarasu ga mumini, sune rowa da mummunar dabi'a". (Sahih Bukhari)

Want your school to be the top-listed School/college in Zaria?

Click here to claim your Sponsored Listing.

Location

Category

Website

Address


Sabon Garin Zaria
Zaria