Kaura zaria city

Kaura zaria city

Share

Kaura is a dynasty BAREBARI, is a very historic Place in Zazzau that produced morethan Emirs of the Great Emirate of Zazzau than any other clan.

23/05/2026

Yau 23rd May 2026 Maigirma Walin Zazzau Amb. Lawal Sambo ke cika shekara 15 da rasuwa.

Tabbas wannan Babban rashi ne da har yanzu baa samu Wanda ya cike gurbin SA ba.

Muna rakon Allah ya kyautata makwansa, tare da sauran Al'umma musulmi Baki daya.

22/05/2026

INNALILLAHI WA'INNA ILAIHIN RAJ'UN

ALLAH yayi ma Salisu Abubakar Datti na Gidan Mai Anguwa Datti, Bayan fama da rashin lafiya.

Lokacin Sallah Jana'izan 2:00Pm
Wuri :- Masallacin Fada, Bayan Sallah Jumma'a

ALLAH ya Gafarta Mashi ya Bashi Aljannah Firdausi da Sauran Musulmi Gaba Ɗaya.

17/05/2026
16/05/2026

TARIHIN SHUGABAN LIKITOCI (CHIEF MEDICAL DIRECTOR)

An haifi Farfesa Musa Tabari a watan Yuni na shekarar 1969 a tsohon birnin Zariya, ƙaramar hukumar Zariya ta Jihar Kaduna. Ya yi karatunsa na firamare a makarantar L.E.A. Primary School da ke cikin birnin Zariya tsakanin shekarun 1974 zuwa 1980. Daga nan ya halarci makarantar Alhudahuda College da kuma Government Day Secondary School Zaria tsakanin shekarun 1980 zuwa 1983 da kuma 1983 zuwa 1985 domin karatun sakandare na ƙasa da babba.

Ya ci gaba da karatu a School of Basic Studies (SBS) da kuma Faculty of Medicine na Jami’ar Ahmadu Bello da ke Zariya tsakanin shekarun 1985 zuwa 1992, inda ya rubuta kuma ya ci jarabawar IJMB wadda ta ba shi damar shiga karatun likitanci. Daga nan ya kammala karatu tare da samun digirin MBBS (Bachelor of Medicine,

Bachelor of Surgery) daga wannan babbar jami’a ta Ahmadu Bello University, Zariya.
Ya yi aikin horaswar likita na shekara guda (Housemanship) a tsohuwar Ahmadu Bello University Teaching Hospital (ABUTH) Kaduna daga shekarar 1992 zuwa 1993. Bayan haka ya yi bautar ƙasa ta NYSC a cibiyar kula da lafiya ta Primary Health Centre da ke Odot a Jihar Akwa Ibom tsakanin shekarun 1993 zuwa 1994.
Saboda ƙwazonsa da sha’awarsa ga ilimi, Farfesa Musa Tabari ya ci gaba da karatun digiri na gaba da na ƙwarewa a University of Ilorin Teaching Hospital (UITH), Ilorin, Jihar Kwara, inda ya yi horon ƙwarewa a fannin Radiology tsakanin shekarun 1998 zuwa 2002. Wannan ya sa ya samu Fellowship na Faculty of Radiology daga National Postgraduate Medical College of Nigeria (NPMCN).

Haka kuma ya samu ƙarin horo na musamman bayan Fellowship a Uniformed Services University of Health Sciences (USUHS) / National Naval Medical Centre, Bethesda, Maryland, Amurka a shekarar 2004, a fannin Tropical Imaging. Ya kuma ƙware sosai a fannin Vascular and Interventional Radiology a Medical University of Graz / LandeskrankenHaus na ƙasar Austria a shekarun 2009 da 2011, sannan a All India Institute of Medical

14/05/2026

Big shout-out to my newest top fans! Saeed Ibrahim Maryam, Mars Musty, Adamu Ibrahim, Yariman Fcbk Maiwada, Muhammad Musa Yero, Lawal Umaru Abdulsalam, Bello Ahmad, Sirajo Yahaya Pate, Suleiman Abdullahi Kaura

14/05/2026

MARIGAYI ALHAJI MUHAMMADU DAN SALANKE

Wannan Bawan Allah shi ne Marigayi Alhaji Muhammadu Dan Salanke, babban ɗa ga Marigayi Mai Shari’a Malam Abdullahi (Salanken Zazzau II). Mutum ne nagari, mai hakuri, taimako da son jama’a wanda ya rayu cikin mutunci da hidima ga al’umma.

Marigayin ya yi aiki a ƙananan hukumomi daban-daban na Jihar Kaduna a matsayin Malamin Asibiti, inda ya sadaukar da rayuwarsa wajen yi wa jama’a hidima cikin gaskiya da riƙon amana. Ya kammala aikinsa lafiya a matsayin shugaban ma’aikata (H.O.D) a Sabon Gari Local Government, Zariya.

Haka kuma, yana daga cikin zuriyar Muhammadu Danga dake Anguwan Kaura, Zaria City, gida mai tarihi da mutunci a ƙasar Zazzau. Muna addu’ar Allah Maɗaukakin Sarki Ya jikansa da rahama, Ya gafarta masa kura-kuransa, Ya sanya Aljannatul Firdausi ta zama makomarsa. Allah Ya sanya ya huta cikin rahama da hasken kabari, Ya albarkaci zuriyarsa da dukkan waɗanda ya bari a baya.
Amin thumma Amin.

14/05/2026

INNA LILLAHI WA INNA ILAIHI RAJI’UN

Yanzu muke samun labarin rasuwar Babba Asiya. Allah Ya yi mata rahama da gafara, Ya sanya Aljannatul Firdausi ce makomarta.
Za a gudanar da jana’izarta da misalin ƙarfe 5:30 na yamma a Kofar Gidan Mai Gwanjo.
Muna addu’ar Allah Ya jikanta da rahama, Ya yafe mata kura-kuranta, Ya bai wa iyalanta da dangi haƙurin jure wannan babban rashi.
Amin Ya Allah.

13/05/2026

With Kaura zaria city – I've just made it onto their weekly engagement list by being one of their top engagers!

Want your school to be the top-listed School/college in Zaria?

Click here to claim your Sponsored Listing.

Location

Category

Telephone

Website

Address


Kaura Zaria City
Zaria
22222