Ayzan Multimedia

Ayzan Multimedia Contact information, map and directions, contact form, opening hours, services, ratings, photos, videos and announcements from Ayzan Multimedia, Kano.

Ayzan Group (Official) – Managing:
• Ayzan Multimedia – 📰 News & Media
• Tamkeen Qur’anic Channel – 📖 Qur’anic Recitation
• المجالس المكثفة لتكوين العلماء – 📚 Islamic Books & Lessons
• Ayzan Islamic Channel – ☪️ Sunnah & History

27/05/2026
🕌 DA DUMI-DUMI 🕌An tabbatar da ganin jinjirin watan Ramadan 1447H a Saudi Arabia.Hukumar kula da harkokin shari’a da gan...
17/02/2026

🕌 DA DUMI-DUMI 🕌
An tabbatar da ganin jinjirin watan Ramadan 1447H a Saudi Arabia.

Hukumar kula da harkokin shari’a da ganin wata ta sanar da cewa, za a fara azumin watan Ramadan daga daren yau, wanda ya yi daidai da shekarar 2026 Miladiyya.

Ramadan wata ne na rahama, gafara da kubuta daga wuta. Wata ne da Al-Qur’ani ya sauka, kuma lokaci ne na ƙara kusanci da Allah ta hanyar azumi, sallah (Qiyamul-Layl), sadaqa da sauran ibadu.

Muna roƙon Allah ﷻ Ya karɓi azuminmu, tsayuwar darenmu da addu’o’inmu, Ya sa mu dace da cin moriyar wannan wata mai albarka

Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf ya ƙaddamar da sabuwar hula da take nuna goyon baya ga Shugaban Ƙasa, Bola Tinubu y...
16/02/2026

Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf ya ƙaddamar da sabuwar hula da take nuna goyon baya ga Shugaban Ƙasa, Bola Tinubu yayin da za a yi bikin karɓar sa zuwa jam'iyyar APC a yau a jihar Kano.

Hadin gwiwar jami’an tsaro sun lalata manyan sansanonin ’yan bindiga uku a Jihar Kogi tare da kubutar da wasu mutanen da...
16/02/2026

Hadin gwiwar jami’an tsaro sun lalata manyan sansanonin ’yan bindiga uku a Jihar Kogi tare da kubutar da wasu mutanen da aka yi garkuwa da su a wuraren.

Arewa Updates ta rawaito cewa, wannan na cikin sanarwar da Kwamishinan Yada Labara na Jihar Kogi, Kingsley Femi Fanwo, ya fitar a ranar Lahadi 15 ga Fabrairu 2026.

Sanarwar ta ce hadin gwiwar ofishin Mai ba Shugaban kasa shawara kan Tsaro, rundunar Sojin ƙasar nan ta 12, rundunar ruwa, rundunar sama, ’yan sanda, jami’an DSS da kuma kungiyoyin sa kai da mafarauta ne s**a kai farmakin.

Sanarwar ta kara da cewa an lalata sansanonin gaba daya tare da kubutar da mutanen da aka tsare a wuraren, yayin da wasu da ake zargi s**a rasa rayukansu a yayin artabun.

Kazalika, Gwamnatin Jihar Kogi ta kai wadanda aka kubutar cibiyoyin lafiya domin kula da su, sannan daga baya za a mayar da su ga iyalansu.

Sanarwar ta bayyana cewa gwamnatin jihar na ci gaba da aiki da hukumomin tsaro domin dakile ayyukan ’yan bindiga a fadin jihar.

- Arewa Updates

Gobarar dai ta ɓarke ne daga ranar Asabar inda ta ci har zuwa Lahadi a wasu rukunin shaguna da ake yi wa laƙabi da Gidan...
16/02/2026

Gobarar dai ta ɓarke ne daga ranar Asabar inda ta ci har zuwa Lahadi a wasu rukunin shaguna da ake yi wa laƙabi da Gidan Gilas, inda aka yi asarar kayayyaki na miliyoyin naira.

Hotuna da bidiyo da aka yaɗa sun nuna yadda hayaƙi s**a turnuƙe saman kasuwar, yayin da shaguna s**a k**a da wuta tare da ƙonewar kayayyakin masarufi masu ɗumbin yawa.

Zaman lafiya mai ɗorewa na buƙatar haɗin kan kowa-Ministan Tsaro CG MusaBabban Ministan Tsaro, Janar Christopher Musa (m...
13/02/2026

Zaman lafiya mai ɗorewa na buƙatar haɗin kan kowa-Ministan Tsaro CG Musa

Babban Ministan Tsaro, Janar Christopher Musa (mai ritaya), ya bayyana cewa ana iya cimma zaman lafiya mai ɗorewa ne kawai idan aka haɗa ƙoƙarin tsaro da bunƙasa tattalin arziƙi, daidaiton zamantakewa, da ci gaban ɗan Adam.

Ya ce yaƙi da matsalar tsaro da ƙauracewar jama’a daga gidajensu ba aikin gwamnati kaɗai ba ne, ya na buƙatar haɗin gwiwar duka sassan gwamnati, al’umma da kuma kamfanoni masu zaman kansu.

Janar Musa ya bayyana hakan ne yayin wani taron kan ilimi da zaman lafiya da aka gudanar a birnin Legas.

A cewarsa, farfaɗo da rayuwar jama’a, gina al’ummomi, da ƙarfafa zaman lafiya a yankunan da rikici ya shafa dole ne su kasance tare da ayyukan tsaro. Ya kuma jaddada buƙatar ƙarfafa haɗin kai tsakanin gwamnati, kamfanoni masu zaman kansu, kungiyoyin ci gaba da na farar hula.

Ya ƙara da cewa Gwamnatin Tarayya ta ƙuduri aniyar magance waɗannan ƙalubale ta hanyar sabbin dabaru masu haɗa kai da ɗorewa, domin kare jama’a, tabbatar da tsaro, da gina ƙasa mai wadata ga kowa.

Address

Kano

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Ayzan Multimedia posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Shortcuts

Share