Minhajus Sunnah Academy, Nigeria

Minhajus Sunnah Academy, Nigeria

Share

للدعوة والنشر الإسلام علی ضوءالکتاب وسنة خیر الأنام

17/08/2026

TSAKANIN SON ANNABI ﷺ DA MAULUDI

— Rubutu na biyu (02)

YAYA SAHABBAN ANNABI ﷺ S**A SO SHI?

بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيمِ
A wannan zangon, za mu yi nazari akan irin ƙauna da Soyayya da Sahabbai s**a nunawa Annabi ﷺ
Domin idan muna son sanin yadda ake son Annabi ﷺ, to Sahabban sa su ne mafi dacewa da za mu duba. Domin;
1. Su ne waɗanda s**a rayu da shi kai tsaye
2. Su ne waɗanda s**a zauna tare da shi.
3. Su ne waɗanda s**a ji maganarsa kuma s**a ɗauki karatu a gaban shi kai tsaye
4. Su ne waɗanda s**a sadaukar da dukiyoyin su, rayukan su da ƙasashen su domin addinin da ya zo da shi.
Saboda haka, ƙaunar da s**a nuna masa ita ce ƙaunar da za mu yi nazari a kai. WANNAN KUMA SHINE ADALCI

Daga cikin mafi ban mamaki na ƙaunar Sahabbai ga Annabi ﷺ akwai yadda suke fifita shi a kan kansu.
Allah سبحانه وتعالى Ya ce:
النَّبِيُّ أَوْلَىٰ بِالْمُؤْمِنِينَ مِنْ أَنْفُسِهِمْ
Ma'ana:
“Annabi ya fi cancanta ga muminai fiye da kawunansu.”
Suratul-Ahzāb: 6.
Wannan ita ce ma'anar ƙauna ta gaskiya:
Annabi ﷺ ya kasance mafi soyuwa, mafi daraja, kuma mafi fifiko a wajen mumini fiye da son kansa.

Umar ibn al-Khaṭṭāb رضي الله عنه ya taɓa cewa:
يَا رَسُولَ اللَّهِ، لَأَنْتَ أَحَبُّ إِلَيَّ مِنْ كُلِّ شَيْءٍ إِلَّا مِنْ نَفْسِي
“Ya Manzon Allah! Lallai kai ne mafi soyuwa a gare ni fiye da komai, sai dai kaina.”
Sai Annabi ﷺ ya ce:
«لَا، وَالَّذِي نَفْسِي بِيَدِهِ، حَتَّى أَكُونَ أَحَبَّ إِلَيْكَ مِنْ نَفْسِكَ»
“Ba haka ba, ina rantsuwa da Wanda raina yake a hannun sa, har sai na fi zama abin ƙauna a gare ka fiye da kanka.”
Sai Umar رضي الله عنه ya ce:
فَإِنَّهُ الْآنَ، وَاللَّهِ، لَأَنْتَ أَحَبُّ إِلَيَّ مِنْ نَفْسِي
“Yanzu kuwa, wallahi, kai ne mafi soyuwa a gare ni fiye da kaina.”
Sai Annabi ﷺ ya ce:
«الْآنَ يَا عُمَرُ»
“Yanzu, ya Umar.”
Sahih al-Bukhari.
Abun lura;
KA GA KENAN HAR SAHABBAI MA ANA MASU GYARA A CIKIN IRIN SOYAYYAR DA ZA SU YIWA SHUGABA ﷺ

Bayan wafatin Annabi ﷺ, lokacin da aka samu fitinar waɗanda s**a ƙi ba da zakka, Abu Bakr رضي الله عنه ya tsaya tsayin daka.
Wasu daga cikin Sahabbai sun ga ya fi dacewa a tausasa musu.
Amma Abu Bakr رضي الله عنه ya ce:
وَاللَّهِ لَأُقَاتِلَنَّ مَنْ فَرَّقَ بَيْنَ الصَّلَاةِ وَالزَّكَاةِ
“Wallahi, zan yaƙi wanda ya raba tsakanin sallah da zakka.”
Sannan ya bayyana dalilinsa da cewa Annabi ﷺ ya bar wannan koyarwar.
Sahih al-Bukhari.
Ka ga Sayyiduna Abubakar رضي الله عنه ya gane cewar ƙaunar Shugaba ﷺ itace a cigaba da tafiya akan karantarwa sa bayan baya nan...

Daga cikin Sahabbai da s**a kasance kusa da Annabi ﷺ sosai akwai Abdullah ibn Mas'ud رضي الله عنه.
Hudhayfah رضي الله عنه ya kasance yana ganin yadda Ibn Mas'ud yake bin tafarkin Annabi ﷺ.
An tambaye shi game da wanda ya fi k**a da Annabi ﷺ a:
سَمْتًا وَهَدْيًا وَدَلًّا
wato a halayya, tafiya, da ɗabi'ar rayuwa.
Sai Hudhayfah ya ce:
مَا أَعْرِفُ أَحَدًا أَقْرَبَ سَمْتًا وَهَدْيًا وَدَلًّا بِالنَّبِيِّ ﷺ مِنِ ابْنِ أُمِّ عَبْدٍ
“Ban san wani da ya fi Ibn Umm Abd kusa da Annabi ﷺ a tafiya, shiriya da ɗabi'a ba.”
Sahih al-Bukhari, 3762
Kun lura cewar a rayuwar Abdullahi bin Mas'ud رضي الله عنه ta yau da kullum aka gano shi mai ƙaunar Annabi ﷺ ne, ba faɗi ya yi da baki ba kawai...?

Akwai ƙissar da ta shahara game da Umar رضي الله عنه, lokacin da ya sumbaci Hajarul-Aswad ya ce:
إِنِّي لَأَعْلَمُ أَنَّكَ حَجَرٌ، لَا تَضُرُّ وَلَا تَنْفَعُ، وَلَوْلَا أَنِّي رَأَيْتُ النَّبِيَّ ﷺ يُقَبِّلُكَ مَا قَبَّلْتُكَ
Ma'ana:
“Na san cewa kai dutse ne; ba ka iya cutarwa kuma ba ka iya amfanarwa. Da ban ga Annabi ﷺ yana sumbatarka ba, da ban sumbace ka ba.”
Sahih al-Bukhari da Sahih Muslim.

Wannan ƙissa ta Umar رضي الله عنه tana nuna cewa ƙaunar Sahabbai ga Annabi ﷺ ta kai su ga cewa: “Na ga Annabi ﷺ yana yin haka, saboda haka nima nake yi... Kenan aikin shi suke kwaikwayo.

Ɗan shi, Abdullah bin Umar رضي الله عنهما ya kasance yana ƙoƙarin kwaikwayon abin da ya gani daga Manzon Allah ﷺ, har ana mishi laƙabi da 'ma'aboci Sunnar Annabi ﷺ'
An ruwaito cewa:
كَانَ ابْنُ عُمَرَ رَضِيَ اللَّهُ عَنْهُمَا إِذَا اسْتَلَمَ الْحَجَرَ قَبَّلَ يَدَهُ
Ma'ana:
“Idan Ibn Umar رضي الله عنهما ya taɓa Hajarul-Aswad, sai ya sumbaci hannunsa.”
An kuma ruwaito cewa Ibn Umar رضي الله عنهما ya ce:
مَا تَرَكْتُ اسْتِلَامَ هَذَيْنِ الرُّكْنَيْنِ فِي شِدَّةٍ وَلَا رَخَاءٍ مُنْذُ رَأَيْتُ رَسُولَ اللَّهِ ﷺ يَسْتَلِمُهُمَا
Ma'ana:
“Ban taɓa barin taɓa waɗannan ginshiƙai guda biyu ba, cikin wahala ko sauƙi, tun lokacin da na ga Manzon Allah ﷺ yana taɓa su.”
Sahih Muslim.
Yana yin wannan aiki ne saboda me?
Saboda ya ga ma'aiki ﷺ ya yi...

Saboda kada mu tsawaita za mu tsaya a nan, za mu cigaba a rubutu na gaba in sha'a Allah

Tabbas a rayuwar Sahabbai رضي الله عنهم za mu fahimci;
1. Suna bin Sunnar sa.
2. Suna girmama umarnin sa.
3. Suna barin abin da ya hana.
4. Suna gabatar da maganar sa akan son zuciya.
5. Suna ƙoƙarin kwaikwayon halayen sa.
6. Suna koyar da Sunnar sa ga wasu.
7. Suna ƙin abin da ya saɓa wa koyarwarsa.
Yanzu ka tambayi kan ka, KAIMA IRIN WANNAN CE SOYAYYAR KA GA ANNABI ﷺ ???
✍️ To be continued...
✍️Minhajus Sunnah Academy, Nigeria
✍️ MHS Media Team

17/08/2026
15/08/2026

TSAKANIN SON ANNABI ﷺ DA MAULUDI

— Rubutu na ɗaya (01)

HAƘƘIN ANNABI ﷺ A KANMU: Son shi dole ne, ba zaɓi ba
بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيمِ
Dukkan yabo da godiya sun tabbata ga Allah سبحانه وتعالى. Tsira da amincin Allah su tabbata ga Annabin mu Muhammad ﷺ, da iyalan sa, Sahabban sa da waɗanda s**a bi tafarkin su da kyautatawa har zuwa ranar Alƙiyama.

Gabatarwa
A cikin wannan jerin rubuce-rubucen, za mu yi magana ne kan:
«TSAKANIN SON ANNABI ﷺ DA MAULUDI»
Abu na farko shine mu san abubuwa k**ar haka;
1. Menene haƙƙin Annabi ﷺ a kanmu?
2. Menene ma'anar son Annabi ﷺ?
3. Yaya sahihiyar ƙauna take bayyana?
4. Kuma shin duk abin da ake yi da sunan ƙaunar Annabi ﷺ yana cikin koyarwarsa?
Idan muka fahimci waɗannan tushe, za mu iya fahimtar sauran batutuwan cikin adalci da hujja, ba da son zuciya ba.

SON ANNABI ﷺ BA ZABI BA NE
Daya daga cikin manyan haƙƙoƙin Annabi ﷺ a kan al'ummarsa shi ne a so shi, kuma wannan ba kawai kyakkyawan hali ba ne; yana daga cikin cikar imani.
Annabi ﷺ ya ce:
«لَا يُؤْمِنُ أَحَدُكُمْ حَتَّى أَكُونَ أَحَبَّ إِلَيْهِ مِنْ وَالِدِهِ وَوَلَدِهِ وَالنَّاسِ أَجْمَعِينَ»
Ma'ana:
“Babu ɗayanku da zai zama cikakken mai imani har sai na fi zama abin ƙauna a gare shi fiye da mahaifinsa, ɗansa, da dukkan mutane.”
📚 Sahih al-Bukhari, Hadisi na 15.
- Wannan yana nuna girman matsayin ƙaunar Manzon Allah ﷺ a cikin imani.

DOLE NE MUSULMI MAI HANKALI YA SO ANNABI ﷺ
1. Saboda shi ne wanda Allah Ya aiko mana da saƙonsa.
2. Ta hannunsa ne muka san Tauhidi, ya fidda mu daga duhun shirka zuwa hasken Tauhidi, da sauran diffai
3. Ta hannunsa ne muka san yadda ake sallah.
4. Ta hannunsa ne muka san azumi, zakka, Hajji da sauran ibadodi.
5. Ta hannunsa ne Allah ya nuna mana hanyar Alƙur'ani da Sunnah.
Saboda haka, ƙaunar Manzon Allah ﷺ tana da alaƙa kai tsaye da ƙaunar Allah.
Allah سبحانه وتعالى Ya ce:
قُلْ إِن كُنتُمْ تُحِبُّونَ اللَّهَ فَاتَّبِعُونِي يُحْبِبْكُمُ اللَّهُ وَيَغْفِرْ لَكُمْ ذُنُوبَكُمْ ۗ وَاللَّهُ غَفُورٌ رَّحِيمٌ
Ma'ana:
“Ka ce: Idan kuna son Allah, to ku bi ni; Allah zai so ku, kuma Ya gafarta muku zunubanku. Kuma Allah Mai gafara ne, Mai jin ƙai.”
📖 Suratu Āli-Imrān: 31.
Wannan aya tana koya mana wani babban ƙa'ida:
Ƙaunar Allah ta gaskiya tana buƙatar bin Manzon Sa ﷺ.
Ba wai mutum ya ce:
“Ina son Allah, ina son Manzon Allah ﷺ”
amma a aikace ya ƙi bin Sunnah.

- ALAMAR SON ANNABI ﷺ ITA CE BINSA
Ƙauna ta gaskiya tana haifar da biyayya.
Allah Ya ce:
وَمَا آتَاكُمُ الرَّسُولُ فَخُذُوهُ وَمَا نَهَاكُمْ عَنْهُ فَانْتَهُوا
Ma'ana:
“Abin da Manzo ya ba ku, ku karɓe shi; abin da ya hana ku, ku bar shi.”
📖 Suratul-Hashr: 7.
Don haka, daga cikin manyan alamomin son Annabi ﷺ akwai:
1. Bin Sunnarsa.
2. Gaskata duk abinda ya bada labarin sa
2. Yin biyayya ga umarnin sa.
3. Barin abin da ya hana.
4. Girmama koyarwar sa.
5. Gabatar da Sunnar sa idan son zuciya ya yi karo da ita.
Annabi ﷺ ya ce:
«كُلُّ أُمَّتِي يَدْخُلُونَ الْجَنَّةَ إِلَّا مَنْ أَبَى»
Sai Sahabbai s**a tambaya: “Ya Manzon Allah, wa zai ƙi?”
Sai ya ce:
«مَنْ أَطَاعَنِي دَخَلَ الْجَنَّةَ، وَمَنْ عَصَانِي فَقَدْ أَبَى»
Ma'ana:
“Dukkan al'ummata za su shiga Aljanna sai wanda ya ƙi.” Sai ya bayyana cewa: “Wanda ya yi mini biyayya zai shiga Aljanna, wanda ya saɓa mini, shi ne ya ƙi.”
📚 Sahih al-Bukhari, 7280.

- SONSA YANA BUKATAR GABATAR DA MAGANARSA
Idan mutum yana son Annabi ﷺ da gaske, to idan aka kawo masa:
قال رسول الله ﷺ
“Manzon Allah ﷺ ya ce...”
bai k**ata son zuciya, al'ada, ko abin da mutum ya saba da shi su zama sama da maganar Manzon Allah ﷺ ba.
Allah Ya ce:
فَلْيَحْذَرِ الَّذِينَ يُخَالِفُونَ عَنْ أَمْرِهِ أَنْ تُصِيبَهُمْ فِتْنَةٌ أَوْ يُصِيبَهُمْ عَذَابٌ أَلِيمٌ
Ma'ana:
“Waɗanda suke saɓa wa umarninsa su kiyaye, kada wata fitina ta same su ko wani azaba mai raɗaɗi ya same su.”

An ruwaito cewa Al-Hasan ibn Muhammad ibn al-Hanafiyyah yana cewa;
تَعْصِي الإِلَهَ وَأَنْتَ تَزْعُمُ حُبَّهُ
هَذَا لَعَمْرِي فِي الْفِعَالِ بَدِيعُ
لَوْ كَانَ حُبُّكَ صَادِقًا لَأَطَعْتَهُ
إِنَّ الْمُحِبَّ لِمَنْ يُحِبُّ مُطِيعُ
Ma'ana:
1. “Kana saɓa wa Allah alhali kana da'awar kana son Sa?!
Wannan, wallahi, abu ne mai ban mamaki a cikin ayyuka.
2. Da ace ƙaunarka ta kasance ta gaskiya, da ka yi masa biyayya;
Domin lallai mai ƙauna ga wanda yake ƙauna, mai biyayya ne gare shi.”

Wannan baitin yana ɗauke da darasi mai girma:
Ƙauna ba magana ce kawai ba.
Idan kana son Annabi ﷺ:
1. Kana son abin da ya zo da shi.
2. Kana girmama Sunnarsa.
3. Kana ƙoƙarin bin tafarkinsa.
4. Kana ƙin abin da ya hana.
5. Kana gabatar da koyarwarsa a kan son zuciyarka.

Don haka ana ganin ƙaunar Annabi ﷺ ne a cikin rayuwar musulmi gaba ɗaya,
1. mu'amalar sa, ta cikin gida da waje
2. Sallar sa
3. Sa tufafin sa
4. Cin abincin sa
5. Kai, hatta biyan buƙata sai da ya koyar, ka yi koyi da shi

Don haka soyayyar shi ﷺ ba sau ɗaya a shekara take bayyana ba, kullum ake son ganin ta tare da musulmi...
✍️ To be continued....
✍️ Minhajus Sunnah Academy, Nigeria
✍️ MHS Media Team

Photos from Minhajus Sunnah Academy, Nigeria's post 15/08/2026

Alhamdulillah !!

Da yaddar Allah Daura ta kammala da yaddar Allah,Muna ƙara gode masa bisa Ni"imar da yayi mana🙏🙏.

In'sha Allahu,Clip ɗin karatu na nan tape da izinin Allah.

Photos from Minhajus Sunnah Academy, Nigeria's post 14/08/2026

Ma,sha Allahu,Kammaluwar Muhadara kenan da yaddar Allah,Da fuskoki cike da raha da Farinciki.

Allah yasa muna da rabon sake haduwa da Yaddar Allah.

14/08/2026

Ga wasu littafai da Mallam ya wallafa.In'sha Allah da izinin Allah gasunan a Ta kaice,Harda Memory card Mai dauke da Darruss**a fiye da dari takwas,In'sha Allahu

Alllah yasa mudace🙏🙏🙏..

14/08/2026

Manufa da gabatarwar su Tare wasu littafai da Mallam ya wallafa.In'sha Allah da izinin Allah gasunan a
Ta kaice,Harda Memory card Mai dauke da Darruss**a fiye da dari takwas,In'sha Allahu

Alllah yasa mudace🙏🙏🙏..

Want your school to be the top-listed School/college in Sagamu?

Click here to claim your Sponsored Listing.

Location

Category

Telephone

Website

Address


Akarigbo
Sagamu