19/06/2026
ANA NEMAN ƳAN UWAN WANNAN MUTUM!
Sojojin Najeriya sun ceto wani bawan Allah daga hannun ƴan bindiga a dajin Matazu da ke Jihar Katsina.
A halin yanzu, ana roƙon duk wanda ya san wannan mutum ko iyalansa da ya taimaka wajen isar da wannan saƙo domin a haɗa shi da ƴan uwansa cikin gaggawa.
Allah Ya ci gaba da kare al'ummar Najeriya tare da kuɓutar da sauran waɗanda ke hannun masu garkuwa.
📍 Majiyar labari: Abba Sani Pantami
19/06/2026
Muna kira ga Masu Gidan Ruwan Pure water na NA'EEMULLAH da su dena rubuta wannan suna a jikin ledar Ruwansu, domin akwai sunan Allah karara a jiki, kuma idan an shanye ruwan leda kowa yasan jefar da ita ake ako ina, Bola, kwata ,hanya da sauran gurare masu kazanta. Dole mu Girmama Sunan Ubangiji a kowane Hali.
Daga Ali zubairu
18/06/2026
DA ƊUMI-ƊUMINSA: EFCC Ta Yi Awon Gaba Da Wani Limamin Coci Kan Zargin Damfarar Mambobin Cocinsa Sama da Miliyan ₦70.3
Hukumar EFCC ta k**a wani limamin coci bisa zargin damfarar wasu daga cikin mambobin cocinsa kuɗaɗe da s**a kai Naira miliyan 70.3.
Ana sa ran za a gurfanar da wanda ake zargin a gaban kotu bayan kammala binciken da hukumar ke gudanarwa.
Ku biyo mu domin samun sahihan labarai cikin gaggawa.
Umd news hausa
18/06/2026
Zafafan Kalamai Daga Trump Kan Najeriya!
Yanzu da rikicin Gabas ta Tsakiya ya lafa, hankalinmu zai koma Nahiyar Afirka, musamman Najeriya da ke shirin gudanar da zaɓen 2027. Na samu rahotannin da ke nuna ana muzgunawa jam'iyyun adawa, kuma ina aika gargaɗi mai ƙarfi ga duk masu hannu a lamarin. — Trump.
Wannan furuci ya jawo ce-ce-ku-ce da martani daga sassa daban-daban, yayin da ake ci gaba da sa ido kan yadda siyasar Najeriya ke tafiya gabanin zaɓen 2027.
17/06/2026
Wannan Shi Ne Martanin Davido Da Ya Dauki Hankalin Jama'a Bayan Bidiyon Rarara Ya Karade Kafafen Sada Zumunta!
Fitaccen mawakin Najeriya, Davido, ya jawo ce-ce-ku-ce a shafukan sada zumunta bayan ya wallafa kalma guda kacal, "Debidooo 😭", a matsayin martani ga wani bidiyon mawakin siyasa Rarara.
Martanin ya bazu cikin sauri, inda dubban mutane s**a yi ta tofa albarkacin bakinsu kan abin da Davido yake nufi da wannan sako nasa.
Wasu na ganin martanin na nuna dariya ne da nishadi, yayin da wasu ke kallonsa a matsayin wata alama ta mamaki game da bidiyon da aka yada.
Yanzu haka dai wannan martani ya zama daya daga cikin abubuwan da s**a fi daukar hankali a kafafen sada zumunta, tare da jawo muhawara daga mabiyan mawakan biyu.
👇 Mene ne ra'ayinka kan martanin Davido? Ka bayyana a sashin sharhi.
15/06/2026
Da duminsa: Rahotanni sun tabbatar da cewa dakarun Operation Fansan Yamma sun yi nasarar ceto matar marigayi Manjo-Janar Rabe Abubakar (Rtd), wadda aka yi garkuwa da ita tare da marigayin.
An ce marigayin ya rasu ne a hannun 'yan bindigar bayan shafe lokaci a tsare. Ceton matarsa ya zo a matsayin wani abin farin ciki ga iyalansa da al'ummar da ke bibiyar wannan lamari mai tayar da hankali.
Muna addu'ar Allah Ya jikansa da rahama, Ya gafarta masa kura-kuransa, Ya kuma ba iyalansa hakurin jure wannan babban rashi.
13/06/2026
Gwamnatin Jihar Katsina ta sanar da rasuwar Manjo-Janar Rabe Abubakar (Rtd), wanda ya rasu yayin da yake hannun 'yan bindiga duk da ƙoƙarin da gwamnati da hukumomin tsaro s**a yi na ganin an kuɓutar da shi cikin koshin lafiya.
A cewar sanarwar da Kwamishinan Tsaro na Cikin Gida, Dr. Nasiru Mu'azu, ya fitar, marigayin ya rasu ne sak**akon matsalolin lafiya da s**a haɗa da ciwon s**ari da hawan jini, yayin da yake tsare a hannun masu garkuwa da mutane.
Gwamnan Jihar Katsina, Dikko Umaru Radda, ya bayyana alhininsa kan wannan babban rashi, inda ya jajanta wa iyalan marigayin tare da jaddada aniyar gwamnatin jihar na ci gaba da haɗa kai da gwamnatin tarayya da hukumomin tsaro domin kawo ƙarshen matsalar 'yan bindiga da tabbatar da hukunta masu hannu a irin waɗannan munanan laifuka.
Allah Ya jiƙan Manjo-Janar Rabe Abubakar (Rtd), Ya gafarta masa kura-kuransa, Ya sanya Aljannatul Firdausi ta zama makomarsa. Allah Ya bai wa iyalansa da al'ummar Katsina haƙurin jure wannan babban rashi.
Matsalar tsaro na ci gaba da karɓar rayukan manyan mutane da talakawa a ƙasar nan, lamarin da ke buƙatar ƙarin matakan gaggawa domin kare rayuka da dukiyoyin al'umma.
09/06/2026
INNA LILLAHI WA'INNA ILAIHI RAJI'UN
Ɗaya daga cikin dattawan da aka yi garkuwa da su a Jihar Kebbi ya rasu a hannun masu garkuwa da mutane.
Ƙungiyar JIBWIS (Izalah) reshen ƙaramar hukumar Koko-Besse a Jihar Kebbi ta sanar da rasuwar shugaban reshen, Malam Yahaya Billi, wanda ke cikin waɗanda aka yi garkuwa da su.
A cewar sanarwar da ƙungiyar ta fitar, za a gudanar da Sallar Jana'izar Salatul Ga'ib ga marigayin da misalin karfe 4:30 na yammacin yau, a ƙofar gidan Sarkin Koko.
Muna roƙon Allah Maɗaukakin Sarki Ya gafarta masa kura-kuransa, Ya yalwata masa rahama, Ya sanya Aljannatul Firdausi ta zama makomarsa, sannan Ya bai wa iyalansa da al'ummar Musulmi juriyar wannan babban rashi.
Allah Ya kuɓutar da sauran waɗanda ke hannun masu garkuwa da mutane cikin koshin lafiya.