Hadisan Annabi S.A.W Da Tarihohi

Hadisan Annabi S.A.W Da Tarihohi Dokokinmu da tsare tsarenmu bama so reshin kunya da sauransu mungode

26/09/2023

Watarana Manzon ALLAH(S.A.W)
Yana Tafiya a Bayan Garin Madina,
Sai Ya Ji An Kira Shi:
Ya Manzon ALLAH(S.A.W)!
Ya Annabin ALLAH!!
Sai Manzon ALLAH(S.A.W) Ya
Duba Baya Bai Ga Kowa Ba Sai Ya
Kuma Jin Kiran Sai Yabi Inda Sautin
Yake Fitowa...........
Da Ya Isa Wajen Sai Ya Iske Wata
Barewa a Daure, a Gefe Kuma Ga
Wani Balaraben Kauye Yana Kwance
Yana Barci,
Sai Barewa Ta Ce Da Shi:“Ya
RASULULLAHI! Wannan Mutumin
Ya Farautoni Alhali Ni Ina Da 'Ya'ya
Guda Biyu a Wancan Kogon Dutse,
Ka Taimaka Min Ka Sake Ni Na Je
Na Shayar Da Su Nono Sannan Na
Dawo",
Sai ANNABI(S.A.W) Ya Ce:"Anya!
Kuwa Zaki Dawo???"
Sai Barewa Ta Ce"Idan Har Ban
Dawo Ba ALLAH Yayi Min Azabar
Da Zai Yiwa Mai Cin Rashawa"
Sai ANNABI(S.A.W) Ya Kwance Ta
Tafi.
Da Barewa Ta Cika Alkawari Ta
Dawo, Sai ANNABI(S.A.W) Ya
K**a 'Kafarta Yana Koƙarin Daureta
Da Igiya, Sai Balaraben Kauye Nan
Ya Farka Daga Bacci,
"Kai Ne Fansar Uwata Da Ubana Ya
Manzon ALLAH... Ni Ne Na Farauto
Ta Ko Kana Da Bukata...???". Inji
Wannan Balaraben Kauyen.
Sai ANNABI(S.A.W) Ya Ce:"Na'am!
Ina Da Bukata.."
Sai Balaraben Qauyen Nan Ya
Ce:"Na Baka Ita Ya
RASULULLAHI"
Sai ANNABI(S.A.W) Ya Saketa Ta
Koma Wajen Ya'yanta Tana Tafiya
Tana Cewa:"Na Shaida Babu Abin
Bautawa Da Gaskiya Sai ALLAH...
Na Kuma Shaida ANNABI
MUHAMMAD Manzon ALLAH Ne".
# DARASI :-
Jama'a Idan Muka Duba Da Idon
Basira Zamu Ga Abubuwan Da
Wannan 'Kissa Take Koyarwa Sune
K**ar Haka:-
*1. CIKA ALQAWARI
*2. TSANANIN TAUSAYIN UWA
AKAN 'YA'YANTA
*3. NEMAN HALAL TA HANYAR
FARAUTA
*4. DABBOBI KANSU NA TSORON
AZABAR MAI CIN RASHAWA.
YA ALLAH! KA QARA NARKAR
DAMU CIKIN SOYAYYAR
SAYYIDUL-WUJUDIA RANAR
GOBE QIYAMA YASA A TASHE A
QARQASHIN FADARSA(S.A.W)
ALBARKACIN WANDA YA CECI
WANNAN BAREWA{S.A.W}
AMEEEN.

Duk Wanda Yaji Dadin Wannan kissar Yataimaka Ya yaɗa wannan sakon

09/09/2023

Annabi Nuhu
Sa'ad Da madaukakin sarki Allah ya aiko annabi Nuhu duniya ba ga dukan kabila na duniya ya aiko shi ba. Ya aiko shi ne ga mutanen da ya fito a cikinsu. ALLAH ya h**e shi ya zo ya qira su ga bin Allah ya gaya musu abubawa marasa kyau, ya h**e su da bari, ya gaya musu masu kyau, ya h**e su da aikatawa, aka haife shi k**ar yadda ake haihuwar kowane d'a, ya girma, kana aka nufe shi da kawo saqo. ya zo ya yi qira a jama'arsa subi ALLAH su aikata abin da ya umarce su da aikatawa su guji abinda ya h**e su da gujewa. Amma ina, sai akad'an daga cikin mutanen nasa s**a bi maganarsa. ya yi ta qoqarin bayyana musu masifar da za ta fad'a musu in sun sa6i saqon Allah, da nasihar da za ta same su in sun bi. Amma ina? da yawa ba su kar6a qiran ba.
Da Annabi Nuhu ya yi, yay, ya ga dai abin ya faskara har Ubangiji Allah ya bayyana masa babu sauran wanda zai ba da gaskiya gare shi daga cikin mutanensa. sai ya roqi Ubangiji Allah da ya hori da jama'ar nan tasa da azaba Ubangiji ya kar6i roqonsa, zancigaba

09/09/2023

ANNABI MUSA
Annbi musa, amincin Allah ya tabbata a gare shi, yana cikin qabilar bani isra'ila ne. A masar aka haife shi, a zamanin wani fir'auna da ake qira Alwalidu ibn musab-ibnal-rayyar. haka aka ruwaito shi cikin littafin da ake qira Hazinu. sunan mahaifin Annabi musa imrana. A lokacin su bani isra'ila suna qarqashin daular wannan fir'aunu ne, sarkin masar. shi kuwa wannan fir'auna, ba abin da ya qi, k**ar wannan qabila ta yahudawa, bani isra'ila. ga su a qarqashinsa, amma k**ar suna qarqashin wuta. azaba kusan ba irin wadda ba shi gwada musu. hasali ma abin har ya kai ya da oda, in yahudawa sun haifi namiji, to sai yace a yanka shi. Wai don wani boka ya gaya masa cewa za a haifi wani jinjiri a cikinsu wanda zai 6ata masa mulkinsa. amma idan sun haifi mace wannan ita ba ya yanka ta.
Ana nan haka, sai wata mace, a cikin yahudawa watau matar imrana ta haifi d'a, aka sa masa suna Musa.shine kuma annabi musa da zamu baku labarinsa a yanzu. Da uwarsa ta haife shi, sai tsoro ya cika ta, ga shi ya fito namiji

09/09/2023

GA AMSOSHIN WADANNAN TAMBAYOYIN KAMAR HAKA
1. Akwai wasu Manyan Annabawa guda uku (3) wadanda Kansu bai ta'ba yin furfura ba.
(Sunayensu yazo acikin Suratu Maryam A.S ) Suwaye wadannan??
ANSWER:
Wadannan Annabawan sune
1) ANNABI HARUNA
2) ANNABI ISMA'I'll
3) ANNABI IDRIS
2. Akwai wasu Annabawa guda Uku (3)
wadanda basu taba yin Aure ba har s**a koma ga Allah (Su ma sunayensu yazo ajere acikin Suratul An-aam). Meye sunansu?
ANSWER:
Wadannan Annabawan sune:
1) ANNABI YAHAYA
2) ANNABI ISAH
3) ANNABI ILIYAS
3. Akwai wasu Annabawa guda biyu, (2)
Sarakuna ne kuma Manzanni ne. Daya daga cikinsu shiya haifi dayan. Meye sunansu?
ANSWER:
Wadannan Annabawan sune:
1) ANNABI DAUDA wanda shi ya haifi
2) ANNABI SULEIMAN
4. Akwai wasu Annabawa Mursalai guda (2) Wa da Qani ne. Shi Qanin an bashi Littafi da Mu'ujizozi. shi kuma yayan an bashi Fasahar harshe. Meye sunansu?
ANSWER:
Wadannan Annabawan sune:
1) ANNABI MUSA (shine karami ) Allah ya bashi littafi mai suna "ATTAURA" kuma ya bashi mu'ojuzoji misali sarrafa "SANDA" Sai kuma
2) ANNABI HARUNA (Shine yayan) Allah ya bashi FASAHAR HARSHE
5. Akwai wani Annabi Mursali (Ba Annabi Adamu bane) amma duk wanda ka gani abayan Qasa, to Jikansa ne. Wani Annabine?
ANSWER:
Wannan Annabi Shine:
Adamu na biyu wato ANNABI NUHU A.S
6. Annabi Ya'aqubu yana da wani suna wanda Allah ya ambaceshi dashi acikin Alqur'ani. Kuma har yanzu ana kiran Zuriyarsa da wannan Sunan.. Shin wanne suna ne wannan?
ANSWER:
An kira su da "ALI YAKUBU" a suratul Maryam, amma kuma an bashi sunan "ISRA'I'll" zuri'ar sa kuma BANU ISRA'ILA
7. Akwai wata halitta wacce Allah yai mata Wahayi. ita ba Mutum bace, ba Aljan bace, kuma ba Mala'ika bace. Shin wacce Halitta ce wannan?
ANSWER:
Wadannan Halittu sune:
1) TURURUWA da kuma
2) QUDAN ZUMA
Allhamdullahi Mungode
Allah yakara mana fahimtar Alqur,ani alfarman Wanda yazo dashi wato ANNABI S.A.W

Katura Zuwa Group 3 Kachal Domin Al'umma Su Amfana ❤️

09/09/2023

Wata rana Annabi Musa (A.S) ya roƙi Allah Ya nuna masa abokin zamansa a Aljanna. Sai Mala'ika Jibrilu (A.S) ya sauko gareshi ya sanar da shi cewa abokin zamansa a Aljanna wani mutum ne mahauci (mai sayar da nama), kuma ya gaya masa inda wannan mutum yake.
Sai Annabi Musa (A.S) ya tashi ya tafi neman wannan mutum don ya gana da shi.

Da zuwa ya tarar da shi yana ta sana'arsa ta fawa. Annabi Musa (A.S) bai yanke masa cinikinsa ba, ya koma waje guda ya jira shi har ya gama kasuwancinsa lokacin tashinsa yayi, sannan ya ƙarasa wajensa ya ce da shi yana so ya sauke shi a gidansa ya kwana zuwa gobe ya tafi. Mutumin ya karɓe shi cikin girmamawa Bayan ya ɗebi nama wanda buƙata a gida, sai s**a tafi tare da Annabi Musa (A.S) zuwa gida.

Da isarsu sai Annabi Musa A.S ya ga mutumin ya buɗe wani ɗaki ya ɗauko wani kwando wanda wata 'yar tsamurarriyar tsohuwa take a ciki, ya fito da ita ya zaunar da ita, ya ɗebo ruwa ya yi mata wanka ya tsaftace mata jikinta fes, sannan ya ɗauko hantar nan ya gasa ta gasu sosai, kasancewar ba ta da haƙoran da za ta iya taunawa, sai ya rinƙa tattauna shi da haƙoransa, in yayi taushi sai ya rinƙa ba ta a baki tana haɗiyewa, a haka har sai da ta ƙoshi, sannan ya ɗauke ta ya mayar da ita ɗaki. Kafin ya shigar da ita ɗakin sai Annabi Musa (A.S) ya ga tana motsa bakinta tana faɗin wata magana wadda bai iya gane abin da take cewa.

Bayan mutumin ya mayar da ita cikin ɗaki, sai kuma ya gabato masu da abinci s**a ci s**a sha s**a yi hani’an. Bayan sun ƙare, sai Annabi Musa (A.S) ya tambaye shi ko meye alaƙarsa da wannan tsohuwa?🤔

Sai mutumin ya ce, "Ita ɗin mahaifiyata ce. Saboda ba ni da wadatar da zan iya saya mata baiwar da za ta rinƙa kula da ita shi yasa nake kula da ita da kaina."

Sai Annabi Musa (A.S) ya tambaye shi ko me take faɗa ɗazu da ya ga tana motsa baki k**ar tana wata magana?

Sai mutumin yayi murmushi ya ce, "Ai kullum in na yi mata wanka na ba ta abinci sai ta dinga yi min addu'a tana cewa: “Allah Yayi maka albarka, Allah Ya gafarta maka, kuma Allah Ya haɗa ka zama da Annabi Musa a gidan Aljanna.” "

Ko da jin haka sai Annabi Musa (A.S) ya ce, "Af! Haka take faɗa? Ai kuwa to ka yi farin ciki, domin Allah Ya karɓi addu'arka. Ni ne MUSA, kuma Allah Ya sanar da ni cewa kai ne abokin zamana a Aljanna!"

MU KYAUTATA WA MAHAIFANMU, MU HIDIMTA MASU, ALLAH ZAI BA MU DUKKAN DACEWA A GIDAN DUNIYA DA LAHIRA.

Allah Ka raba mu da mahaifanmu lafiya, Ka ji ƙan waɗanda s**a riga mu, amin.

07/09/2023

Sheikh Hassan Antaki wani babban malami ne da ya rayu a ƙasar Korasan. Wata rana da daddare sai ya yi baƙi fiye da mutum talatin. Ga shi gidansa babu abinci sai wata 'yar ragowar gurasa wadda ko mutum biyu ba za ta ishe su ba. Kuma ga shi dare ya yi sosai babu inda zai sayo masu abinci.
Hakanan dai ya gutsuttsura gurasar nan ya zubo ta a wani ƙyalle ya kawo gaban baƙin ya ajiye, ya gayyace su zuwa cin wannan abinci. Yayin da za su fara cin abincin sai ya kashe fitilar dake ɗakin.
Sai ya ji motsin tauna ya cika ɗakin, alamar kowa ya fara cin abincin. Zuwa can sai ya ji shiru, alamar an kammala, don haka sai ya kunna fitila.
Ga mamakinsa, sai ya ga gurasar nan tana nan yadda take ko alamar taɓawa ba a a yi ba!

Ko kun san abinda ya faru?

Ashe kowannensu ya yi k**ar yana cin abincin ne amma ba ci yake ba, saboda kowanne yana ganin in ya ci abincin nan ɗan'uwansa ba zai samu ba saboda ƙarancin abincin!

ALLAHU AKBAR!

Ya Allah Ka ba mu ikon damuwa da damuwar 'yan'uwanmu, amin.

07/09/2023

An tambayi Sayyiduna Abdullahi dan Abbas (RA) cewa, yaya za ka iya sifanta mana zafin Mutuwa? Sai ya yi shiru, zuwa can sai ya ce, "Babbar Magana! Ai zafin mutuwa ba ya sifantuwa, amma dai zan iya kwatantawa cewa, tamkar a samu wani dogon abu mai kayoyi ne, a tura wannan abu cikin cikin mutum, sannan a janyo shi zuwa waje, ya fizgo abinda zai fizo. To k**ar haka radadin mutuwa yake."

Shi kuwa Annabi Idris (AS), lokacin da mala'ikan mutuwa ya dandana masa mutuwa ya ji yadda take, yayin da mala'ikan ya tambayeshi ko yaya zai iya sifanta yadda ya ji mutuwa, cewa ya yi, "K**ar yadda dabba za ta ji idan aka fedeta da ranta!" A hakan ma wai mala'ikan ya yi masa sassauci iya sassauci akan yadda yake daukar ran.

Annabimmu (SAW) kansa, lokacin da mutuwa ta zo masa, ya sa an kawo masa ruwa a tasa yana shafawa a fuskarsa yana cewa, "Innalillahi Wa-Innaa Ilayhi Raji'un, lallai mutuwa tana da magagi mai dimautarwa!"

Dan uwana, ka ji fa yadda bayanin mutuwa ya zo daga bakunan Annabawan Allah da Sahabbai, mafiya daraja daga cikin bayin Allah. To kai me ya mantar da kai da wannan babban aiki da ke fuskantarka? Me ka tanadar wa ranar mutuwarka?

Allah Ka shiryar damu, Ka ba mu ikon yin guzuri mai kyau, kuma kar Ka jarrabe mu da azabar mutuwa, saboda alfarmar Annabin Rahma ﷺ, Amin.

07/09/2023

QISSA MAI KARYA ZUCIYA 😥

Wani balaraben ƙauye yana tafiya a cikin wasu tsaunuka sai ya ga wata bukka ita kaɗai a cikin daji, ya je ya leƙa don ya ga ko waye ke rayuwa a ciki, sai ya tarar babu kowa ciki sai wani ɗan tsamurmurin motsattsen tsoho mai k**a da matsattsen lemun tsami kwance a bisa wata shimfiɗa.
Tsohon nan ya kasance makaho, kuma yana cikin halin rashin lafiya ƙwarai, yana jin jiki sosai, kusan babu wata gaɓa a jikinsa wadda ba ta tawaya ba, sannan ga dukkan alamu kuma ɓarin jikinsa guda ya mutu (paralysed), kusan dai a iya cewa lokacin ajalinsa ne kawai yake jira, amma ga mamakin balaraben ƙauyen nan sai ya ji yana cewa, "Godiya ta tabbata ga Allah wanda Ya ba ni kariya daga cututtuka masu yawa waɗanda Ya jarrabi halittunsa, kuma Ya fifita ni akan da yawa daga bayinSa, fifitawa!"
Ko da jin haka sai balaraben ƙauyen nan ya cika da mamaki, har ya kasa haƙuri ya dubi tsohon ya ce, "Haba ya kai wannan tsoho, ai ni gani nake k**ar babu wata cuta wadda aka tserar da kai daga gareta. Ina tsammanin cewa kana tare da duk wata cuta da ke a wannan duniya!"
Sai tsohon yayi murmushi ya ɗaga kansa sama k**ar yana kallon balaraben ƙauyen ya ce da shi, "Tafi ka ba ni waje! Shin ashe ban mallaki lafiyayyen harshe ba wanda nake ambaton Allah da shi kuma ina tunawa da Shi a kowane lokaci? Kuma ashe ban mallaki lafiyayyar zuciya ba wadda take mai yin imani da Shi?"

Jin waɗannan kalamai daga bakin wannan yamusasshen tsoho ya sa jikin balaraben ƙauyen ya yi sanyi, domin waɗannan zantuka sun isa su sanya shi ya tuba zuwa ga Allah daga zunubansa kuma Ya nemi gafararSa.

: KODAYAUSHE KA RINƘA TUNAWA CEWA AKWAI WANDA YA FI KA MATSALA A RAYUWA, KUMA KA RINƘA DUBAN NI'IMOMIN DA ALLAH YA YI MAKA, SAI KA GODE MASA.

GARKUWOYI GUDA HUƊU (4)Sayyidina Abu Huraira (R.A) ya ce: “Wata rana Annabi (S.A.W) ya ce da mu, "Ku sanya wa kawukanku ...
07/09/2023

GARKUWOYI GUDA HUƊU (4)

Sayyidina Abu Huraira (R.A) ya ce: “Wata rana Annabi (S.A.W) ya ce da mu, "Ku sanya wa kawukanku garkuwoyi!"
Sai muka ce, "Ya Rasulullahi, shin wasu maƙiya suna fuskanto mu ne?"
Sai ya ce, "Ku sanya wa kawukanku garkuwoyi daga azabar Wuta! Ku ce:
(( سبحان الله ))
"TSARKI YA TABBATA GA ALLAH!"
(( الحمد لله ))
"GODIYA TA TABBATA GA ALLAH"
(( لا إله إلا الله ))
"BABU ABIN BAUTAWA SAI ALLAH"
(( الله أكبر ))
"ALLAH SHI NE MAFI GIRMA!"

To, waɗannan kalmomi guda huɗu za su zo a matsayin garkuwoyi ranar alƙiyama, za su kange wanda ya karanta su ta gaba da baya, dama da hauni (kariya ta kowane ɓangare!)" ”

–ŤABARANI YA RUWAITO.

👉KA TABBATAR KA YAƊA WANNAN SAƘON DOMIN SAMUN LADAN DUK WANDA YA KARANTA KUMA YA AIKATA!

07/09/2023

BUTULCIN ƊAN ADAM...

Wata rana Annabi (S.A.W) ya ƙissanta wa Sahabbansa (R.A) wannan ƙissar:
"An yi wasu mutane uku a Banu Isra'il, guda ya kasance kuturu, guda kuma mai saiƙon kai (marar gashi), guda kuma makaho. Sai Allah (S.W.T) Ya yi nufin Ya jarrabe su, sai Ya aiko wani mala'ika zuwa ga kowannensu.
Sai mala'ikan ya fara zuwa wajen kuturun ya ce da shi, "Me ka fi so?"
Kuturu ya ce, "Ina so fatar jikina ta zama kyakkyawa, kuma wannan cutar kuturtar ta rabu da ni, mutane su daina gudu na kuma su daina ƙyamar zama da ni!"
Sai mala'ikan ya sanya hannunsa a jikin kuturun ya shafi jikinsa. Nan take sai ya warke, fatarsa ta zama mai kyau mai sheƙi.
Daga nan sai mala'ikan ya ce da shi, "Wacce irin dukiya ka ke so?"
Sai ya ce, "Raƙumma!"
Sai mala'ikan ya kawo masa wata taguwa mai ciki ya ba shi, ya ce da shi, "Ga ta nan, Allah Ya sanya maka albarka a cikinta!".
Daga nan sai mala'ikan ya je wajen mai saiƙon kai, ya ce da shi, "Me ka fi so?"
Mai saiƙo ya ce, "Ina so gashin kaina ya fito, domin mutane su daina yi min dariya suna min ba'a duk inda na nufa!"
Sai Mala'ikan ya shafi kansa, sai kyakkyawar suma ta fito masa, gwanin ban sha'awa.
Sai mala'ikan ya ce da shi, "Wacce irin dukiya ka ke so?"
Sai ya ce, "Shanu!"
Sai mala'ikan ya ba shi wata saniya mai ciki ya ce da shi, "Ga ta nan, Allah Ya sanya maka albarka a cikinta!".
Sai mala'ikan ya je wajen makaho, ya ce da shi, "Me ka fi so?"
Makaho ya ce, "Idanuwana su dawo don in rinƙa ganin komai!"
Sai Mala'ikan ya shafi idanuwansa, sai ganinsa ya dawo k**ar bai taɓa yin makanta ba. Sai mala'ikan ya ce da shi, "Wacce irin dukiya ka ke so?"
Sai ya ce, "Awaki!"
Sai mala'ikan ya kawo akuya mai ciki ya ba shi, ya ce da shi, "Ga ta nan, Allah Ya sanya maka albarka a cikinta!", sai ya tafi.
Ai kuwa sai Allah Ya albarkaci dabbobin nan nasu, kafin wani lokaci duk yankin ya cika da raƙuma da shanu da awaki na waɗannan mutane uku.
Bayan haka wata rana sai Mala'ikan nan ya zo a cikin sifar wani mutum mabuƙaci. Sai ya tafi wajen kuturun nan wanda a baya ya warkar da shi da izinin Allah, ya ce da shi, "Ya kai wannan attajiri, ka sani cewa ni dai talaka ne matafiyi, dukkan guzurina ya ƙare a hanya kuma dabbar hawana ta mutu. Yanzu ba ni da komai kuma ba ni da wata mafita sai Allah sai kai. Ka dubi girman Allah wanda Ya ba ka wannan kyakkyawar halitta da wannan tarin dukiyar, Ka ba ni raƙumi ɗaya wanda zan hau in ƙarasa garinmu!"
Jin haka sai mutumin nan ya ɗaure fuska, ya dube shi ya ce, "Tafi ka ba ni wuri! Ni nan ina da muhimman abubuwan da zan yi da wannan dukiyar, ba ni da wani abu da zan iya cirewa in ba ka daga ciki!"
Sai mala'ikan (a sifar mabuƙaci) ya ce, "K**ar ko na gane ka! Shin ba kai bane wannan wanda a baya ka kasance kuturu daga baya Allah Ya warkar da kai? Ba kai bane ka kasance matsiyaci wanda kowa yake gudunka, daga baya Allah Ya azurta ka?"
Mutumin nan ya ce, "Me kake cewa? Lallai ba ka da hankali. Ni wannan dukiyar duk da ka gani na gaje ta ne a wajen iyayena!"
Sai mala'ikan ya ce, "To, in ƙarya kake, Allah Ya mayar da kai yadda ka ke da farko!"
Sai ya tafi wajen wannan mutumin mai saiƙon kai, shi ma ya nemi taimako daga wajensa, shi ma k**ar yadda s**a yi da na farkon nan haka ta kasance, ya hana shi. Sai shi ma ya ce da shi, "Allah Ya mayar da kai irin yadda ka kasance a baya!"
A ƙarshe sai ya tafi wajen makahon nan. Ya ce da shi, Ya kai wannan attajiri, ka sani cewa ni dai talaka ne matafiyi, dukkan guzurina ya ƙare a hanya kuma dabbar hawana ta mutu. Yanzu ba ni da komai kuma ba ni da wata mafita sai Allah sai kai. Ka dubi girman Allah wanda Ya warkar da kai daga makanta, Ka ba ni akuya ɗaya wadda zan sayar in samu guzurin da zai ishe ni zuwa garinmu!"
Jin haka sai mutumin nan ya ce, "Babu shakka, ni a baya na kasance makaho, sai Allah cikin RahamarSa da kyautarSa Ya dawo min da ganina. Kuma na kasance matalauci, sai Ya azurta ni daga falalarSa. Yanzu ga shi bawanSa ya zo wajena da buƙata, ba zai yiwu a gareni in hana bawanSa abin da yake buƙata ba matuƙar na mallaki wannan abu! Ya kai wannan bawan Allah, ga dukiyata nan, ka ɗebi iya abin da ka ke so ka bar abin da ba ka so, ina rantsuwa da Allah ba zan taɓa dakatar da kai ba!"
Sai mala'ikan Ya ce, "Ka bar dukiyarka, ni ne mala'ikan nan wanda ya zo maka a baya, na zo ne don in jarraba ka, yanzu kam ka cinye jarrabawar!"
Daga nan sai Allah Ya bar wannan mutum da dabbobinsa, su kuma waɗancan biyun sai Allah Ya karɓe dukiyarSa, kuma Ya mayar da su k**ar yadda suke a baya."

07/09/2023

YARDAR ALLAH TANA CIKIN YARDAR MAHAIFIYA...

A zamanin Annabi (S.A.W) an yi wani “sahabi” mai suna Alƙamatu, ya kasance mutum ne mai yawan ibada: salloli da azumi da zakka da yawan sadaƙa. Wata rana sai ciwon ajali ya k**a shi, ya kwanta jinya a gida.
Ranar da zai mutu ciwonsa ya yi tsanani, sai matarsa ta zo ta gaya wa Annabi (S.A.W) cewa ga mijinta Alƙamatu can jikinsa ya tsananta, yana a gaɓar mutuwa. Jin haka, sai Manzon Allah (S.A.W) ya tashi Sayyadina Ammar – a wata faɗar kuma an ce Bilal ne da Suhaib, Allah Ya ƙara yarda a garesu – ya ce su je su biya wa Alƙamatu Kalmar Shahada don ya maimaita kafin ya cika.
S**a tafi wajensa s**a dinga biya masa suna umurtarsa da ya maimaita, amma harshensa ya kasa ko motsawa b***e ya maimaita. Sai s**a garzayo s**a gaya wa Annabi (S.A.W) cewa sun yi sun yi da shi amma ya ƙi maimaitawa.
Sai Annabi (S.A.W) ya ce, "Shin akwai wani daga mahaifansa da yake a raye?"
Aka gaya masa cewa tabbas mahaifiyarsa tana nan da ranta, amma sai dai ta tsufa ƙwarai.
Sai Annabi (S.A.W) ya ce, "A je a faɗa mata cewa in tana iya zuwa ta zo ina kiran ta. In kuma ba ta iya zuwa to ni zan zo in same ta, ina son magana da ita."
Aka je aka faɗa wa mahaifiyar Alƙamatu saƙon Manzon Allah (S.A.W). Ko da jin wannan saƙo, sai ta ce, "Raina fansa a gareshi, ai ba abinda zai hana ni amsa kiransa matuƙar ina numfashi!"
Sai ta ɗauki sanda tana doddogarawa ta tafi wajen Annabi (S.A.W). Da zuwanta sai Annabi (S.A.W) ya ce da ita, "Ya Ummu Alƙamah, ki faɗa min gaskiya, kuma ki sani in kika ɓoye min, to Allah Zai saukar min da wahayin gaskiyar abin da kika ɓoye! Me kika sani game ɗanki Alƙamatu?"
Sai ta ce, "Ya Ma'aikin Allah, yana yawaita sallah da azumi, da yawan ba da sadaka!"
Sai Annabi (S.A.W) ya ce, "A game da ke fa?"
Ta ce, "Ni kam ina fushi da shi."
Ya ce, "Saboda me?"
Ta ce, "Ya Ma'aikin Allah, haƙiƙa shi ya fifita matarsa a kaina, kuma ba yai min biyayya!"
Sai Annabi (S.A.W) ya ce, "Ya Ummu Alƙamah, ki sani cewa fushinki ga ɗanki ya hana harshensa ya iya furta kalmar tsira. Shin za ki gafarta masa ne ko kuwa kina so ya mutu ya shiga Wuta?"
Sai ta yi shiru ba tare da ta ce komai ba. Sai Annabi (S.A.W) ya sa aka tara itatuwa ya kunna gagarumar wuta, ya ce a je a ɗauko Alƙamatu a zo da shi.
Sai ta ce, "Ya Ma'aikin Allah, me kake nufin aikatawa ne?"
Ya ce, "Zan ƙone shi ne a gaban idonki!"
Ta ce, "Ya Ma'aikin Allah, shi ɗana ne fa! Ba zan iya jure ganinka kana ƙona shi a gabana ba!"
Sai Ya ce, "Ya Ummu Alƙamah, ki sani cewa azabar wannan wutar mai sauƙi ce. Azabar Lahira ita ce mafi tsanani, kuma ita ce madawwamiya! Saboda haka, in har kina so Allah Ya gafarta masa, to ki yafe masa. Na rantse da wanda rayuwata take a hannunSa, sallar Alƙamatu da azuminsa da sadaƙarsa da ya aiwatar duka ba za su amfana masa komai ba matuƙar kina fushi da shi!"
Jin haka sai tsohuwar ta nisa ta ce, "Ya Ma'aikin Allah, ina shaidantar da Allah Maɗaukaki da dukkan mala'ikunSa, kuma ina sanya ka a matsayin Shaida, da dukkan jama'ar musulmai da ke wajen nan, cewa ina farin ciki da ɗana Alƙamatu (na yafe masa)!"
Jin haka, sai Annabi (S.A.W) ya ce wa Sayyadina Bilal (R.A), "Je ka yanzu ka sake biya wa Alƙamatu kalmar Shahada ka gani idan zai iya furtawa ko akasin haka, mai yiwuwa mahaifiyarsa ta faɗi wannan ne don ganin idona ba da gaske daga cikin zuciyarta ba!"
Sai Bilal (R.A) ya tafi, tun daga bakin ƙofa ya ji Alƙamatu yana ta faɗi yana maimaitawa:
"LÃ ILÃHA ILLAL-LÃH"
"LÃ ILÃHA ILLAL-LÃH"
"LÃ ILÃHA ILLAL-LÃH"
Ko da ganin haka, sai Bilal (R.A) ya ce, "Tabbas, lokacin da mahaifiyar Alƙamatu take fushi da shi, an ɗaure harshensa ne an hana shi furta kalmar tsira. Amma yanzu da ta yarda da shi, an kwance masa!"
A ranar nan Alƙamatu (R.A) ya yi wafati. Annabi (S.A.W) ya zo ya sa aka yi masa wanka aka yi masa sutura, ya yi masa sallah aka bizne shi. Sai Annabi (S.A.W) ya tsaya a gefen ƙabarinsa ya yi wa'azi ga mutane yana cewa, "Ya ku taron masu hijira da mataimaka! Ku san cewa, duk wanda ya fifita matarsa akan mahaifiyarsa, Allah da mala'ikunSa da dukkan mutane suna tsine masa! Allah ba Ya karɓar ibadarsa ko sadaƙarsa har sai ya tuba zuwa ga Allah, kuma Ya nemi gafarar mahaifiyarsa da yardarta. Domin kuwa, yardar Allah tana cikin yardarta, kuma fushin Allah yana cikin fushinta...!"

— DABARANIY DA AHMAD S**A RUWAITO.

07/09/2023

Sayyidina Abdullahi Ibn Abbas (R.A) ya ce, "Bayan wafatin Annabi (S.A.W) na ce da wani abokina mutumin Madina:
"Yanzu Annabi (S.A.W) ba ya tare da mu, amma ga Sahabbansa nan da yawa a tare da mu, zo mu rinka zuwa wajensu muna koyon al'amuran addini!”.
Sai ya ce da ni, "Kai kam wa zai zo wajenka don ɗaukar wata fatawar addini alhali ga waɗannan tarin Sahabban (abokan Annabi)?"
Duk da haka dai ban karaya ba, sai na zage damtse wajen neman ilimi, ina zuwa wajen duk wani mutumin da na san ya zauna da Annabi (S.A.W) ya ji wani abu daga wajensa don ya sanar da ni.
Na kasance idan na je wajen wani Sahabi na tarar da shi yana barci, sai in shimfiɗa dardumata a ƙofar gidansa in zauna in jira komai daɗewa har sai ya farka. Wani lokacin ƙura takan baɗe min dukan fuskata da jikina, amma zan jira har sai sun fito na gana da su. Wasunsu s**an ce da ni, "Ya Abdullah, kai fa ɗan'uwan Ma'aiki ne, me ya sa ba ka aiko mana ba sai ka zo da kanka?"
Ni kuma sai na ce, "Dole ne in zo da kaina wajenku, domin ni ɗalibinku ne, ku kuma malamaina ne!"
Wasu kuma waɗanda nake zama in jira su s**an ce, "Tun yaushe kake zaman jiranmu?"
Sai in ce, "Na ɗan jima!"
Sai su ce, "Allah Sarki! Amma me ya sa ba ka tayar da mu ba?"
Sai na ce, "Ba na so in takura maku ne saboda wata buƙatar ƙashin kaina!"
Haka dai na cigaba da wannan aikin neman ilimomi har sai da ta kai mutane sun fara kewaye ni suna ɗaukar karatu!
Lokacin da wannan abokin nawa ya ga haka sai ya ce, "Lallai wannan yaron ya tabbatar mana cewa ya fi mu hankali!"

Source: "Akhbaar as-Sahaabah", Sheikh Muhammad Zakariyya.

Address

New Bussa

Telephone

+2347039941442

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Hadisan Annabi S.A.W Da Tarihohi posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The School

Send a message to Hadisan Annabi S.A.W Da Tarihohi:

Shortcuts

Share