Mallm Kabiru lawal Garba zai kasance tare da mu a garin Zaria domin gabatar da karatun daurar littafin Aqeedar Al-Imaamul Bukhary ranar Jumaa 7 ga wannan watan. Za a fara bayan la'asar zuwa magriba sai kuma washe gari asabar a cigaba kuma a karkare a ranar insha Allah.
wuri;; Tsauni Sabon Gari Zaria masallacin mallam Yahuza.
Sai kuma muhadara da mallam zai gabatar da asubahin ranar asabar mai taken Da'awar Gaskiya a masallacin markazul Khayr Dogarawa Sabon gari Zaria.
Allah ya ilmantar da mu abin da zai anfanar da mu ya anfanar damu da abin da ya ilmantar da mu ya kuma karfafe mu wurin bin tafarkin Annabi saw da sahabban sa da magabata na kwarai.
Sahaabus Salafiyyah
Assalamu alaykum
10/03/2024
Masjid al-Hijrah, Soro, Ganjuwa LGA, Bauchi State, Nigeria.
Ayyukan Watan Ramadan Na Masallaci Mai Suna A Sama
Tafsirin Ƙur’ani:
Gabatarwa: Dr. Ibrahim Lawal Soro (H) Tare Da Alr. Ahmad Ibrahim (H)
Lokaci: 1:30 PM – 20:30 PM
Ramadaniyyat:
Waɗannan Jerangiyar Muhadarori Ne Dr. Ibrahim Lawal Soro (H) Zai Rinqa Gabatarwa A Kowace Rana A Cikin Watan Ramadana Daga 9:00 PM – 10:00 PM A Shafinsa na Facebook mai suna: Sheikh Dr. Ibrahim Lawal Soro.
Taken Muhadarori:
1. Azumin Ramadan Mai Armashi Da Sabubansa.
2. Ƙira Zuwa Ga Tauhidi Tsakanin Gaskiya Da Qarya.
3. Muhimman Bambance-Bambance Tsakanin Salafiyyah Da Sururiyyah A Nigeria.
4. Siyasantar Da Addini A Fagen Da’awah A Nigeria.
5. Alamomin Gaskiyar Maqirayi (Mai Da’awah) 6. A Wajen Gama-Garin Musulmai A Nigeria.
7. Tasirin Ƙungiyar Ikhwan Al-Muslimin Ga Ƙungiyoyin Da’awah A Nigeria.
8. Taƙaice Littafin “الهدية الهادية إلى الطائفة التجانية” (Gabatacciyar Kyauta Zuwa Ga Dariqar Tijjaniyyah) na Dr. Taqi al-Din al-Hilali (R.A).
9. Aƙidar Biyayya Ga Mahukunta Da Martani Ga Waxanda S**a Sava Mata.
10. Tsakure Daga Cikin Littattafan Sheikh Ihsan Ilahi Zahir A Kan Shi’ah Da Shi’anci.
11. Fassarar Nasihar Sheikh Sa’id Maikwano Ga Dr. Idris Abdul-Aziz Dutsen Tanshi.
12. Tushen Matsalar Dr. Ahmad Gumi Da Hanyoyin Magance Ire-Irenta.
13. Ɗalibta Da Sabbin Qalubalenta (Social Media A Matsayin Misali).
14. Batun Tattalin Arziƙin Musulunci: Wasu Keɓantattun Ra’ayoyi.
15. Rîba da Ribà: Da Sauran Rina A Kaba.
16. Kangara Da Sharrinta: Misalai Daga Suratu Hud.
17. Dabarun Neman Arziqi Da Cin Moriyarsa A Zamanance.
18. Uzuri Da Jahilci: Haƙiƙarsa Da Maganganun Malamai A Kansa.
19. Haƙurin Mai Da’awah Da Tasirinsa Ga Nasarorinsa: Misalai Daga Rayuwar Magabata Na Ƙwarai.
20. Shirkar Da Take Kore Tauhidi Da Ɓangarorinta A Wajen Sheikh Muhammad Ibn Abdulwahab (R.A).
21. Hukunce-Hukuncen Sababi Da Batun Nema A Musulunci
22. Wasiyoyi Talatin (30) A Bisa Manhajin Annabta.
23. Albarka Da Nau’ukanta, Da Sabuban Samuwarta Ko Rashinta.
24. Misalai Daga Ɗabi’un Manzon Allah (S.A.W).
25. Arziƙi Da Sabubansa.
26. Tsigale Haɗin Kai A Manhajin Ikhwan Al-Muslimin.
27. Dabarun Tattalin Budurci Har Zuwa Lokacin Aure Da Kura-Kuran Daren Angonci.
28. Wasu Ƙa’idojin Tafarkin Annabta.
29. Fassarar Littafin “وظائف يوم العيد” (Ayyukan Ranar Idi) Na Dr. Kabir Lawal Garba (H).
Saƙonnin Juma’ah:
Jerin muhadarori ne waxanda Dr. Ibrahim Lawal Soro (H) ya saba gabatarwa a bayan kowace sallar Juma’ah a cikin watan Ramadan.
Juma’ah Ta Farko:
Karin maganar Bahaushe “Noma Tushen Arziƙi” a Mahangar Shari’ar Musulunci.
Juma’ah Ta Biyu:
Hassada Da Illolinta Ga ƊaiƊaiku Da Al’ummah.
Juma’ah Ta Uku:
Ma’aunin Soyayya Da Ƙiyayya A Musulunci.
Juma’ah Ta Huɗu:
Bankwana Da Watan Ramadan: Wasu Muhimman Darrusa Ga ƊaiƊaiku Da Al’ummah.
TAHAJJUD:
An saba gabatar da Tahajjud a wannan Masallaci, kuma za a ci gaba da gabatarwa a wannan shekara –In sha Allah-.
Lokaci: 01:00 PM – 02:00 PM
Allah Ya Ba Mu Ikon Aiwatarwa, Kuma Ya Ba Ku Ikon Halarta!
Kungiyar izalah kungiya ce karkatacciya ,shiyasa Basu iya barranta kansu daga Dan bidi'ah matukar zasu anfana da shi ko matsayin shi acikin tafiyar su.
Shiyasa har gobe Dr Ahmad Abubakar gumi Yana cikin tafiyar su.
Ka barrantar da kanka daga wanna kungiya idan ma'abocin Sunnah kake son zamantowa.
26/8/1445
7/3/2024
صديق أحمد أبو بكر
Dr. Ahmad Gumi Da Wasu Masu Yi Masa Martani
Dr Ibrahim Lawal Soro
(Tsohuwar Ajiya, 12. 07. 2019 CE)
Inda irin wannan ruwan martanoni da aka yi wa Dr. Ahmad Gumi za a yi wa mabarnata irinsa, musamman masu kokarin kautar da mutane gabarin Tafarkin Magabata a akida da Manhaji, lallai da kowa ya shiga taitayinsa, amma abin mamaki galibin wadanda s**a jagoranci wasu martanonin sun yi daidai da shi a kan kangare wa ra'ayi da son zuciya tare da bayyanar gaskiya gare su.
Allah ya rufa asiri.
Tsakanin Dr. Ahmad Gumi da Sayyid Qutb da Izalah da Ikhwan al-Muslimeen
*Dr Ibrahim Lawal Soro*
(Tshohuwar Ajiya, 30. 07. 2017 CE)
Bana tsakkar samuwar barbarar tunani da k**anceceniya a tsakanin Dr. Ahmad Gumi da Sayyid Qutb, k**ar yadda aka samu tsakanin Kungiyar Izalah da Ikhwan al-Muslimeen, daga cikin abubuwan da za su bayyana maka haka akwai:
1. Sayyid Qutb Bakhawarije ne a bangaren mu'amala da mahukunta, haka da Dr. Ahmad Gumi, kurarinsa na fin karfin gwamnati da gagararta bai yi nisa gabarinka ba.
2. Sayyid Qutb Bamu'utazile ne dangane da al'amuran da s**a shafi qaibi; yana gabatar da hankali a kan nakali, haka ma Dr. Ahmad Gumi, domin yana kore shigar Aljani a jikin Dan Adam, kuma yana karyata tasirin sihiri da sauransu.
3. Sayyid Qutb mazagin Sahabban Manzon Allah [R. A] ne, ya zagi 'Uthmaan Bn 'Affaan da Mu'aawiyah Bn Abee Sufyaan [R. A], k**ar yadda Dr. Ahmad Gumi ya sa Mu'adh Bn Jabal [R. A] da cin mutunci.
4. Duk irin aika-aikar Sayyid Qutb da bidi'o'insa kungiyar Ikhwaan al-Muslimeen da ya kasance jigo a cikinta ba ta taba furta kalma ta barranta da shi ba, k**ar yadda Kungiyar Izalah ba ta taba jefar da kalma da nisantar da kanta gabarinsa Dr. Ahmad Gumi a kungiyance ba, kuma martanin wasu malaman kungiyar gare shi ba ya wakiltar kungiyar a zahiri, shi ya sa tasirinsa ya yi karanci a wajen Yan Kungiyar da suke ganinsa har yanzu a matsayin Malaminsu.
5. Matukar mutum ya yi imani da tsare-tsaren Kungiyar Ikhwaan al-Muslimeen da manufofinta shi kenan, domin ba ta damuwa da akidah da tafarkin da yake dauke da ita, hakika irin wannan salo Kungiyar Izalah ta k**a, musamman a baya-bayan nan, batun Dr. Ahmad Gumi bai yi nisa gare ka ba!
Watarana Malaminmu Sheikh Dr. Muhammad Sa'eed Raslaan [H. A] ya taba cewa dangane da Sayyid Qutb:
"Sayyid Qutb kundin bidi'o'i ne."
Ma'ana yana tattare da bidi'o'i kala-kala na jiya da yau. Idan ka bibiyi lamarin Dr. Ahmad Gumi za ka iske ba shi da maraba da nasa, shi ne yau a cikin wannan bidi'ar gobe a cikin waccar, ya rasa matsaya guda daya hatta a kan bidi'anci, dama haka halin wadanda suke gabatar da hankali a nakali yake a kowane zamani da muhalli.
قال أحمد بن حنبل :
لم يكن أحد في زمان ابن المبارك أطلبَ للعلم منه .
السير (ج٧ص٥٩٥)
Ka jarraba wannan qaidar,
zaka zauna lafiya a duniya Ka kuma hadu da Allah salin-aalin .
Kafin Ka tsoma baki a wani lamari Ka tuna hadisin : Yana daga kyawon musulunci na mutum shine ya bar abinda babu ruwan sa.
In ya Zama da ruwan Ka kuma sai Ka tsoma baki to sai Ka tuna hadisin duk Wanda yayi Imani da Allah da Ranar lahira ya Fadi alkhairi ko yayi shiru..
Idan Kayi shiru din sai Ka dauki shawarar da manzo saw ya baiwa Abdullah ibn Busr cewa : Kada Ka bari harshen ka ya zauna ba tareda ambaton Allah ba..
In kuma kuma bazaka iya Zama cikin ambaton Allah ba to Ka dau shawarar da manzo saw ya baiwa muazh ibn jabal cewa: Ka kame harshen ka.
Domin da dama anji Wanda yawan surutun su ya halakar da su Amma ba a taba Jin Wanda yawan shirun sa ya halakar da shi ba.
© Usman Husain Adam
2022
أمور تساعد على الوقاية من العين قبل وقوعها.
الشيخ محمد سعيد رسلان حفظه الله
Babu masu lalata tarbiyyar al'ummar Hausawa da Musulmi na arewacin najeriya k**ar yan kannywood
Dr Idris abdulaziz da Yan izalar Jos.
1-yan izalar Jos suna kan zamiya na kungiyanci da ta'assubanci ,shi Kuma Dr Idris Yana kan khawarijan cin shi.
Abubuwan da suke gardama Akai na sabawa Sunnah (Yan izalar )abubuwa ne da daliban ilimi a mataki na kasa ma suna fahimtar jahilcin su Akai ,Kuma hatsarin dogewan su Akai bakai hatsarin dogewan Dr Idris abdulaziz akan khurujin shi ba.
Wajibin da yake kan ko wannen su ya bar abunda yake Kai na sabawa Sunnah ya koma kan tafarkin Sunnah.
2-A irin wanna sabanin nasu Babu bukatan lauyanci ga Dr Idris abdulaziz ,A baya wasu sun fake da maganan tauheedi ne ,sabani ne tsakanin shirka da tauheedi ,Amma yanzu Kuma a dauko ma'salar da Bata Kai tashi hatsari ba .
Yabon shi k**ar tsarkake shi ne.kada ka rudu da masu Yaba mishi wanna ya sabawa tafarkin musulman farko.
3-muna mishi fatan shiriya dashi da kungiyar izalah su watsar da tarkacen da suke Kai su tsayu akan Sunnah.
15/11/2023
صديق أحمد أبو بكر
Ka nisanci jinginuwa zuwa ga wata kungiya .
1-Daga cikin darasi da dalibin ilimi zai dauka a wajen ma'abota Sunnah na wanna zamanin akwai nisantar jinginuwa zuwa ga wata kungiya Koda ko tana dauke da sunan Sunnah ne.
Cikin malaman da s**a farfado da da'awar Sunnah a wanna Karnin akwai malamai hudu:
Sheikh Muhammad nasirudden albani Wanda ya rayu a yankin sham.
Sheikh muqbil Wanda ya rayu a Yemen.
Sheikh Muhammad saleh al'uthaimeen da ibnu Baz su biyun a su'udiyyah.
2-duka wadanna malaman babu Wanda ya jinginu zuwa ga wata kungiya ,sunyi da'awah ne akan Sunnah kurum ,Hakan Kuma sai yafi Sanya al'ummah su anfana da da'awar su ,Duk dalibin da kungiyoyi s**a fara kwallo dashi cikin kungiyoyin wanna zamanin Yana komawa gare su(wadanna malaman Sunnah din) da abunda s**a koyar sai ya warke daga rudanin kungiyoyi.
١١/٩/٢٠٢٣م
صديق أحمد أبو بكر
Click here to claim your Sponsored Listing.
Location
Category
Telephone
Website
Address
Sabon Gari Zaria
Zaria