21/08/2026
Alamomin Annabtar Manzon Allah SAW.
Farkon alamar Annabtar Manzon Allah SAW da ake iya gani itace: tsaga girjinsa mai girma da akayi. An tsaga ƙirjin Manzon Allah SAW sau huɗu a rayuwar sa SAW.
1. Lokacin yana ƙaramin shekaru a wurin Halimatus Sa'adiyyah.
2. Lokacin yana shekara goma.
3. An tsaga ƙirjin sa a lokaci da Mala'ika Jibrilu ya fara zuwa masa da Wahayi.
4. A daren Isra'i da Mi'iraji kamar yadda yazo a Hadisai.
Alamar Annabta ta biyu shine: Khatamun Nubuwwa ( Hatimin Annabta) wata alama ce ko tsoka ce ta ɗago a allon kafadar sa na gefen hagu tana feshin haske da kwarjini da kamshi wanda yake nuna alamar cewa shi Annabin Allah ne SAW.
Alama ta uku itace : Al'ru'uyas Saliha wato Kyakkyawan Mafarki ko Mafarkin gaskiya. Manzon Allah SAW ya kasance yana yin mafarki kuma sai abunda ya gani a mafarkin nan yaz kamar hasken safiya, yana ganin haske kuma yanajin sauti kuma duk abunda yagani a mafarki shine ke faruwa a zahiri.
Yana daga cikin alamomin Annabtar sa: Duwatsu da bishiyoyi sunayi masa sallama kuma girgije nayi masa inuwa.
Allah ya bamu albarkacin Manzon Allah SAW.
Ya Allah ka bawa mahaifiyata lafiya dan darajar Manzon Allah SAW.
20/08/2026
Karmu mance da yawaita yima Annabi SAW salati a wannan daren na Juma'a da kuma ranar Juma'a kuma cikin watan Maulud
20/08/2026
Innalillahi wa'inna ilaihir raji'un
Muna miƙa saƙon ta’aziyyar wafatin Maulana Khalifa Gali Bn Maulana Sheikh Yahuza Zaria. Allah Ya gafarta masa, Ya haskaka kabarinsa, Ya sanya iliminsa da ayyukansa su zama sadakar jariya. Allah ya bamu hakurin wannan babban rashi, kuma Ya sanya Aljannar Firdausi ta zama makomarsa ya sada shi da Manzon Allah SAW.
20/08/2026
Yabo ga Mahaifin Manzon Allah SAW.
Ya mahaifin Manzon Allah SAW, ka cimma dukkanin wata girma.
Ka zo da alkhairi ga waɗanda s**a gabata da waɗanda za su zo.
Ba a taɓa samun wata falala kamar wacce ka samu ba, kuma ka haɗa
dukkan alfahari da yabo a cikin ɗa mai cikakkiyar ɗabi'a.
Lalle ne ka yi fice a kan iyayen da s**a gabata ta fuskar daraja,
da girma, yabo da kyakkyawan suna a sammai.
20/08/2026
Wannan gaskiya ne a saki Maulana Sheikh Sani Khalifa na take.
20/08/2026
Sunayen Manzon Allah SAW
Daga cikin sunayensa SAW da s**a zo acikin Alqur'ani akwai: Bashirun Nazirun Sirajun Munirun, Ra'ufun Rahimun, Rahmatun Lil-Alamin, Muhammadun, Ahmadu, Ɗaha, Yasin, Muzammilun, Mudassirun, Abdullahi, Nazirun Mubinun, Muzakkirun, Nurun da sauran su
Manzon Allah SAW yana cewa: Nine Muhammad kuma nine Ahmad kuma nine AlMahiy wanda Allah zai shafe kafirci dani, Kuma nine Hashiru wanda Allah zai tara mutane a bayana, kuma nine Al'Aqibu wanda babu Annabi a bayana kuma nine AlMuqaffah kuma Annabin-Tuba kuma Nine Annabin-Rahama Sallallahu alaihi wa Alihi Wasallam.
Allah kabawa mahaifiyata lafiya da dukkan sauran marasa lafiya lafiya Albarkar Manzon Allah SAW.
19/08/2026
Nagode da Addu'o'in ku ga mahaifiyata.
Allah ya bar zumunci alfarmar Manzon Allah SAW
19/08/2026
Dan Allah ku saka mahaifiya ta a addu'a, bata da lafiya.
😭
19/08/2026
Rayuwar Manzon SAW kafin aiko shi.
Manzon Allah SAW ya kasance kafin aiko shi da Manzanci; Ma'abocin addini, mai ladabi da biyayya da girmama manya. Bayason gumaka kuma baya son duk wani haram. Bai taba shan giya ba b***e yima gunki sujjada kuma baya zuwa duk inda ake aikata ba daidadi ba.
Ya kasance yana Kiwon tumakin mutanen Makkah suna biyanshi, kuma yana kasuwanci, kuma ya kula da kasuwancin Nana Khadijah suna zuwa gari-gari kasuwanci tare da yaron Nana Khadija mai suna Maisarah lokacin yana Shekara 25, s**a dawo da riba mai yawa.
Halin ruqon Amanan shi ne ya sanya Nana Khadijah taji tana so ta aure shi bayan da aka mata bushara da cewa shine Annabin karshen zamani.
Manzon Allah SAW ya kasance mai ruqon amana har ya kasance mutanen Makkah suna bashi ajiyan dukiyoyin su, har s**ai masa laqabi da Al'ameen Amintacce.
18/08/2026
Wanda ya jingina zuciyarsa ga Masoyi, Annabi Muhammad ﷺ, ba ya taɓa tashi da asara. Haka kuma wanda ya dawwama a ƙofar Annabi SAW