29/05/2026
MAI GIRMA SANATA WAMAKKO, TARE DA MAIGIRMA GWAMNA, AHMAD ALIYU. SUN HALARCI, SALLAR IDIN BABBAR SALLAH TA, BANA WATAU 1447, 2026. A MASALLACIN IDI DAKE SAKKWATO, TA TARAYYAR NAJERIYA.
A Ranar Larbar da ta Gabata ne. 27/05/2026 Maigirma Sanata. Dr. Aliyu Magatakarda Wamakko Sarkin Yamman Sakkwato, Sarkin Yakin Sakkwato, Kana Wakili A Majalisar Koli ta Majalisar Hadin kan Musulmi ta Duniya Mai Mazamni A Birnin Makkah Tare da Dan sa, Mai Girma Gwamnan Jihar Sakkwato, Alhaji Ahmad Aliyu Sakkwato, PhD, FCNA, ACIT. S**a Halarci Filin Idin Dake Sakkwato Domin Haduwa da Saurn 'Yan'uwan su Musulmi Wajjan Sallar Idin Babbar Sallah, da Zuwa Fadar Mai Alfarma Sarkin Musulmi. Domin Shaidar Bukukuwan Sallah, da Gabatarda Gaisuwar Sallah ga Mai Alfarma Sarkin Musulmi.
Muna Rokon Allah da ya Karbi Dukkan Ibadodimmu da Addu'o,immu Baki Daya, Kuma Allah ya Mai Maita Muna ta Badin Badada, Muna Cikin Koshin Lafiya da Walwala.
Jum'ah. 29/05/2026.
23/05/2026
GANAWAR MAIGIRMA SANATA. DR. ALIYU MAGATAKARDA WAMAKKO, DA AMININ SA, MAIGIRMA SHUGABAN KASAR TARAYYAR NAJERIYA, ALHAJI ASIWAJU AHMAD BOLA TINUBU. A GIDAN SA DAKE LEGOS. DA YAMMACIN JIYA JUM'AH, 21/05/2026
AKAN SHAWAR WARIN DA ZA SU TAIMAKI AL'UMMAR WANNAN KASA, DA KUMA ITA KANTA KASAR TA NAJERIYA. BISA GA ABABEN DA S**A ADDABI KASAR DA AL'UMMA. DA KUMA TATTAUNAWA AKAN ABINDA ZAI KAWO KYAUTATUWAR SAMARDA ZAMAN LAFIYA, DA KWANCIYAR HANKALI, MUSAMMAN A AREWACIN NAJERIYA, DA KUMA KASAR BAKI DAYA.
ASSABAR. 22/05/2026
19/05/2026
INNA LILLAHI WA'INNA ILAIHI RAJI'UN!
INNA LILLAHI WA'INNA ILAIHI RAJI'UN!!
INNA LILLAHI WA'INNA ILAIHI RAJI'UN!!!
Cikin Jimami da Kaduwa Ina Mai Bakin Cikin Sanarda ku, Allah ya yiwa Wani Magajimmu, Kuma Aminimmu, Kana Abokin Tafiyar mu, Rasuwa. Mai Suna Alhaji Mai'akwai Jaredi.
Allah yayi Masa Rasuwa ne, Acikin Daren Jiya Attanin. 18/05/2026. A Gidan sa Dake Unguwar Hajiya Halima. Anan Cikin Garin Sakkwato, ta Tarayyar Najeriya.
Za'ayi Masa Sallar Jana'iza A Gidan Nasa Dake Unguwar ta Hajiya Halima, Ayau Talata. 19/05/2026 da Misalin Karfe Biyar na Yamma.
Muna Rokon Allah da ya Jikan shi da Gafara, ya Yafe Masa Kura Kurran sa, ya Kyautata Makwancin sa, ya Kaddari Aljannar Firdausi Itace Makoma Agare shi.
Mu Kuma Idan tamu ta zo Allah yasa Mucika da Imani, ya Kyautata Karshemmu. Muna yiwa Iyali, 'Yan'uwa da Abokanen Arziki, Ta'aziyyar Wannan Rashin da Mukayi. Allah ya Bamu Hakurin Jure Wannan Rashin.
Talata. 19/05/2026
13/05/2026
INNA LILLAHI WA'INNA ILAIHI RAJI'UN!
INNA LILLAHI WA'INNA ILAIHI RAJI'UN!!
INNA LILLAHI WA'INNA ILAIHI RAJI'UN!!!
Cikin Jimami da Bakin Cikin da Mayarda Al'amari ga Mahaliccimmu Allah Swa, Ina Mai Bakin Cikin Sanarda ku Cewa, Allah ya Karbi Rayuwar Daya Daga Cikin Kannemmu, Kuma Mai Biyayya Gare mu. Rasuwa.
Mai Suna Alhaji Yusuf Ibrahim Gidan Kanawa Sakkwato. ya Rasu ne da Yammacin yau Larba. 13/05/2026. da Misalin Karfe 5:33pm. Na yamma A Assibitin Kwararru ta Sakkwato. A Sanadiyyar Gajeruwar Rashin Lafiya.
Anyi Masa Jana'iza. Anan Gidan mu Dake Gidan Kanawa Akan Titin Sultan Atiku Dake Cikin Birnin Sakkwato, ta Tarayyar Najeriya. Ayau Dinnan Larba. da Misalin Karfe Tara na Dare. 9:00pm.
Muna Rokon Allah da ya Jikan shi da Gafara ya Kyautata Makwancin sa, ya Yafe Masa Kura Kurran sa, ya Kaddari Aljannar Firdausi Itace Makoma Agare shi. Allah ya Albarkaci Iyalin da ya Bari. Idan Tamu ta zo Allah yasa Mucika da Kalimar Shahada. Allahumma Amin.
Larba. 13/05/2026.
25/04/2026
INNA LILLAHI WA'INNA ILAIHI RAJI'UN!
INNA LILLAHI WA'INNA ILAIHI RAJI'UN!!
INNA LILLAHI WA'INNA ILAIHI RAJI'UN!!!
Cikin Jimami da Kaduwa da Mayarda Al'amari ga Allah Swa. Ina Mai Bakin Cikin Sanarda ku Cewa Allah ya yiwa Daya Daga Cikin Abokanemmu Rasuwa. Watau Fagachin Sakkwato, Alhaji Shehu Muhammad Gyelgyel.
Allah ya Karbi Ransa ne A Assibitin Koyarwa ta Jami'ar Usman Damfodiyo Dake nan Sakkwato, da Sanyin Safiyar yau. Assabar. 25/04/2026. Bayan Fama da Doguwar Jinyar da ya Dade yana yi.
Za'ayi Masa Jana'iza ne, A Masallacin Jum'ah na Isah Mai Kware. Dake Akan Titin Shehu Shagari Anan Cikin Garin Sakkwato. da Karfe 12:00pm. Na Rana. Muna Rokon Allah da ya Jikan shi da Gafara, ya Yafe Masa Kura Kurran sa, ya Kyautata Makwancin sa, ya Kaddari Aljannar Firdausi Itace Makoma Agare shi. Ba Shakka Munyi Rashi Masoyi, Kuma Amini na Tsawon Lokaci, Munyi Fadi Tashin Rayuwa Iri Iri Tare Dashi, Muna Rokon Allah da Idan tamu ta zo Muyi Kyakkyawan Karshe Mucika da Imani. Allahumma Amin.
Assabar. 25/04/2026
15/04/2026
INNA LILLAHI WA'INNA ILAIHI RAJI'UN!
INNA LILLAHI WA'INNA ILAIHI RAJI'UN!!
INNA LILLAHI WA'INNA ILAIHI RAJI'UN!!!
Cikin Kaduwa Jimami da Yarda da Hukumcin da Allah ya Kaddara Ina Mai Bakin Cikin Sanarda ku Cewa Allah ya yiwa Alhaji Isah Yaro Maitaya. Anguwar Malammai Sakkwato Rasuwa.
Wanda Akafi Sani Acan Suleja da Alhaji Isah Imam Sar. Malamman Bakin Eku Kaduna Road Suleja
Dan Kasuwa Dake Zaune Anan Checheniya. Suleja Kaduna Road Suleja. Ta Jihar Niger A Tarayyar Najeriya.
Allah ya yi Masa Rasuwa ne A Jiya. Talata. 14/04/2026. A Gidan sa Dake Checheniya. Suleja. Akayi Masa Jana'iza Yau Larba. 15/04/2026 A Masallacin Jum'ah. na Al'ansar Dake Akan Titin Kaduna Road Suleja. da Karfe 9:30am. na Safe. Aka Bisne shi. A Makabartar Bayan General Hospital Dake Akan Titin Church Road Suleja. Wanda ya Jagoranci yi Masa Sallar Jana'iza Shine Malam Bello Hayi Dake Zaune Anan Suleja Kaduna Road.
Ana Karbar Ta'aziyyar Rasuwar sa A Gidan sa Dake Bakin Eku Kaduna Road Suleja. da Kuma Gidan su Dake Unguwar Malammai Kofar Atiku Akan Titin Atiku Road Anan Cikin Garin Sakkwato ta Tarayyar Najeriya.
Muna Rokon Allah da ya Karbi Bakuncin sa, ya Jikan shi da Gafara, ya Yafe Masa Kura Kurran sa, ya Kyautata Makwancin sa, ya Kaddari Aljannar Firdausi Itace Makoma Agare shi. Kuma Allah ya Albarkaci Iyalin da ya Bari.
Larba. 15/04/2026.