Yakawada Page

Yakawada Page Yakawada Page Domin Cigaban Yakawada...

02/07/2026

TARIHIN RAYUWAR FARFESA ANGO ABDULLAHI, CON: JAGORAN KUNGIYAR DATTAWAN AREWA, KUMA JAGORAN ILIMIN NOMA DA KIWO.

Daga Bangis Yakawada ✍️

Farfesa Ango Abdullahi, CON, na ɗaya daga cikin fitattun masana a fannin noma, tsohon Shugaban Jami'ar Ahmadu Bello (ABU), Zariya ne, kuma fitaccen dattijon Arewa wanda ya shafe shekaru da dama yana ba da gagarumar gudummawa wajen bunƙasa ilimi, noma, shugabanci da ci gaban Najeriya. Har ila yau, shi ne Convener kuma Shugaban Kwamitin Amintattu (Board of Trustees) na Kungiyar Dattawan Arewa (Northern Elders Forum – NEF), inda ya kasance ɗaya daga cikin manyan muryoyin da ke kare muradun Arewa da Najeriya baki ɗaya.

Haihuwa da Farkon Rayuwa

An haifi Farfesa Ango Abdullahi a ranar 13 ga watan Disamba na Shekarar 1938, a garin tsohuwar Giwa da ke Karamar Hukumar Giwa, Jihar Kaduna. Ya taso cikin iyalai masu kishin ilimi da tarbiyya. Ya fara karatunsa a Kali Elementary School a shekarar 1944, sannan ya kammala firamare a Giwa Elementary School. Daga nan ya wuce Zaria Middle School kafin ya shiga fitacciyar makarantar nan da tayi shura wajen horas da manyan shuwagabannin Najeriya wato Barewa College, daje garin Zariya, inda ya yi karatu tsakanin shekarun 1953 zuwa 1958.

Karatunsa da Ƙwarewarsa

Bayan kammala karatun sakandare, ya ci gaba da neman ilimi a Nigerian College of Arts, Science and Technology, Zariya daga shekarar 1959 zuwa 1961. Daga bisani ya yi karatu a Jami'ar Ibadan tsakanin shekarun 1961 zuwa 1964.

Daga nan ya tafi Jami'ar Kansas State da ke Ƙasar Amurka, inda ya samu Digiri na Babbar Kwarewa (MSc) a fannin Noma a shekarar 1968, sannan ya kammala Digirin Digirgir (PhD) a fannin Agronomy a shekarar 1976.

Ayyuka da Gudummawa

Da ya dawo Najeriya, Farfesa Ango Abdullahi ya fara aiki a Institute for Agricultural Research (IAR), Samaru, inda ya yi fice wajen bincike da koyarwa har ya zama Farfesa tun yana da kusan shekaru 40, a duniya.

A shekarar 1979 aka naɗa shi Shugaban Jami'ar Ahmadu Bello (Vice-Chancellor), mukamin da ya riƙe har zuwa shekarar 1984. A lokacin shugabancinsa, jami'ar ta samu ci gaba sosai ta fuskar ilimi da gudanarwa.

Baya ga harkokin ilimi, ya shiga siyasa inda ya taɓa zama ɗan Majalisar Tarayya mai wakiltar Zaria North West. Haka kuma ya kasance Mai Bai wa Shugaba Ƙasa Olusegun Obasanjo Shawara kan Harkokin Abinci da Tsaro tsakanin shekarun 1999 zuwa 2003.

Sarautarsa

Baya ga gudummawar da ya bayar a fannonin ilimi, noma da shugabanci, Masarautar Zazzau ta naɗa Farfesa Ango Abdullahi sarautar Magajin Rafin Zazzau wanda ya gaji magabatan sa a shekarar 2007 domin karrama irin hidimar da ya yi wa al'umma da ƙasa. Ya ci gaba da riƙe wannan sarauta har zuwa shekarar 2025, lokacin da ya ajiye ta da kansa saboda tsufa. Bayan ajiyewarsa, Sarkin Zazzau ya naɗa ƙaninsa, Alhaji Shehu Abdullahi, a matsayin sabon Magajin Rafin Zazzau.

Iyali da Zuriyarsa

Farfesa Ango Abdullahi ya gina iyali mai cike da ilimi da hidimar ƙasa, inda wasu daga cikin 'ya'yansa s**a yi fice a fannoni daban-daban.

Babban ɗansa, Marigayi Isah Ango Abdullahi, ya kasance ma'aikacin gwamnati wanda ya ba ƙasa gudummawa a ɓangaren tsaro da leƙen asiri. Kafin rasuwarsa, ya yi aiki a Hukumar Leken Asiri ta Ƙasashen Waje a Najeriya wato (Nigerian Intelligence Agency – NIA) da ke Abuja. Ya rasu a shekarar 2022, inda rasuwarsa ta haifar da alhini ga iyalansa, abokansa da duk waɗanda s**a san shi.

Daga cikin sauran 'ya'yansa akwai Hon. Mohammed Shamsuddeen Ango Abdullahi, wanda ya kasance ɗan Majalisar Wakilai na Tarayya a Majalisa ta Bakwai daga shekarar 2011 zuwa 2015, inda ya wakilci mazabar Birnin Gwari/Giwa ta Jihar Kaduna.

Haka kuma akwai Hon. Sadiq Ango Abdullahi, wanda yake ɗan Majalisar Wakilai ta Tarayya a halin yanzu, yana wakiltar mazabar Sabon Gari ta Jihar Kaduna tun daga shekarar 2023.

Matsayinsa a Yanzu

A matsayinsa na Convener kuma Shugaban Kwamitin Amintattu na Kungiyar Dattawan Arewa (Northern Elders Forum – NEF), Farfesa Ango Abdullahi ya ci gaba da kasancewa ɗaya daga cikin manyan dattawan Najeriya masu ba da shawarwari kan harkokin siyasa, tsaro, zaman lafiya da ci gaban Arewa.

Har ila yau, yana ci gaba da kira ga gwamnati da al'umma da su ba noma muhimmanci, yana mai jaddada cewa bunƙasa noma da samar da wadataccen abinci su ne ginshiƙan bunƙasar tattalin arzikin Najeriya.

A tsawon rayuwarsa, Farfesa Ango Abdullahi ya kasance abin koyi ga ɗalibai, malamai, manoma, shugabanni da matasa. Gudummawar da ya bayar wajen bunƙasa ilimi, noma da shugabanci ta sanya sunansa cikin jerin fitattun mutanen da s**a taka muhimmiyar rawa a tarihin Najeriya.

Allah Maɗaukakin Sarki Ya ƙara wa Farfesa Ango Abdullahi lafiya, nisan kwana da albarka. Ya saka masa da alheri bisa irin gudummawar da ya bayar ga ilimi, noma da ci gaban Najeriya, Ya kuma jiƙan yayansa Marigayi Alhaji Samaila Abdullahi Yakawada, da Ɗansa Isah Ango Abdullahi da rahama, Ya gafarta masu kura-kuransu, Ya sanya Aljannatul Firdausi ta zama makomarsu da sauran Al'ummar Musulmai baki daya. Amin.

30/06/2026
Amen ya Alrahman
22/06/2026

Amen ya Alrahman

Gone from our sight, but never from our hearts.
May Allah shower my father with mercy and forgiveness. Amin thumma Amin

Alhamdulillahi Allah Mun Gode Maka Kwarai!
13/06/2026

Alhamdulillahi Allah Mun Gode Maka Kwarai!

TAYA MURNA GA SABON SHUGABAN JIBWIS RESHEN KARAMAR HUKUMAR GIWA, JIHAR KADUNA.Alhamdulillah.Muna miƙa saƙon taya murna t...
06/06/2026

TAYA MURNA GA SABON SHUGABAN JIBWIS RESHEN KARAMAR HUKUMAR GIWA, JIHAR KADUNA.

Alhamdulillah.

Muna miƙa saƙon taya murna tare da addu'o'i na alkhairi ga sabon Shugaban JIBWIS na Ƙaramar Hukumar Giwa, Dr. Kabiru Ahmad Rufa'i Yakawada, bisa amincewar da aka yi masa ta jagorantar wannan babbar ƙungiya ta addinin Musulunci.

Wannan naɗi wata babbar alama ce ta yarda da nagarta, ƙwarewa, da jajircewarsa wajen hidimtawa addini da al'umma baki daya. Muna da yakinin cewa ƙarƙashin jagorancinsa, JIBWIS Reshen Ƙaramar Hukumar Giwa za ta samu ci gaba, haɗin kai, da bunƙasar ayyukan da'awa da ilimantarwa.

Haka kuma muna yabawa tsohon Shugaban JIBWIS na Ƙaramar Hukumar Giwa, wanda ya gabata wato Alhaji, Abdulhamid Aliyu, bisa shekaru 33 da ya shafe yana jagorancinsa cikin gaskiya, rukon amana, haƙuri da kishin addini. Allah Ya saka masa da alkhairi, Ya ƙara masa lafiya da nisan kwana, ya kuma sa ayi Kyakykyawan karshe

Muna addu'ar Allah Maɗaukakin Sarki Ya ba sabon shugaba hikima, basira, da ikon gudanar da wannan amanar yadda ya dace, Ya kuma sanya alkhairi da nasara a cikin dukkan ayyukansa.

Muna taya ka murna, Allah Ya taimaka Ya kuma sa ka gama lafiya.

Al'ummar Yakawada Da Kewaye✍️

02/02/2026

Yesterday, I had the honour of attending the Northwest Stakeholders Summit as an invited guest, a high-level engagement organized by the Joint Committees of the Northwest Development Commission in the Senate and the House of Representatives, held at Murtala Muhammed Square, Kaduna.

I participated not only as the Chairman of NWDC, but as a stakeholder deeply interested in the progress of our region. The summit represented a critical political and developmental moment for the Northwest — a rare platform where leadership, experts, and citizens converged to interrogate the pressing challenges confronting our zone and to design a coherent roadmap for sustainable recovery and growth.

The discussions were frank and purposeful. They acknowledged the security, economic, and social realities facing the Northwest, while also projecting a future built on strategic planning, institutional accountability, and regional solidarity. It was reassuring to see a strong commitment toward aligning the Commission’s mandate with the real needs of the people, ensuring that development is not abstract, but measurable in improved livelihoods and strengthened communities.

Equally significant was the emphasis on public sensitization. A commission of this magnitude must be understood by the people it serves. Citizens and stakeholders must see themselves as partners in progress, not spectators. The Northwest is endowed with immense human and material resources, and by properly harnessing our comparative advantages, we can reposition the region as a driver of national stability and economic strength.

I commend the organizers for extending the invitation and for creating a platform that encouraged honest dialogue and visionary thinking. There is much to reflect upon and even more to implement. The success of this summit will ultimately depend on political will, disciplined ex*****on, and sustained engagement with the people.

The Northwest cannot afford incremental progress. The moment demands bold action, unity of purpose, and leadership that is accountable to history. I leave the summit more convinced than ever that our region possesses both the capacity and the collective spirit to overcome its trials and claim its rightful place in Nigeria’s development story.

Hon. Lawal Sama’ila Yakawada
Dan’iyan Atyaf,
Chairman, Northwest Development Commission

Allahu AkbarAllahu AkbarAllahu AkbarAkwana atashi bawuya wajen Allah yau 6/12/2025 shekaru 19 kenan darasuwa wannan bawa...
06/12/2025

Allahu Akbar
Allahu Akbar
Allahu Akbar
Akwana atashi bawuya wajen Allah yau 6/12/2025 shekaru 19 kenan darasuwa wannan bawan Allah ( Alhaji Samaila Abdullahi Yakawada ) muna kara addu'a Allah yajikanshi da sauran yan uwa musulmi bakidaya.

21/11/2025

Juma'ah Special Prayer!

On this blessed Friday, we turn to Allah, the Most Merciful, with sincere hearts and humble hands raised in prayer.

O Allah, the Lord of all creation,
We ask You to bless our beloved nation,
• Grant us peace in every community, stability in every region, and unity in every heart.
• Remove hardship, insecurity, poverty, and every form of trial from our land.
• Strengthen our brotherhood, protect our homes, and guide our youth towards righteousness and success.

O Allah, we pray for the progress of our nation:
• Bless our economy with growth and opportunities.
• Grant wisdom to our scholars, resilience to our workers, and prosperity to our farmers, traders, and all who strive for a better future.
• Let justice, compassion, and truth prevail in our institutions.

O Allah, we pray for our leaders, past and present:
• Guide them with wisdom and sincerity.
• Inspire them to lead with honesty, fairness, and a genuine desire to uplift the lives of every citizen.
• Protect them from temptation, corruption, and harmful influences.
• Surround them with people of integrity who will remind them of responsibility and accountability.
• Reward those who serve with good intentions and reform those who have lost their way.

O Allah, the Turner of hearts,
• Purify our intentions, increase our faith, and fill our hearts with gratitude.
• Forgive our shortcomings and accept our prayers.
• Make this Friday a source of blessing, mercy, and spiritual upliftment for us, our families, and our nation.

May Allah’s peace and blessings be upon every Muslim, today and always.
Amin.

Hon. Lawal Samaila Abdullahi Yakawada
Chairman, North-West Development Commission (NWDC)

21/11/2025

Tarihin Rayuwar Farfesa Ango Abdullahi

Farfesa Ango Abdullahi, na ɗaya daga cikin fitattun masana a fannin noma kuma dattijo mai girma a Arewa da Najeriya baki ɗaya, ya bar gagarumin tasiri a rayuwar al’umma. Ya shahara musamman a matsayin Shugaban Kungiyar Dattawan Arewa wato ''Northern Elders Forum'' (NEF) sannan kuma tsohon Shugaban Jami’a (Vice-Chancellor) na Jami’ar Ahmadu Bello, Zaria (ABU). Wannan tarihin yana haskaka rayuwa da nasarorin wannan fitaccen ɗan Najeriya.

---

Farkon Rayuwa da Ilimi

An haifi Ango Abdullahi ne a ranar 13 ga Disamba, 1938, a ƙauyen Tsohuwar Giwa, kusan kilomita 30 daga Zariya. Rayuwarsa ta tashi daga ƙananan tushe amma ta kai shi ga manyan matsayi a ilimi da siyasar Najeriya.

Ya yi karatu a muhimman makarantu kamar:

Barewa College (1953–1958)

Nigerian College of Arts, Science, and Technology, Zaria (1959–1961)

University of Ibadan (1961–1964)

Kansas State University, Amurka

---

Aiki a Fannin Noma da Ilimi

Bayan kammala karatu a 1964, Farfesa Ango ya dawo Najeriya ya fara aiki a Ma’aikatar Noma ta Arewa. Daga nan aka tura shi Samaru, inda ake gina Jami’ar Ahmadu Bello (ABU). A lokacin, cibiyoyin da ke yankin Samaru su ne tushen wasu daga cikin sassan farko na jami’ar.

Aikin farko da aka bashi shi ne a Institute for Agricultural Research (IAR), wanda daga baya ya koma cikakken ɓangare na ABU.

Don ƙara inganta iliminsa, ya sake komawa Kansas State University, inda ya samu:

MSc a Agronomy (1968)

PhD a Agronomy (1976)

Bayan dawowarsa ne ya kai matsayin Farfesa saboda jajircewa da ƙwarewarsa.

---

Matsayi a Siyasa da Ilimi

Baya ga ilimi, Farfesa Ango Abdullahi ya taka rawa a siyasa. Ya yi aiki a matsayin:

Ɗan majalisa mai wakiltar Zaria North West Federal Constituency

Kwamishinan Tsare-tsaren Tattalin Arziki na North Central State (1973–1975)

A fannin ilimi kuma ya rike mukamai da dama:

Daraktan Binciken Noma, ABU (1977–1979)

Mataimakin Shugaban Jami’a (1979)

Shugaban Jami’a (Vice-Chancellor) daga 1979 zuwa 1986

---

Gwagwarmayar Tallafa wa Noma

A duk rayuwarsa, Farfesa Ango ya kasance mai fada a ji wajen jaddada muhimmancin noma ga Najeriya. Lokacin da yake Mai Ba da Shawara ga Shugaba Olusegun Obasanjo kan Harkokin Noma da Tsaro (1999–2003), ya karfafa wa manoman Arewa su koma noma domin bunkasa tattalin arzikin kasa.

Ko da yake ya amince da muhimmancin man fetur ga tattalin arziki, ya yi imani cewa noman ne ya kamata ya zama ginshiƙin Najeriya ba man fetur Kadai ba.

---

Girmamawa da Karramawa

Saboda gudummawar da ya bayar, Gwamnatin Tarayya ta ba shi lambar yabo ta:

Commander of the Order of the Niger (CON) a 2007.

Haka kuma masarautar Zazzau ta ba shi sarautar:

Magajin Rafin Zazzau, wadda take nufin mai kula da ruwa da albarkatun noma.

---

Gado da Tasiri

Gadon Farfesa Ango Abdullahi ya wuce mukamai da ya riƙe. Ya kasance shugaban kwamitoci da hukumomi da dama, ya shugabanci kwamitocin jami’o’i, ya kuma taka muhimmiyar rawa a harkar ilimi da noma a Najeriya.

Jajircewarsa wajen ganin Najeriya ta ci gaba ta hanyar ilimi da noma ya tabbatar da irin babban tasirin da ya bari ga al’umma.

Muna Adu'a Allah ya Karama masa Lafiya Ameeeen.

Address

Yakawada

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Yakawada Page posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Shortcuts

Share