17/08/2026
TSAKANIN SON ANNABI ﷺ DA MAULUDI
— Rubutu na biyu (02)
YAYA SAHABBAN ANNABI ﷺ S**A SO SHI?
بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيمِ
A wannan zangon, za mu yi nazari akan irin ƙauna da Soyayya da Sahabbai s**a nunawa Annabi ﷺ
Domin idan muna son sanin yadda ake son Annabi ﷺ, to Sahabban sa su ne mafi dacewa da za mu duba. Domin;
1. Su ne waɗanda s**a rayu da shi kai tsaye
2. Su ne waɗanda s**a zauna tare da shi.
3. Su ne waɗanda s**a ji maganarsa kuma s**a ɗauki karatu a gaban shi kai tsaye
4. Su ne waɗanda s**a sadaukar da dukiyoyin su, rayukan su da ƙasashen su domin addinin da ya zo da shi.
Saboda haka, ƙaunar da s**a nuna masa ita ce ƙaunar da za mu yi nazari a kai. WANNAN KUMA SHINE ADALCI
Daga cikin mafi ban mamaki na ƙaunar Sahabbai ga Annabi ﷺ akwai yadda suke fifita shi a kan kansu.
Allah سبحانه وتعالى Ya ce:
النَّبِيُّ أَوْلَىٰ بِالْمُؤْمِنِينَ مِنْ أَنْفُسِهِمْ
Ma'ana:
“Annabi ya fi cancanta ga muminai fiye da kawunansu.”
Suratul-Ahzāb: 6.
Wannan ita ce ma'anar ƙauna ta gaskiya:
Annabi ﷺ ya kasance mafi soyuwa, mafi daraja, kuma mafi fifiko a wajen mumini fiye da son kansa.
Umar ibn al-Khaṭṭāb رضي الله عنه ya taɓa cewa:
يَا رَسُولَ اللَّهِ، لَأَنْتَ أَحَبُّ إِلَيَّ مِنْ كُلِّ شَيْءٍ إِلَّا مِنْ نَفْسِي
“Ya Manzon Allah! Lallai kai ne mafi soyuwa a gare ni fiye da komai, sai dai kaina.”
Sai Annabi ﷺ ya ce:
«لَا، وَالَّذِي نَفْسِي بِيَدِهِ، حَتَّى أَكُونَ أَحَبَّ إِلَيْكَ مِنْ نَفْسِكَ»
“Ba haka ba, ina rantsuwa da Wanda raina yake a hannun sa, har sai na fi zama abin ƙauna a gare ka fiye da kanka.”
Sai Umar رضي الله عنه ya ce:
فَإِنَّهُ الْآنَ، وَاللَّهِ، لَأَنْتَ أَحَبُّ إِلَيَّ مِنْ نَفْسِي
“Yanzu kuwa, wallahi, kai ne mafi soyuwa a gare ni fiye da kaina.”
Sai Annabi ﷺ ya ce:
«الْآنَ يَا عُمَرُ»
“Yanzu, ya Umar.”
Sahih al-Bukhari.
Abun lura;
KA GA KENAN HAR SAHABBAI MA ANA MASU GYARA A CIKIN IRIN SOYAYYAR DA ZA SU YIWA SHUGABA ﷺ
Bayan wafatin Annabi ﷺ, lokacin da aka samu fitinar waɗanda s**a ƙi ba da zakka, Abu Bakr رضي الله عنه ya tsaya tsayin daka.
Wasu daga cikin Sahabbai sun ga ya fi dacewa a tausasa musu.
Amma Abu Bakr رضي الله عنه ya ce:
وَاللَّهِ لَأُقَاتِلَنَّ مَنْ فَرَّقَ بَيْنَ الصَّلَاةِ وَالزَّكَاةِ
“Wallahi, zan yaƙi wanda ya raba tsakanin sallah da zakka.”
Sannan ya bayyana dalilinsa da cewa Annabi ﷺ ya bar wannan koyarwar.
Sahih al-Bukhari.
Ka ga Sayyiduna Abubakar رضي الله عنه ya gane cewar ƙaunar Shugaba ﷺ itace a cigaba da tafiya akan karantarwa sa bayan baya nan...
Daga cikin Sahabbai da s**a kasance kusa da Annabi ﷺ sosai akwai Abdullah ibn Mas'ud رضي الله عنه.
Hudhayfah رضي الله عنه ya kasance yana ganin yadda Ibn Mas'ud yake bin tafarkin Annabi ﷺ.
An tambaye shi game da wanda ya fi k**a da Annabi ﷺ a:
سَمْتًا وَهَدْيًا وَدَلًّا
wato a halayya, tafiya, da ɗabi'ar rayuwa.
Sai Hudhayfah ya ce:
مَا أَعْرِفُ أَحَدًا أَقْرَبَ سَمْتًا وَهَدْيًا وَدَلًّا بِالنَّبِيِّ ﷺ مِنِ ابْنِ أُمِّ عَبْدٍ
“Ban san wani da ya fi Ibn Umm Abd kusa da Annabi ﷺ a tafiya, shiriya da ɗabi'a ba.”
Sahih al-Bukhari, 3762
Kun lura cewar a rayuwar Abdullahi bin Mas'ud رضي الله عنه ta yau da kullum aka gano shi mai ƙaunar Annabi ﷺ ne, ba faɗi ya yi da baki ba kawai...?
Akwai ƙissar da ta shahara game da Umar رضي الله عنه, lokacin da ya sumbaci Hajarul-Aswad ya ce:
إِنِّي لَأَعْلَمُ أَنَّكَ حَجَرٌ، لَا تَضُرُّ وَلَا تَنْفَعُ، وَلَوْلَا أَنِّي رَأَيْتُ النَّبِيَّ ﷺ يُقَبِّلُكَ مَا قَبَّلْتُكَ
Ma'ana:
“Na san cewa kai dutse ne; ba ka iya cutarwa kuma ba ka iya amfanarwa. Da ban ga Annabi ﷺ yana sumbatarka ba, da ban sumbace ka ba.”
Sahih al-Bukhari da Sahih Muslim.
Wannan ƙissa ta Umar رضي الله عنه tana nuna cewa ƙaunar Sahabbai ga Annabi ﷺ ta kai su ga cewa: “Na ga Annabi ﷺ yana yin haka, saboda haka nima nake yi... Kenan aikin shi suke kwaikwayo.
Ɗan shi, Abdullah bin Umar رضي الله عنهما ya kasance yana ƙoƙarin kwaikwayon abin da ya gani daga Manzon Allah ﷺ, har ana mishi laƙabi da 'ma'aboci Sunnar Annabi ﷺ'
An ruwaito cewa:
كَانَ ابْنُ عُمَرَ رَضِيَ اللَّهُ عَنْهُمَا إِذَا اسْتَلَمَ الْحَجَرَ قَبَّلَ يَدَهُ
Ma'ana:
“Idan Ibn Umar رضي الله عنهما ya taɓa Hajarul-Aswad, sai ya sumbaci hannunsa.”
An kuma ruwaito cewa Ibn Umar رضي الله عنهما ya ce:
مَا تَرَكْتُ اسْتِلَامَ هَذَيْنِ الرُّكْنَيْنِ فِي شِدَّةٍ وَلَا رَخَاءٍ مُنْذُ رَأَيْتُ رَسُولَ اللَّهِ ﷺ يَسْتَلِمُهُمَا
Ma'ana:
“Ban taɓa barin taɓa waɗannan ginshiƙai guda biyu ba, cikin wahala ko sauƙi, tun lokacin da na ga Manzon Allah ﷺ yana taɓa su.”
Sahih Muslim.
Yana yin wannan aiki ne saboda me?
Saboda ya ga ma'aiki ﷺ ya yi...
Saboda kada mu tsawaita za mu tsaya a nan, za mu cigaba a rubutu na gaba in sha'a Allah
Tabbas a rayuwar Sahabbai رضي الله عنهم za mu fahimci;
1. Suna bin Sunnar sa.
2. Suna girmama umarnin sa.
3. Suna barin abin da ya hana.
4. Suna gabatar da maganar sa akan son zuciya.
5. Suna ƙoƙarin kwaikwayon halayen sa.
6. Suna koyar da Sunnar sa ga wasu.
7. Suna ƙin abin da ya saɓa wa koyarwarsa.
Yanzu ka tambayi kan ka, KAIMA IRIN WANNAN CE SOYAYYAR KA GA ANNABI ﷺ ???
✍️ To be continued...
✍️Minhajus Sunnah Academy, Nigeria
✍️ MHS Media Team
15/08/2026
15/08/2026
14/08/2026