HISNUL MUSLIM

HISNUL MUSLIM Ingantattun Adduo’i daga Alqur'ani da Hadisan Annabi Muhammad (S.A.W.)

24/08/2025

HAKKIN MIJI AKAN MATA DA HAKKIN MATA AKAN MIJI

Gabatarwa

Aure wata babbar alaka ce ta soyayya da amana tsakanin ma’aurata. Addinin Musulunci ya gindaya hakkin kowane ɓangare domin tabbatar da zaman lafiya da jituwa a cikin iyali. Wannan rubutu zai bayyana hakkin miji akan mata, hakkin mata akan miji, da kuma hakkin tarayya tsakanin ma’aurata, domin a sami fahimtar juna da zaman lafiya mai ɗorewa.

1. Hakkin Miji Akan Mata

Ga wasu hakkokin da mata ke da su a wurin mazajensu:

1. A ciyar da ita gwargwadon iko.

2. A tufatar da ita daidai hali.

3. A shayar da ita.

4. A samar mata da kayan kwalliya.

5. A samar mata da kayan tsafta.

6. A samar mata da gurin kwana.

7. A kula da lafiyarta.

8. A biya mata bukatar saduwa.

9. A ilmantar da ita.

10. A girmama ta.

11. A mutunta ta.

12. A tausasa mata.

13. A yaba mata da abinci, kwalliya ko tsafta.

14. A nuna damuwa da ita.

15. A sakar mata fuska da murmushi.

16. A gaya mata kalmomi masu daɗi na yabo.

17. A zauna da ita ana hira da tattaunawa.

18. A kira ta da suna mai daɗi.

19. A yi mata kyauta ba zato ba tsammani.

20. A fita da ita wajen unguwa ko taro ko tafiya.

21. A taimaka mata da aikin gida ko ɗan ƙaramin abu.

22. A barta ta zabi abincin gida a wasu lokuta.

23. A barta ta zabi tufafinta.

24. A mutunta iyayenta da danginta.

25. A bata hakuri idan an yi mata ba daidai ba.

26. A yaba mata idan ta yi daidai.

27. Kada a zageta ko a muzantata a gaban yayanta.

28. Banda duka.

29. Banda zagi.

30. Banda saurin fushi.

31. A kasance mijin mai tsafta.

32. A kasance miji mai kula da goge baki.

33. A kasance miji mai kwalliya.

34. Kada ya kasance mai almubazzaranci.

35. Kada ya kasance mai kwauro.

36. Kada ya kasance mai shan taba.

37. Kada ya kasance mai shan giya.

38. Kada ya kasance mai yawon dare.

39. Kada ya kasance mai neman mata.

40. Kada ya kasance miji mai hira da wasu mata a gabanta.

41. Kada ya kasance mai yawan faɗa.

42. Kada ya kasance mai kauracewa shimfidar iyali.

43. Kada ya kasance mai nuna rashin damuwa da halin iyali.

44. Kada ya kasance mai tsananin kishi.

45. Kada ya kasance mai yawan zagi.

46. A nuna cewa an gamsu da ita.

47. A bata damar faɗin ra’ayinta.

48. A yi shawara da ita akan harkokin gida.

49. A dinga sumbatar ta lokaci zuwa lokaci.

50. A yi wanka tare a wasu lokuta.

51. A rera mata waka ko kirari.

52. A yi wasa da guje-guje.

53. Kada ya kasance mai zargi.

54. Kada ya kasance mai mugunta.

55. Kada ya kasance mai kushe.

56. Kada ya kasance mai bakin ciki da abin da iyali ke da shi.

57. Kada ya kasance mai ragwanci.

58. Ya kasance mai lafiya wajen biyan bukatar aure.

59. Ya kasance mai kaunar yayansa.

60. Ya kasance mai girmama kawaye da aminan matarsa.

Hakkin Mata Akan Miji.

Ga wasu hakkokin da mazaje ke da su a wurin matansu:

1. Ta riƙe masa amana.

2. Ta yi masa biyayya a duk abin da ba sabawa Allah ba.

3. Ta kula da dukiyarsa.

4. Ta kula da sallah da addu’a don zaman lafiya.

5. Ta girmama shi a gaban idonsa.

6. Ta kare girmansa a bayan idonsa.

7. Ta so abin da yake so, koda ba ta so ba.

8. Ta ƙi abin da yake ƙi, koda tana so.

9. Ta damu da abin da ya damu da shi.

10. Ta kau da kai daga abin da ya ƙi.

11. Ta yi fushi da duk abin da ya yi fushi da shi.

12. Ta yarda da abin da ya yarda da shi.

13. Idan ya bata ƙanana ta ga babba.

14. Idan ya bata da yawa ta yi godiya.

15. Ta farka kafin ya farka.

16. Sai ya yi bacci kafin ta yi.

17. Ta yi hakuri idan ya yi fushi.

18. Ta yi taushi idan ya yi tsauri.

19. Ta lallashe shi idan ya hasala.

20. Kada ta nuna raki a gabansa.

21. Kada ta yi kuka alhali yana dariya.

22. Kada ta yi dariya alhali yana kuka.

23. Kada ta tsaya kai da fata sai ya mata wani abu.

24. Kada ta matsa masa da buƙatu.

25. Kada ta ɗauke shi tamkar yaro.

26. Kada ta riƙa masa gyara barkatai.

27. Kada ta kushe tsarinsa.

28. Kada ta zuga shi a gaban danginta.

29. Ta girmama shi a wajen kawayenta.

30. Ta nuna masa abu mai kyau.

31. Ta ɓoye abu mummuna.

32. Idan ya kawo wata damuwa, ta taimaka masa.

33. Idan baya son wani abu ta daina.

34. Ta kwantar masa da hankali lokacin damuwa.

35. Ta sassauta masa idan yana bakin ciki.

36. Ta tsaya masa idan yana rashin lafiya.

37. Ta taimaka masa lokacin da yake buƙatar taimako.

38. Idan yana cikin kunci ta sassauta buƙatu.

39. Ta yi masa rakiya lokacin fita ta tarbe shi idan ya dawo.

40. Ta tausasa harshe lokacin magana.

41. Ta tsaftace gida iya iyawarta.

42. Ta tsara dakinta yadda zai birge.

43. Ta yi masa bankwana idan zai yi tafiya.

44. Ta yi ado gwargwadon iyawarta.

45. Ta bayyana halaye masu kyau.

46. Ta yi ishara mai hikima.

47. Ta bayyana kanta a matsayin mace.

48. Ta yi murmushi da lafazi mai kwantar da rai.

49. Ta cika zuciyarsa da soyayya da kwalliyarta.

50. Ta ja hankalinsa da abin da yake so.

51. Ta mayar da alheri idan ya mata mummuna.

52. Ta yafe masa idan ya yi mata laifi.

53. Ta karɓi uzurinsa.

54. Kada ta yi sallar nafila sai da izininsa.

55. Kada ta ɗauki azumi sai da izininsa.

56. Kada ta fita daga gida sai da izininsa.

57. Ta iya girki kala-kala.

58. Ta nisanci kazantar jiki.

59. Kada ta shigar da wani gida sai da izininsa.

60. Kada ta nemi saki ko rabuwa haka kawai.

Hakkin Tarayya Tsakanin Ma’aurata.

Hakkin da ya haɗa su duka kuwa sun haɗa da:

1. Nuna juna kauna da soyayya.

2. Taimakon juna a farin ciki da bakin ciki.

3. Kowa ya gyara kansa da tsafta.

4. Kowa ya kasance mai kishin ɗayan.

5. A sami amincewa juna.

6. A bawa juna hakkokin jin daɗi gwargwadon shari’a.

7. Kyakkyawan zamantakewa tsakanin juna.

8. Hakuri da juna.

9. Amincewa da juna.

10. Faranta juna rai.

11. Yin shawara tare.

12. Girmama iyayen juna da danginsu.

13. Taimakon juna idan aka shiga jarabawa.

14. Kada su tona asirin juna a waje.

15. Kada su ci amanar juna.

16. Kada su bayyana mu’amalar auratayya.

17. Akwai gado tsakaninsu idan ɗaya ya rasu.

Kammalawa

Aure ibada ce mai tsarki, wadda ake buƙatar ma’aurata su fahimci hakkin juna domin zaman lafiya da tsira. Idan aka kiyaye waɗannan hakkoki, za a samu iyali nagari, ƙasa nagari, da al’umma nagari.

Allah ya ba mu ikon kiyaye hakkin juna, ya cika zukatanmu da soyayya da kauna da girmamawa a tsakaninmu.

Mallam Aminu Ibrahim Daurawa

Manzon Allah Sallallahu alaihi Wasallama ya ce.Inda ace zaku dogara ga Allah tawakkali na gaskia, to da ya azurta ku k**...
24/08/2025

Manzon Allah Sallallahu alaihi Wasallama ya ce.

Inda ace zaku dogara ga Allah tawakkali na gaskia, to da ya azurta ku k**ar yadda yake azurta tsuntsu.
Tsuntsu zai wayi gari cikin sa ba komai, Amma bazai wuni ba sai ƙoshe.
Kuma ba tare da ya ajiye komai ba.

Yana Allah ka azurtamu da halal cikin sauƙi.
Ameen.

BismillahirrahmanirrahimAnas Ɗan Maalik ya ruwaito hadisi cewa...Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallam yace:"Imanin ɗa...
04/12/2022

Bismillahirrahmanirrahim
Anas Ɗan Maalik ya ruwaito hadisi cewa...

Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallam yace:
"Imanin ɗayan ku bazai cika ba har sai na kasance mafi soyuwa a gareshi fiye da ƴaƴan sa da iyayen sa da duk mutane baki ɗaya"
>Sadaƙa Rasulul Kareem.

Sahihul Bukhari, Sahihul Muslim.
(Muttafaƙun Alaihi)

Wannan ingantaccen hadisi ya tabbatar da cewa lallai soyayyar Manzon Allah itace cikon imani, duk wata kula da tsantsaini da mutum zai nuna a fili ko a ɓoye, to wannan baya sanyawa imanin sa yazam cikakke kuma karɓaɓɓe a wajen Allah har sai an sami chuɗanyuwar sa da soyayyar Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallam.

Ita kuma soyayya tana ɗamfare a jikin biyayya.
Babu biyayya...
Babu soyayya.
Idan dai kana so a same ka da cikakkiyar soyayyar Manzon Allah, to dole ne a same cikin yi masa biyayya kan abinda yai umurni ko hani.

Amma inda zaka cika duniya da kururuwar cewa kai masoyinsa ne Sallallahu Alaihi Wasallam, amma aka same ka dumu-dumu cikin saɓa masa kan umurni ko hani da yayi to wallahi soyayyar ka ba ta gaskiya bace, kuma Allah bazaiyi duba gareta a matsayin Ibada ba, sai dai ma a jefa ka cikin masu yaudara musamman ma idan kana nuna wa mutane kai mai tsananin ƙaunar sa ne Sallallahu Alaihi Wasallam.

Kuma mu sani cewa son Annabi Sallallahu Alaihi Wasallam Ibada ce, sannan ba'ayin Ibada ba tare da neman ilimi ba.
Don haka idan kana so Allah ya karɓi soyayyar ka ga Manzo Allah a matsayin Ibada kuma ka rabauta da ita a ranar gobe kiyama, to dole kaje wurin Malamai ka koyi yaya akeyin wannan gagarumar Ibada ta nuna so da ƙauna ga fiyayyen halitta Manzo Sallallahu Alaihi Wasallam.

Idan kuma kace kai kawai da ka zakayi, to lallai zaka samu kan ka a fagen saɓa masa, ko ma ka tsinci kanka a fagen yin faɗa ko yaƙar abinda ya karantar.
Allah ya tsare mu daga faɗawa cikin wannan mummunar jarabawar.

Ina fatan wannan gajeruwar faɗakarwa/Tunatarwa zai amfane mu baki ɗaya.

Allah ya nuna mana gaskiya ya bamu ikon bi, ya fahimtar damu ƙarya ya bamu ikon guje mata.

Wassalamu Alaikum Warahmatullahi Wabarakaatuhu.

30/08/2022

Kaji Fiyayyen Halitta...
Annabin mu, Masoyin mu, kuma Babba farin jakada.
Sallallahu Alaihi Wasallam.

Tunasar wa don ranar Juma'a.Ingantaccen hadisi ya tabbatar cewa.Yin salati ga Annabi yana daukaka darajar bawa a wajen A...
26/08/2022

Tunasar wa don ranar Juma'a.

Ingantaccen hadisi ya tabbatar cewa.
Yin salati ga Annabi yana daukaka darajar bawa a wajen Allah.
Kuma yana sanya bawa ya samu babban rabo a lahira.
Kuma hadisi ya tabbata cewa yawaita salati ga Annabi a dare da kuma ranar Juma'a abune mai matukar kyau da kuma amfani ga bawa.

Haka zalika karanta Suratul Kahfi ranar juma'a.
Manzo Sallallahu alaihi Wasallam ya fitar da hadisi akan haka.
Cewa "Duk wanda yake Karanta Suratul Kahfi a ranar Juma'a, to Allah zai warware kuma ya haskaka masa tsakanin Jama'o'in guda biyu, haka zai haskaka masa ranar lahira.

Yawaita salati ga fiyayyen halitta wajibi ne ga dukkan Musulmi.
Karanta suratul Kahfi ranar juma'a abune mai kyau ga wanda Allah maɗaukaki ya bashi iko.
Allah yasa mu dace.

::::::::::::::::::::::::::::::::::::::::::::::::
|| Please, Like and Share ||
::::::::::::::::::::::::::::::::::::::::::::::::

25/08/2022

Taƙaitaccen bayani aka Sujjadar Ƙabli da Ba'adi.
Allah yasa mu dace.

Addu'a Takobin mai Imani.Addu'a Ɓargon Ibada.Addu'a Garguwar Muminai.Yaakai dan uwana, idan zaka roki Allah don neman ka...
24/08/2022

Addu'a Takobin mai Imani.
Addu'a Ɓargon Ibada.
Addu'a Garguwar Muminai.

Yaakai dan uwana, idan zaka roki Allah don neman kariya ko neman biyan wata buƙata, to ka roƙeshi da sakankance wa.
Ma'ana (kaji a ranka wannan addu'ar ta karɓu)

Domin Manzon Allah Sallallahu alaihi Wasallama yace.
"Ana amsa addu'ar dayanku matuƙar baiyi gaggawa ba, yana cewa nayi addu'a amma ba'a karɓamin ba"

Shi mai imani a koda yaushe idan yayi addu'a to a ɗayan ukku take.

1. Kodai a biya masa bukata ta hanyar abinda ya nema.
2. Ko a tare masa wata fitina a madadin abinda ya nema (wanda acikin ilimin Allah haka shine yafi masa)
3. Ko a ajiye masa se yaje lahira sai a bijiro masa da ladan da aka ādana masa a haɗa a masa rahama.

Yaa dan uwa a matsayin ka na mai ƙaramin ilimi ba lallai bane ka fahimci alkairin abinda kake nema ko sharrin sa.

Ga wani Misali.
Yaro ne yake da ciwon mura (sanyi), sai s**a je wani shago kuma akwai kayan sanyi a wajen, sai yaron nan yace shi yana so abashi ƙanƙara ko Ice_cream yasha (kasan yaro da son kayan sanyi)
Kai kana da sanin cewa idan aka bashi ciwon sa na mura ko sanyi zai tashi yayi ta faman tari da zazzabi, amma shi yaro buƙatar sa kawai yake dubawa, don haka sai yayi ta kuka se an bashi...
Shin a matsayin ka na me ilimi da hankali zaka bashi ko kuma hana shi zakayi don kare lafiyar sa?

Don haka kaima bawan Allah akwai yiwuwar abinda kake nema cutar dakai zaiyi, don haka sai Allah ya hanaka ko ya chanza maka da wani wanda ya fi shi alkairi.

Daga ƙarshe ina mana nasiha da muji tsoron Allah mu kiyaye cin haram, don ita haram tana sa mutum yayi ta faman addu'a amma ba'a karɓa masa ba.

Allah yasa mu dace duniya da lahira

Wassalamu Alaikum Warahmatullahi Wabarakaatuhu.

Mu Koma Tsangaya
Tsangaya Online
ZAUREN FIQHU

LABARIN NURUDDEEN ZENKI.Mutumin da ya bada kariya ga kabarin Manzon Allah Sallallahu alaihi Wasallama Lokacin da Kafirai...
24/08/2022

LABARIN NURUDDEEN ZENKI.

Mutumin da ya bada kariya ga kabarin Manzon Allah Sallallahu alaihi Wasallama Lokacin da Kafirai s**ayi shirin Daukewa Jikin Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallam a Madina

Ya kasance sarki ne a Masar mai tsananin tsoron Allah a lokacin mulkin sa, wanda ana kiran sa Nuruddin Zanki.
Wannan al'amari ya faru ne Shekara ta 557 bayan hijra, yanzu kimanin shekaru 887 kenan da faruwar al'amarin.

Wata rana bayan yayi Tahajjud yaa kwanta, sai ya ga Annabi (Sallallahu Alaihi Wasallam) a mafarkinsa.
Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasallam) ya masa nuni zuwa ga wasu mutane biyu masu launin ja yana cewa:
"Ka cece ni daga wadannan mutane biyun"
Nuruddin ya farka a rude. Yai alwala yayi sallah sannan ya koma bacci.
Ya sake ganin wannan mafarkin.
Ya farka ya sake gabatar da alwala yayi sallah ya kwanta. Sai ya maimaita wannan mafarkin a karo na uku.
Nan dai bai sake komawa barci ba. Da gari ya waye, sai labarta mafarkin sa ga mai ba shi shawara, Jamal-ud-Din Al-Musali. Mashawarcin ya ce masa, “Me ya sa kake zaune a nan? Ka gaggauta zuwa Madina. Ya kara da cewa, "Don Allah kar ka labarta mafarkinka ga kowa".
Washe gari Nuruddin ya shirya tafiya zuwa Madina.
Ya tafi da mutum ashirin tare da shi har da mai ba da shawara. Sun ɗauki kyaututtuka masu tsada masu yawa tare da su don yin sadaka. Sun isa Madina cikin kwanaki goma sha shida. Nuruddin ya shiga masallacin Annabi ya yi salla. Sannan ya yi sallama ga Annabi (Sallallahu Alaihi Wasallam) da Sahabbansa. Nuruddin ya zauna a masallaci yana tunanin me zai yi.
Daga baya sai ya umarci Mashawarcin sa ya sanar da cewa, “Sultan ya kawo kyaututtuka da yawa don yin sadaka. Za a raba wadannan kyaututtuka ga mazauna Madina. Sultan ya bada kyauta ga kowane mazaunin Madina bi da bi. Sultan ya dubi kowane mai karɓan kyauta sosai don tantance fuskokin da ya gani a cikin mafarkin amma bai gansu ba.
Daga karshe Sultan ya tambaya, "Shin duk mazauna garin nan sun ziyarce ni?"
Amsar daga mazaunan ita ce, "Eh, amma“Akwai wasu yan Morocco masu tsoron Allah, waɗanda ba sa karɓar komai daga wurin wasu.
Suna ciyar da mabukata da karamci sosai. Suna yin azumi akai-akai. Da yin tahajjudi da yin satati ga Annabi (Sallallahu Alaihi Wasallam) dare da rana.
Suna kuma ziyartar masallacin Quba sau daya a mako". Sultan yace "Subhanallahi". Sai Sultan ya yi umarni a kawo masa su duka biyun. Bayan an kawo su sai aka tambaye su ku meyasa baku zo kun karbi kyautar ba? Sai s**a ce, "Muna da wadata sosai kuma ba ma buƙatar sadaka."
Tuni dama da zuwan su, Sultan ya gane su, ya tambaye su, "Daga ina kuka fito?" S**a ce, “Mu ’yan Morocco ne. Mun zo nan ne don aikin Hajji, muna son zama a nan ne don kusanci da Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasallam).
Sultan yace meyasa bazaku fadi gaskiya ba? Nan s**a yi shiru. Sultan ya tambayi inane masaukin su. jama'a s**a ce
Gidansu yana kusa da Masallacin.
Sultan ya tasa su a gaba har masaukin su.
Ya tarar da kayayyaki masu tsada da yawa a jibge.
Sultan ya dinga yawo a gidan shi kadai har ya hango wata tsohuwar darduma a daya daga cikin ɗakunan gidan.
A ƙarkashin wannan darduma sai yaga wani sabon rami babba da ake haƙawa ta ƙarƙashin ƙasa inda ya doshi zuwa kabarin Manzon Allah (Sallallahu alaihi Wasallama).
Mutanen nan s**a firgita zasu gudu ganin an gano su, amma aka kamosu aka kawosu har gaban sultan.
Sultan ya ce musu, "Yanzu ku gaya min gaskiya."
Sai s**a ce, “Hakika mu Kiristoci ne. Sarki mu ne ya aiko mu nan a matsayin Mahajjata daga Morroco. Ya biya mu kudi mai yawa domin mu cire jikin Annabi daga nan Madina. Don mu cimma burinmu sai muka fara zama a wannan gida mafi kusa da Masallaci mai Alfarma.
Muna tona ramin karkashin kasa da daddare kuma muna dauke da ƙasar a cikin jakunkuna zuwa makabartar Baqee muna zubda ƙasar a kusa da kaburbura.
A lokacin da muka isa kusa da ƙabarin, mun ga wata walƙiya mai tsananin firgitarwa, girgizar ƙasa mai ƙarfi kuma ta girgiza ƙasa.
Se kuma yanzu asirin mu ya tonu ka zo ka k**a mu.
Mun shaida cewa muna gab da aikata wannan laifin.
Sarkin Musulmi ya ba da umarnin kashe wadannan masu laifi. Ya godewa Allah (SWT) da ya zabe shi ya don gano wannan makircin.
An shirya makirci har sau biyu na farko tsakanin 386H. da 411H. Makirci na uku ya faru ne a shekara ta 557H. Bayan wannan makirci na uku, Sultan Nuruddin ya ba da umarnin tona wani rami mai zurfi a kewayen ƙaburburan Manzon Allah da Sahabban sa. Ya kuma cika wannan rami da narkakkiyar dalma.
Ta wannan hanyar babu wanda zai iya isa ga kaburburan ta hanyoyin karkashin kasa.

Wannan shine Labarin Nuruddeen Zenki.
Allah ya masa Rahama, shi da muƙarraben sa.

Mu Koma Tsangaya
Tsangaya Online
ZAUREN FIQHU

Yara Manyan Gobe...Yaa Allah ka ƙarfafe mu da yin Sallah akan lokaci kuma yadda aka koyar da ita a shari'a.Allah kasa mu...
24/08/2022

Yara Manyan Gobe...

Yaa Allah ka ƙarfafe mu da yin Sallah akan lokaci kuma yadda aka koyar da ita a shari'a.
Allah kasa mu iske ka muna masu cikakken imani.

Mu Koma Tsangaya

Tsangaya Online

ZAUREN FIQHU

Allahu Akbar...Kimanin mutum dubu sha ukku 13,000 kenan maza da mata dangin alkairi suke tare da wannan shafi namu mai a...
23/08/2022

Allahu Akbar...

Kimanin mutum dubu sha ukku 13,000 kenan maza da mata dangin alkairi suke tare da wannan shafi namu mai albarka kuma acikin shekaru bakwai 7 na gudanar wa.

Muna muku gaisuwa da fatan alkairi, kuma lallai mu sani cewa "alkairi ne ya haɗa mu"

Muna yiwa kowa fatan alkairi duniya da lahira.

Daga dukkan masu gudanar da wannan shafi.

HISNUL MUSLIM MANAGEMENT.

Mu Koma Tsangaya

Tsangaya Online

ZAUREN FIQHU

23/08/2022

DALILAN MUTUWAR ZUCIYA GUDA SHIDA (6)

Imam Hasanul Basariy yace:

Zukatan mutane suna ɓaci ne saboda dalilai guda shida :

1. Suna aikata zunubi da gangan, da nufin wai daga baya zasu tuba.

2. Suna neman ilimi amma basu yin aiki dashi.

3. Idan ma sunyi aiki da ilimin, to basu sanya ikhlasi (tsarkake zuciya domin Allah).

4. Suna cin arzikin Allah amma basu yi masa godiya.

5. Basu gamsuwa da rabon da Allah ya raba ya basu. (shi ke sanyasu neman arziki ta hanyar haram).

6. Suna bisine mamatansu amma basu wa'aztuwa dasu.

ALLAHU AKBAR!!!.

Ya Allah ka sanya mu zamto cikin bayinka masu yawan tuba, masu neman ilimi da aiki dashi, masu yawan ikhlasi, masu yawaita godiya gareka, masu yarda da gamsuwa da duk abinda ka bamu, masu wa'aztuwa da kowacce alama daga gareka.

Address

Unguwar Gabas
Yana

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when HISNUL MUSLIM posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The School

Send a message to HISNUL MUSLIM:

Shortcuts

Share