Muhammad Sani Sa'idu Ringim

Muhammad Sani Sa'idu Ringim محمد ثاني بن الشيخ سعيد أحمد نائبي رنغم

05/09/2025

Narrated Abu Sa`id Al-Khudri: Allah's Messenger (ﷺ) Said, "The taking of a bath on Friday is compulsory for every Muslim who has attained the age of puberty."
Sahih Bukhari.

27/04/2022

Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gareshi Ya ce: "... Wanda ya raya daren Lailatul ƙadari da imani da neman lada a gurin Allah za'a gafartamasa abin da ya gabata na zunubansa." Bukhari hadisi na 2014.

17/07/2021

FALALAR AZUMIN RANAR ARFÀ

Daga Abi Ƙatada (R.A) Yace: An tambayi Manzon (S.A.W) dangane da Azumin ranar Arfà sai Yace: "Yana kankare zunubin shekarar da ta shuɗe da wacce ake ciki." Muslim ne ya rawaito.

A duba Riyadussalihin Hadisi na 1250 Darul Fikir Ɗaba'ar 2008. Sannan yana nan a cikin dogon Hadisi a Sahihu Muslim ƙarƙashin Hadisi na 1162.

Allah Ya bada ikon yi,

03/05/2021

FALALAR SALLAR WALAHA
DAGA
MUHAMMAD SANI SA’IDU
[email protected]
Saƙo kawai: 09031705769
1 RAJAB, 1442 A.H/ 13 FEBRUARY, 2021 A.D
Dukkan godiya ta tabbata ga Allah Ubangijin halittu, tsira da aminci su tabbata ga shugaban mu Annabi Muhammad da iyalan sa da shabban sa da waɗanda s**a biyo bayan su da kyautatawa har zuwa ranar sakamako.
Ya ƴan’uwa musulmai ! Sallar walaha tana da falalar gaske kuma lokacin da ake yinta shi ne lokacin da rana ta fara zafi, ya danganta da irin yanayin da aka wayi gari da shi. Amma za'a iya ɗauka kamar ƙarfe goma shine abin da yafi domin rana ta take da zafii a wannnan lokacin. Amman idan mutum yana da uzuri. Zai iya yinta ƙasa da ƙarfe goma, saboda a riski falalar da ake nema domin gudun wofantar da ita ga sashen masu sakko su bar gida. Sannan Annabi (S.A.W) ya ambaceta da sallar masu neman tuba inda yace: “Sallar masu neman tuba lokacin da ɗan dalo yake ƙonewa”. Muslim ne ya rawaito.
Daga Aisha (R.A) ta ce: “Manzon Allah (S.A.W) yana sallatar walaha raka’a huɗu kuma yana daɗa abin da Allah ya so”. Muslim ne ya rawaito.
Daga Abi Zar (R.A) Daga Annabi (S.A.W) Ya ce: “Yana wayar gari akan kowacce gaɓa ta ɗayanku ladan sadaka, kowanne tasbihi sadaka ne, kowacce Alhamdullah sadaka ce, kowacce Hailala sadaka ce, kowacce Kabbara sadaka ce, umarni da kyakkyawa sadaka ne, hani da aikata mummuna sadaka ne, yana isuwa daga wancan Raka'a guda biyu da zai yisu na walaha”. Muslim ne ya raiwato.
Daga Abi Huraira (R.A) ya ce: “Maƙaunaci na (S.A.W) ya yimin wasiyya da Azumin kwana uku a kowanne wata, da raka’oin walaha, da yin wutiri kafin na kwanta”. Bukhari da Muslim.
A ƙarshe, ina roƙon Allah (S.W.T) ya sanya wannan aiki ya zamanto tsarkakakke, kuma ya sanya shi ya kasance mai sauƙi ta yadda musulmai da yawa za su amfana da shi, Amin. Sannan ina roƙon duk wanda ya amfana da wannan fa’ida da ya yi min addu’a ta alheri da iyayena da malamaina da maƙaunatan mu.

Address

Nasarawa Ringim
Ringim

Telephone

+2349031705769

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Muhammad Sani Sa'idu Ringim posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The School

Send a message to Muhammad Sani Sa'idu Ringim:

Shortcuts

Share

Category