06/12/2025
Big shout out to my new rising fans! Nura Mlm Kusanchi
Bridging the "Sectorian" Muslim populous towards global trends
06/12/2025
Big shout out to my new rising fans! Nura Mlm Kusanchi
Salam alaikum yan uwana na wannan shafin Mai albarka,Ina Mai baku hakuri na shiru da kukaji da gareni,insha Allah za mu cigaba da fashin Baki akan lamarin maulana Amirul waizina (H)
18/06/2022
KIRA GA MEMBOBIN AKAFSAN A MATAKIN FARKO DAMA DUK WANI DAN AS'HABUL-KAHFI | Daga Akafsan Management
Allah (SWT) cikin Surah al-Mujaadila, Aya 12, yana cewa;
( يَا أَيُّهَا الَّذِينَ آمَنُوا إِذَا نَاجَيْتُمُ الرَّسُولَ فَقَدِّمُوا بَيْنَ يَدَيْ نَجْوَاكُمْ صَدَقَةً ۚ ذَٰلِكَ خَيْرٌ لَّكُمْ وَأَطْهَرُ ۚ فَإِن لَّمْ تَجِدُوا فَإِنَّ اللَّهَ غَفُورٌ رَّحِيمٌ )
المجادلة (12) Al-Mujaadila
"Yã kũ waɗanda s**a yi ĩmãni! Idan zã ku gãnã da Manzon Allah, to, ku gabãtar da ƴar sadaka a gabãnin gãnãwarku, wannan ne mafi alhẽri a gare ku, kuma mafi tsarki. Sai idan ba ku sãmi (abin sadakar ba), to, lalle, Allah, Mai gãfara ne, Mai jin ƙai".
Faɗin Allah subhanahu wata'ala cewa; "A gabãtar da sadaka". Bawai don Annabi (ﷺ) mabuƙaci ne ba, Allah yace a gabatar masa da sadaka, a'a..! Allah (SWT) ya faɗi haka ne domin tsarkake muminai (Khairan Lakum Wa Aɗhar). Annabi (ﷺ) Mawadaci ne gaba ga duk wani abu da wani wanda ba Allah ba zai bashi, ya tabbata a tarihi cewa "Dandazon Mutane ne suke cin abinci a gidan Annabi (ﷺ) kullum". Wanda ba mawadaci ba, baza a sami haka daga gareshi ba. Ku rabu da maganar ana kwana arba'in ba a dora tukunyar abinci ba, a gidan Annabi (ﷺ), hankali bazai karɓi wannan ba. Wanda dandazon mutane suke jiransa domin ya basu abinda zasuci, kuma shine yake kwana arba'in ba ayi abinci a gidansa ba? Wannan ba gaskiya bane.
Kasancewar yanzu Annabi (ﷺ) baya tare damu a zahiri, wannan aya zata yi aiki kan waɗanda suke massala aikin da Annabi Sallallahu alaihi Wasallam yayi. Kamar yadda ya tabbata a wani hadisi "Malamai sune magada Annabawa" da kuma faɗin Allah a cikin 'Suratu Taubah', ayar Sadaka, zuwa fadin Allah "Wa Fisabilillah" wadanda suke kan tafarkin daukaka addinin Allah. Wannan a bayyane yake cewa akwai Malaman da suke massala wannan gado na Annabawa, ko shakka babu Sheikh Abduljabbar Kabara ɗaya ne daga ciki, don haka;
AKAFSAN tana kira ga ɗaukacin Membobinta dama duk wani ɗan As'habul-kahfi kan kulawa ta sosai ga lamarin Sheikh Abduljabbar Kabara, k**ar yadda kowa ya sani, yanzu kusan shekara guda kenan Malam yana tsare, bayan buƙatu (magidanci, babban mutum, kuma babban malami) na yau da kullum da tsadar rayuwa, ga kuma Shari'ar da aka ɗauki lokaci ana fafatawa tsakanin Malam shi kaɗai da raunanan dake tare dashi, da kuma Gayyar Masu Mulki, Attajirai, Sarakuna, Hamshaƙan Malaman Maja, Ƴan Siyasa da Gwamnatoci, shari'a wacce take fara lissafi daga Miliyoyin Nairori, wanda zuwa yanzu ta lashe fiye da lissafin ƴan yatsu.
Aiki da ayar da muka kawo a farkon wannan rubutu (Suratul Mujadila, Aya ta 12), lallai kowannen mu yana ganawa da Malam kusan kowacce rana (ta hanyar Sauraron Karatukansa), ''Najwa" da akace a wannan aya, ana nufin neman wani ƙarin haske gameda lamarin addini. Wanda mu Ɗaliban Malam har yanzu da aka rufe makarantun, muna Saurarar karatukansa da ƙarfin ikon Allah, kuma muna samun haskake-haskake daga karatukan Malam da aka ɗauka a tsawon shekaru (na kusa da na nesa).
Don haka muke kira a ci gaba da bada gudunmawar neman albarka da tsarkaka (k**ar yadda Allah (SWT.) Ya fada a Alkur'ani mai girma.
Hanya ɗaya sahihiya itace, ta Account ɗin;
As'habul-kahfi Warraqeem Development Association, wato Asusun Banki Mallakin Jagoran As'habul-Kahfi, k**ar haka:
LAMBAR ASUSU (ACCOUNT NUMBER): 1140109791
SUNAN ASUSU (ACCOUNT NAME): Assahabulkahfi Warraqim Development Association
ASUSUN AJIYA (BANK): Polaris Bank
_______________
JAN HANKALI:
Duk wanda ya tura, yayi mana comment da hoton shedar tura kuɗin wato (teller, ko resit, ko screenshot na debiting alert a kasan wannan rubutu ( https://www.facebook.com/100141528415016/posts/573108557784975/). A shafin ƙungiya na Facebook.
Membobin AKAFSAN kuma da suke da register a wannana ƙungiya sai su tura ta WhatsApp group na ƙungiyar AKAFSAN, saboda ƙungiya za tayi documenting ɗin duk wanda s**a tura.
Allah ya bada ikon bayarwa, Amin.
AKAFSAN MANAGEMENT
18/6/2022
17/06/2022
GANDUJE LIBRATE ABDULJABBAR
As'habul kaaf is symbol of unity and peace. Kindly, that is ready to eradicate sentimentalism in the generalality of contemporary Islamic world
BA IDO RUFE MUKE BIN SHEIKH ABDULJABBAR BA | Akafsan Management
Leave a Comment / Post / By Akafsan Reporters
KIRA GA MASU KISHIN AS’HABU-KAHFI DA JAGORANTA (SHEIKH ABDULJABBAR KABARA)
Idan Allah (SWT) ya haska maka wani al’amari wanda zai ciyar da wannan tafiya gaba, ko wanda ya shafi As’habul-Kahfi, zai fi dacewa, abi hanya mafi kyau, kuma mafi dacewa wajen bijirarwa ta fuskar shawara.
Hanya mafi kyawu ita ce a je a sami jagoran tafiya a sanar dashi, kuma a sami yarda da amincewarsa, kafin a aiwatar da abun.
Haka zalika, wanda yake ganin cewa jagoranmu yayi kuskure a cikin wani al’amari, bai dace ya ɗauki matakin yaɗa (wannan abu da yake zargi ba), ta hanyar sakar wa al’ummar duniya (General Public), bai k**ata a futo ana faɗa a duniya ba.
Mun san inda jagora yake, kuma munsan protocols da ake bi domin, ganawa dashi. Ya k**ata mu san cewa kurmawa, ba Maƙabarta bace, Malamin mu yana raye, ana iya ganin sa, ana iya tattaunawa dashi, Mai zai hana ba za aje a sameshi ba..?
Duk wanda ya san Sheikh Abdulhabbar, ya sani cewa mutum ne mai sauƙin kai gameda lamarin gaskiya, yana ƙarbar gaskiya koda daga wajen magauta ne, ballantana kuma masoya, Shugabannin AKAFSAN shaida ne akan haka. Mun sani sarai cewa Shehin Malamin bashi da ra’ayin riƙai wajen karɓar gaskiya.
Inda ake samun matsala shine, hanya, siga ko kuma yanayin da ake isar da saƙo (Channels of Communication), waɗanda suke da ƙwarewa a fannonin( Psychology, Philosophy, Education) da masana a fannin (Information and Communication) sune za sufi fahimtar abunda muke nufi anan.
Sheikh Abduljabbar Kabara, gogaggen Malamin Addini ne, ba haka kawai yake aiwatar da lamura sa-sakai ba, yana da irin nasa philosophy wanda yake amfani dashi wajen karɓa ko rashin karɓar shawarwari. Abinda yake damun mutane shine gaggawa cikin Al’amura.
ABINDA YA KAMATA SHINE:
A sanda kake so ka isarwa jagora wani saƙo, ka tanadi hujjoji gamsassu waɗanda suke na gaskiya, kada kayi masa dungu, kada ka ɓoye masa duk wani abu da kasan muhimmine wanda yake da alaƙa mai ƙarfi da bayanan ka, idan kuma ka manta dashi, kada kayi ƙasa a gwiwa wajen komawa domin yi masa bayani, kuma ka tsarkake zuciyar ka.
Indai har ka kiyaye waɗannan sharuda wallahi zaka tarar cewa jagoranmu, mutum ne mai sassauƙan ra’ayi, kuma mai fahimta da buɗaɗɗiyar zuciya, a daina yanke masa hukunci batare da anyi zuzzurfan nazari ba.
AKAFSAN MANAGEMENT
16/06/2022
16/06/2022
https://www.facebook.com/100141528415016/posts/571499901279174/?sfnsn=scwspmo
ABUBUWAN DA YA KAMATA AL'UMMA SU SANI | Akafsan Management
Sheikh Abduljabbar ba wai gaggawa yake akan a kunna/sanya audio na karatunsa a kotu ba, domin ya fito daga Makarantar Annabi Yusuf (AS), a'a!
Shehin Malamin yafi buƙatar Kotu da sauran Al'umma su fahimci cewa kariya yake bawa Annabi (ﷺ), wato akasin ƙage da sharri wanda ƴan Maja s**a kitsa masa.
Sheikh Abduljabbar yana son taimakan Azzalumai masu hannu cikin zalintarsa, musamman waɗanda aka shigar bisa rashin sani, cewa su gane, kuma su fahimci irin ƙullallalen makirci da aka shirya cikin wannan lamari.
Jagoranmu, ya sani cewa kotu hujja take nema, kuma yana da yaƙini idan aka kunna wa kotu cikakkun jumloli da gaɓoɓin da ake dambarwa akansu, babu shakka Allah zai fahimtar da mutane masu tarin yawa, musamman waɗanda aka burkitawa gaskiya, aka juya musu sama ta koma ƙasa.
Kunna gaɓoɓi da jumlolin karatuttukan da ake wannan dambarwa akan su, zai zama sular warware ƙulle-ƙullen makirai, kuma hakan zai farantawa masoya, kuma ya baƙantawa maƙiya. Mun san yadda Jagora yake son ganin farin cikin masoyansa. Domin kuwa sau da yawa idan mukaje wajensa (Makarantar Annabi Yusuf) shine yake haƙur-ƙurtar damu, kuma yake bin hanyoyin da zasu kwantar mana da hankula. Madallah da Wannan Jagora...!
Natijar ita ce Malam yana son a jiyar da Al'ummah haƙiƙar girma da ƙimar Annabinsu daga bayanansa, ta hanyar kunnawa kotu domin ya shiga cikin record, domin mun sani masu hankali suna bibiyar wannan Shari'ah sau da ƙafa, wasu kuma har rubutawa suke, kenan akwai fa'ida a sanya cikakkun waɗancan jumloli da gaɓoɓi, wannan shi ne burin Shehin Malamin.
Abinda ya k**ata mu sani shine, Sheikh Abduljabbar ba matsoraci bane, domin kuwa matsoraci ba zai iya irin karatun da Malamin yake yi ba. Babu maganar tsoron ɗauri ko mutuwa daga ɓangaren Malamin mu. Mai tsoron ɗauri a kurku ba zai iya jiɓuntar lamarin Annabi da Iyalan Gidansa ba, musamman a wannan zamani.
Sanya waɗancan karauttuka da ake zargin akwai ɓatanci cikinsu, shi ne zaifi zama Maslaha ga Al'umma musamman masu neman gaskiya.
Dangane da batun Barrister Hashim, ya k**ata mu fahimci cewa:
Barrister Hashim Masoyi ne, kuma kishin Addini da Son Ganin an sami mafita a wannan Shari'ah shine hadafinsa.
Don haka, idan ana zaton Barrister Hashim ya aikata kuskure ne, yana da kyau abi hanya mafi kyau wajen gyara masa kuskurensa.
Yana da kyau mu daina gaggawa wajen yanke wa mutane hukunci, mu zama masu bada uzuri tareda buɗe ƙofofin tattaunawa domin samun dai-daito.
Allah Ya fito mana da jagora, cikin Girma da Buwaya Alfarmar Annabi da Iyalan Gidansa.
AKAFSAN MANAGEMENT
15/06/2022
A yau ranar Alhamis (9/06/2022), Mai Shari’ah Ibrahim Sarki Yola ya cigaba da Sauraren Shari’ar dake gudana tsakanin Sheikh Abduljabbar da Gwamnatin Jihar Kano.
Idan ba a mantaba a zaman da ya gabata, Mai Shari’a Alƙali Ibrahim Sarki Yola, ya umarci Barista Ɗalhatu Shehu Usman, Lauya Mai zaman kasa, cewa yazo domin tsayawa Sheikh Abdulhabbar a matsayin Lauyan kariya, a wannan Shari’ah. Don haka, Barista Dalhatu yazo kotu bisa umarnin Alƙalin.
Kamar yadda aka saba, Lauyoyin Gwamnati sun gabatar da kansu, haka shima Lauya mai tsayawa Sheikh Abduljabbar ya gabatar da kansa a gaban kotu bisa al’adar kotu.
Kotu (bisa jagorancin Alƙali Yola) ta fara da cewa: Bayan dogon nazari da kotu tayi, dangane da karɓar karatun da Shehin Malamin ya gabatar a matsayin shaida.
“To, ni fahimta ta babu adalci ace na karɓa na ajiye, ko kuma naji ni kaɗai a ɗaki. Zai fi zama adalci a kunna wannan karatu a kotu, gaban kowa da kowa a saurara”. Inji Alƙali Ibrahim Sarki Yola.
Sannan, kotu ta tambayi Lauyan Shehin Malamin: “Shin a shirye kake da a kunna wannan karatu?”
Lauyan Sheikh Abduljabbar: Ya amsa da cewa eh, “a shirye nake”.
Suma kuma Lauyoyin Gwamnati ba suyi s**a ba akan hakan.
Nan ta ke sai kotu tai umarni da a kunna wannan audio na karatun shehin Malamin, kuma an kunna karatun ne mai taken ‘JAUFUL FARAH NA 92’. Wanda Malamin ya gabatar a ranar Juma’ah (30/08/2019), a wurin karatunsa dake unguwar Sani Mainagge, ƙaramar Hukumar Gwale dake Jihar Kano, Nigeria.
An saurari karatun daga farko har ƙarshe, a gaban mutanen dake cikin wannan kotu, sai Alƙali ya tambayi Lauyoyin Gwamnati “shin ko kuna da tambayar da zaku yiwa Malamin akan karatun da aka kunna yanzu?”
Lauyoyin Gwamnati s**a amsa da cewa, suna buƙatar kotu ta basu kwafin wannan karatu, su koma suji shi a nutse.
Sai Alƙali ya tambayi Lauyan Sheikh Abduljabbar Kabara da cewa “shin ko kana da s**a akan abinda s**a roƙa?”
Lauyan Malamin yace: “Ina da s**a, ya k**ata idan suna da wata tambaya, to su yita yanzu, tunda dai a gaban kowa aka kunna wannan karatu, Musamman idan akayi la’akari da cewa wanda ake tuhuma yana tsare a Gidan kurkuku, lauyan ya kafa hujja da wani Littafin ‘TUHFATUL AHKAM…!”
Sai, Alƙali ya tambayi Lauyoyin Gwamnati, cewa ko me za kuce akan haka?
Layoyin Gwamnati: “Wannan audio da aka gabatar yanzu yana da alaƙa ta kusa da abinda mu keso muyi tambaya akansa. Wakilin Lauyoyi ya cigaba da cewa: Bisa waɗannan dalilai ne muke so kotu ta karɓi roƙonmu, ta bamu kwafin wannan karatu musaurara a nutse, sannan muma muna so mu gabatarwa da kotu fefen muryar dake hannunmu na shi Malamin.
A dai-dai wannan gaɓa ne, kotu ta tafi hutun rabin sa’a (mintuna 30).
Bayan dawowa daga hutun ne, Alƙali yace, dangane da roƙon da Lauyoyin Gwamnati s**ayi, na cewa a basu kwafin karatun, to kotu tayi umarnin da abasu wannan karatu, su saurara, hakan shine yafi k**a da adalci, bayan Hujjoji da kotu ta dogara dasu na wasu daga cikin Litattafan Musulunci, k**ar yadda Alƙali ya yi bayani.
A wannan gaɓa ne Mai Shari’a, Alkali Ibrahim Sarki Yola ya ɗage sauraren wannan Shari’ar zuwa ranar Alhamis (23/06/2022), a matsayin ranar da zai cigaba da sauraron wannan Shari’ah.
~ AKAFAN REPORTES