17/05/2026
Abdullahi Bala Lau
This is an Official Page of Sheikh Abdullahi Bala Lau (National Chairman Of Jama'atu Izalatil Bidi'a [email protected]
17/05/2026
16/05/2026
NAIBI FOUNDATION
Founded by Sheikh Dr. Abdullahi Bala Lau, NAIBI Foundation is committed to transforming lives through Quranic education, youth empowerment, and social impact initiatives across Nigeria.
Our Programs
Quran Memorization (1 Year Program)
An intensive 1-year Tahfiz program with qualified instructors.
Open to youth nationwide.
Youth Empowerment
Skills acquisition, vocational training, and anti-drug campaigns designed to build a better future
Free & Affordable Education
Scholarships, free schooling, and educational support for underprivileged children.
Follows Us on our
https://www.facebook.com/share/1J3N4LA4FX/?mibextid=wwXIfr
Visits Our Website https://naibifoundation.com.ng
15/05/2026
HOTUNA: Huɗuba da sallar juma’a da shugaban JIBWIS Sheikh Dr. Abdullahi Bala Lau ya gabatar a masallacin JIBWIS Na FCDA Area 11 FCT Abuja.
Allah Ya Amsa Mana Dukkan Ibadun Mu Amin 🙏
Jibwis Nigeria
KAI TSAYE: HUƊUBAR SALLAR JUMA'AH Daga Masallcin JIBWIS Na FCDA Area 11 FCT Abuja.
Me gabatarwa:
Sheikh Imam Dr ABDULLAHI BALA LAU
(Shugaban JIBWIS Nigeria)
Allah Ya Amsa Mana Dukkan Ibadun Mu Amin 🤲🏻
JIBWIS NIGERIA
27th Z/QA'ADAH 1447H
15th MAY 2026
03/05/2026
Makarantar Sheikh Abdullahi Bala Lau ta yaye mahaddata 153 a garin Kaduna.
…….. Jimillar waɗanda s**a haddace Al’qurani a makarantin dake sassan Naijeriya ya kai mutum 2,900.
A safiyar Lahadin nan 3 ga Mayu, 2026, an gudanar da gagarumin taron yaye dalibai 153 da s**a haddace Alƙur’ani Mai Girma a Kaduna, ƙarƙashin kulawar Na’ibi Charity Foundation, gidauniyar da Imam Abdullahi Bala Lau ya kafa kuma yake ɗaukar nauyin karatunsu.
A jawabinsa, Imam Abdullahi Bala Lau ya gode wa Allah bisa wannan babbar nasara, tare da bayyana cewa adadin Mahaddata da gidauniyar ta yaye yanzu ya kai 2,900, a cibiyoyi 10 da ya buɗe a sassa daban-daban na ƙasar nan, ciki har da Jigawa, Lau, Adamawa da sauran garuruwa.
Haka kuma, ya yaba wa Mai Girma Gwamnan Jihar Kaduna, Sen. Uba Sani, bisa samar da wurin gudanar da taron, da kuma masaukan da aka tanada domin baki. Ya kuma yi kira ga Gwamnan da ya ƙara mayar da hankali wajen ganin an kawo ƙarshen rikicin Masallacin Low-Cost, wanda ya ɗauki lokaci, kamar yadda Gwamnan ya yi alƙawari.
A nasa jawabin, Mai Girma Gwamnan Jihar Kaduna, Sen. Uba Sani, ya jinjina wa Imam Abdullahi Bala Lau bisa wannan kyakkyawan yunƙuri na hidimtawa Alƙur’ani da al’umma. Gwamnan ya kuma yi alƙawarin ci gaba da tallafawa ayyukan alheri da gidauniyar ke gudanarwa.
Gwamnan ya bayyana cewa za a fara aiki a cibiyar horas da sana’o’i ta gidauniyar a mako mai zuwa, tare da samar da kayan aiki a cikinta, domin waɗanda ake haddatarwa su samu horo da abin dogaro da kai bayan kammala haddarsu.
A nasu jawaban, Kakakin Majalisar Wakilai ta Tarayya, Rt. Hon. Abbas Tajuddeen, da Mai Martaba Sarkin Zazzau, Amb. Ahmed Nuhu Bamalli, OFR, sun yi kira ga Imam Abdullahi Bala Lau da ya buɗe irin wannan cibiya a Zaria, domin wannan alkhairi ya ƙara faɗaɗa zuwa wasu yankuna.
Daga cikin manyan Malamai da s**a halarci taron akwai Mataimakin Shugaban Kungiyar na Ɗaya, Sheikh Isa Taliyawa Gombe, Dr. Ahmad Abubakar Gumi, Dr. Ibrahim Jalo Jalingo, Farfesa Abdullahi Saleh Pakistan, Sheikh Yakubu Musa Hassan Katsina Sautussunnah, Sheikh Dr. Muhammad Kabir Haruna Gombe, Sheikh Yusuf Sambo Rigachukun, da sauran iyayen dalibai, Malamai da Alarammomi daga sassa daban-daban na ƙasar nan.
An rufe taron da addu’o’i na musamman domin zaman lafiya, haɗin kai da ci gaban al’umma, daga bakin Chief Imam na Sultan Bello, Dr. Sulaiman Muhammad Adam, da Sheikh Yusuf Sambo Rigachukun.
Allah Ya sanya albarka a wannan taro, Ya karɓi wannan hidima, Ya albarkaci Mahaddata, Malamansu, iyayensu da duk waɗanda s**a bada gudunmawa wajen nasarar wannan babban aiki.
Jibwis Nigeria
01/05/2026
Shugaban JIBWIS Sheikh Dr. Abdullahi Bala Lau, ya buɗe katafaren masallacin juma’a da makaranta a unguwar Charanci gabas dake birnin kano. Sakataren JIBWIS na ƙasa Sheikh Dr. Muhammad Kabir Haruna Gombe, Shugaban JIBWIS na jahar kano Farfesa Abdullahi Sale Pakistan, Daraktan agaji na ƙasa Engr Mustapha Imam Sitti, Sakataren Alarammomi Sheikh Nasiru Gwandu da Prof Ibrahim Abdullahi R/lemo na ɗaya daga cikin waɗanda s**a halarci buɗewan.
Jibwis Nigeria
29/03/2026
A madadin JIBWIS Ina mika sakon ta’aziyyar rasuwar Hajiya Umma El-rufa’i, mahaifiyar tsohon gwamnan Jahar Kaduna, Malam Nasiru Ahmad El-rufa’i. wannan rashi babban rashi ne garemu, tare da sauran iyalanta, muna addu’ar Allah ya jikanta ya kyautata makwanci, ya kuma bada hakuri ga ‘yan uwa da iyalanta, tabbas rashi na mahaifiya ba karamin rashi ne ba.
Allah Ya Gafarta Mata Kura-Kuranta Baki Ɗaya, ALLAH Yayi Mata Rahamah Yasa Aljannah Alfirdausi Ce Makomarta tare da sauran musulmai muminai da s**a rigaye mu.
JIBWIS NIGERIA
13/03/2026
Hotuna: Rufe tafsirin Sheikh Dr Muhamnad Kabir Haruna Gombe na bana a masallacin Umar ɗan khaɗɗabi dake utako Abuja.
Jibwis Nigeria
03/03/2026
Shugaban JIBWIS Ya Yi Kira Ga Limamai Su fara Qanut Kan Rikice-Rikicen Gabas ta Tsakiya da Karin Hare-Haren Ta’addanci a Najeriya
Shugaban Kungiyar Jama’atu Izalatil Bid’ah Wa Iqamatus Sunnah (JIBWIS), Ash-Sheikh Dr Abdullahi Bala Lau , ya yi kira ga daukacin limamai da al’ummar Musulmi a faɗin Najeriya da su tsayar da addu’o’in qanuti a cikin sallolinsu, sakamakon ta’azzarar rikice-rikice a Gabas ta Tsakiya da kuma ƙarin hare-haren ta’addanci da ake fuskanta a cikin ƙasar nan.
Sheikh Bala Lau ya bayyana hakan ne a ranar Talata, 3 ga Maris, 2026, yayin Tafsirin Ramadan da yake gabatarwa a Yola, Jihar Adamawa. A cikin jawabin nasa, ya nuna alhini matuƙa kan yadda ake ci gaba da salwantar da rayukan jama’a, inda ya ce mafi yawan waɗanda abin ya shafa Musulmi ne marasa laifi.
“Abu ne mai tayar da hankali yadda rayuka ke salwanta ba gaira ba dalili,” in ji shi. “Iyaye, mata da yara suna shiga cikin halin ƙunci da rarrabuwar kawuna sakamakon rikice-rikicen da ke ƙara tsananta.”
Malamin ya bayyana cewa halin da ake ciki babbar jarabawa ce ga al’ummar Musulmi da ma duniya baki ɗaya, musamman idan aka yi la’akari da cewa tashe-tashen hankulan na faruwa ne a yankunan da ke da muhimmanci a tarihin Musulunci.
Haka kuma, ya nuna damuwa kan yadda hare-haren ta’addanci ke ƙara ƙamari a wasu sassan Najeriya, inda ya ce al’ummomi da dama na rayuwa cikin fargaba sakamakon hare-haren ‘yan ta’adda da masu garkuwa da mutane.
“Ba za mu manta da abin da ke faruwa a ƙasarmu ba,” in ji shi. “’Yan ta’adda na ci gaba da ƙara kai hare-hare, al’ummomi na fuskantar barazana, kuma zaman lafiya na ƙara shiga hatsari. Wannan na buƙatar mu tashi tsaye da addu’a da kuma gyaran halaye.”
Sheikh Bala Lau ya buƙaci limamai su ware lokaci a cikin salloli domin yin qunut, tare da roƙon Allah Ya kawo ƙarshen zubar da jini, Ya kare bayinSa,Ya ba shugabanni hikima, tare da dawo da zaman lafiya a duniya da Najeriya baki ɗaya.
Ya ƙara da cewa watan Ramadan wata dama ce ta tuba, komawa ga Allah, da kuma neman rahama a lokutan ƙalubale.
A ƙarshe, ya yi addu’ar Allah Ya kawo sauƙi ga waɗanda ke cikin ƙunci, Ya kawo ƙarshen rikice-rikice, kuma Ya wanzar da zaman lafiya mai ɗorewa a duniya da ƙasarmu Najeriya.
“Allah Shi ne Mai iko a kan komai,” in ji shi. “Gare Shi muka dogara, kuma gare Shi muke roƙon mafita da zaman lafiya.”
Jibwis Nigeria
Shugaba Sheikh Dr. Abdullahi Bala Lau Yayi kira shuwaga limamai da asoma addu'oi da alqunut akan masifu da suke faruwa a Nigeria da duniya baki daya, Allah yakawo mama sauki.
25/02/2026
Zaku iya Bibiyar mu a shafin mu na YouTube domin samun Tafsiran bana. Danna wannan link 🔗
Sheikh Dr. Abdullahi Bala Lau, Tafsir Day 5, 2026 Enjoy the videos and music you love, upload original content, and share it all with friends, family, and the world on YouTube.
Click here to claim your Sponsored Listing.
Location
Category
Contact the school
Telephone
Website
Address
Bekaji Street Jimeta Adamawa
Yola
640261