SHARHI AKAN WAKAR “NI DAI
BARHAMA NAKE BAUTAWA, DAN SHI
YA HALICCENI”
Daga Muhammad Rabiu Umar
Dalilin Yin Wakar “Ni Dai Barhama
Nake Bautawa, Don Shi Ya Halicce Ni”
A yan kwanakin nan wata waka da
wani mawaki ya yi mai take “Ni dai
Barhama nake bautawa, don shi ya
halicce ni” ta jawo cece-kuce a tsakanin
mutane, kuma da yawa daga cikin
mutane sun yi mamakin a ce wai
musulmi ne ya yi wannan wakar,
wanda daga baya-bayan nan
gwamnatin Kano ta hanyar hukumar
tace finafinan ta bada sammacin a kamo
wannan mawaki.
Amma alal-hakika duk wanda ya san
irin akidar da take cikin manya-manyan
littattafan darikun sufaye – musamman
yan tijjaniyya – to ba zai yi mamakin jin
irin wannan waka ta fito daga irin masu
wannan darika.
Idan muka dauki babban littafin darikar
tijjaniyya mai suna “Jawahirul Ma’ani”
zamu ga cike yake da akidar “Komai
Allah ne” ma’ana duk wani abu da yake
duniyar nan Allah ne, kuma in an bauta
masa babu laifi, Allah aka bautawa, ga
kadan daga cikin abin da ya zo akan
haka : Shehu Tijjani ya ce :
“ ﻓﻤﺎ ﻓﻲ ﺫﻭﺍﺕ ﺍﻟﻮﺟﻮﺩ ﻛﻠﻪ ﺇﻻ ﺍﻟﻠﻪ ﺳﺒﺤﺎﻧﻪ
ﻭﺗﻌﺎﻟﻰ ﺗﺠﻠﻰ ﺑﺼﻮﺭﻫﺎ ﻭﺃﺳﻤﺎﺋﻬﺎ، ﻭﻣﺎ ﺛﻢّ ﺇﻻ
ﺃﺳﻤﺎﺅﻩ ﻭﺻﻔﺎﺗﻪ” ( ﺟﻮﺍﻫﺮ ﺍﻟﻤﻌﺎﻧﻲ : 1/259 ).
Ma’ana “Babu abin da yake cikin zatin
dukkan samammu gaba dayansu sai
Allah Subhanahu Wa Ta’ala, shi ne ya
bayyana a surarsu da sunayensu. Babu
wani abu sai sunayensa da
siffofinsa” (Jawahirul Ma’ani 1/259).
Wannan magana tana nuna cewa duk
wani abin da yake samamme a wannan
duniya to ba komai ba ne face Allah ne,
saboda Allah ne ya bayyana a cikin
dukkan komai da sunayensa da
siffofinsa.
A wani wurin ya ce :
“ ﺇﻥ ﺟﻤﻴﻊ ﺍﻟﻤﺨﻠﻮﻗﺎﺕ ﻣﺮﺍﺗﺐ ﻟﻠﺤﻖ…ﻓﺈﻥ ﺍﻟﻮﺟﻮﺩ
ﻋﻴﻦ ﻭﺍﺣﺪﺓ ﻻ ﺗﺠﺰﺅ ﻓﻴﻬﺎ ﻋﻠﻰ ﻛﺜﺮﺓ ﺃﺟﻨﺎﺳﻬﺎ
ﻭﺃﻧﻮﺍﻋﻬﺎ ﻭﻭﺣﺪﺗﻬﺎ” ( ﺟﻮﺍﻫﺮ ﺍﻟﻤﻌﺎﻧﻲ : 2/92 ).
Ma’ana : “Dukkan ababen halitta wasu
yanki ne na Allah….saboda da dukkan
samamme abu daya ne, babu wani
yanki-yanki a cikinsa, duk da jinsinsa
mai yawa da nau’o’insa da
hadewarsa” (Aljawahir 2/92).
Wannan bayani yana nuna cewa duk
wata halitta Allah ce ita, kuma komai da
muke gani abu daya ne, wanda shi ne
Allah!.
Ya sake cewa :
“ ﻓﻜﻞ ﻋﺎﺑﺪ ﺃﻭ ﺳﺎﺟﺪ ﻟﻐﻴﺮ ﺍﻟﻠﻪ ﻓﻲ ﺍﻟﻈﺎﻫﺮ ﻓﻤﺎ
ﻋﺒﺪ ﻭﻻ ﺳﺠﺪ ﺇﻻ ﻟﻠﻪ ﺗﻌﺎﻟﻰ، ﻷﻧﻪ ﻫﻮ ﺍﻟﻤﺘﺠﻠﻲ ﻓﻲ
ﺗﻠﻚ ﺍﻷﻟﺒﺎﺱ، ﻭﺗﻠﻚ ﺍﻟﻤﻌﺒﻮﺩﺍﺕ ﻛﻠﻬﺎ ﺗﺴﺠﺪ ﻟﻠﻪ
ﺗﻌﺎﻟﻰ … ﻭﻗﻮﻟﻪ “ ﻻ ﺇﻟﻪ ﺇﻻ ﺃﻧﺎ” ﻳﻌﻨﻲ ﻻ ﻣﻌﺒﻮﺩ
ﻏﻴﺮﻱ ﻭﺇﻥ ﻋﺒﺪ ﺍﻷﻭﺛﺎﻥ ﻣﻦ ﻋﺒﺪﻫﺎ ﻓﻤﺎ ﻋﺒﺪ
ﻏﻴﺮﻱ” ( ﺟﻮﺍﻫﺮ ﺍﻟﻤﻌﺎﻧﻲ : 1/184 )
“Duk wani mai bauta ko mai sujjada ga
wanin Allah a zahiri, ba wanda ya
bautawa ko ya yi wa sujjada sai Allah
Ta’ala, saboda shi ne yake bayyana a
cikin wadannan abubuwa, kuma duk
wadannan abubuwa da ake bautawa
suna sujjada ne ga Allah (S.W.T)
….sannan fadin Allah “Babu abin
bautawa sai ni” yana nufin babu wani
abin bautawa, wanda ba ni ba, ko da
kuwa masu bautar gumaka sun bauta
masu, ba su bautawa wani
ba” (Jawahirul Ma’ani 1/184).
Wannan kadan kenan daga cikin
mummunar akidar dake cikin wannan
babban littafin na darikar tijjaniyya. To
yanzu dan uwa mai karatu wanda ya
karanta wadannan maganganu, kuma
ya yi imani da su, ya yarda da cewa
wanda ya yi su, waliyyi ne daga cikin
waliyyan Allah, kuma duk abin da yake
fada Annabi ne (S.A.W) yake fada masa,
a farke a cikin barci, to yaya ba zai ce
“Barhama Yake Bautawa ba”!.
Wata kila mai karatu ya ce, to ba
Barhama ba ne ya koyar da haka, don
haka me ya sa shi mai wakar bai ce “Shi
Tijjani yake bautawa ba” sai ya ce
Barhama.
Dalili, shi kansa Barhama din wato
shehu Ibrahim Inyass haka shi ma ya
koyar ya kuma kira muridansa da
mabiyansa a kan haka, a cikin
littattafansa, ga kadan daga cikin abin
da ya fada a kan haka :
Yana cewa :
ﻓﺈﻥّ ﺍﻟﺸّﻴﺦَ ﻣﻈـﻬﺮُ ﺫﺍﺕ ﺭﺑِّﻲ ﻭﻋﻴﻦُ ﺍﻟﻌَﻴﻦ ﻋﻴﻦُ
ﺃﺑﻲ ﺍﻟﻌﺒﺎﺱ . )) ﺩﻳﻮﺍﻥ ﺗﺤﻔﺔ ﺃﻃﺎﻳﺐ ﺍﻷﻧﻔﺎﺱ ((
(ﺹ 86 ).
Ma’ana : Lallai hakika shehu shi ne
Mazharin zatin Ubangijina. Kuma
Hakikanin zati, shi ne zatin Abul Abbasi
(wato shehu Tijjani).
Anan zamu ga Inyass yana cewa shehu
Tijjani shi ne Allah, kuma duk wani zati
na wani abu, ba komai ba ne face zatin
shehu Tijjani, don haka komai shehu
Tijjani ne, shi kuma Allah ne!!.
A wani wuri cewa ya yi :
ﺧﻠﻴﻔﺔُ ﺍﻟﻠﻪ ﻓﻲ ﺃﺭﺽٍ ﻟﺬﻟﻚ ﻣَﻦ ﺭﺁﻛﻢُ ﻗﺪ ﺭَﺃﻯ ﺭﺏَّ
ﺍﻟﺒﺮﻳَّﺎﺕ
Ma’ana : “Khalifan Allah a bayan kasa,
don haka duk wanda ya ganku, to lallai
ya ga ubangijin halitta”. (Duba littafinsa
Diwanu Tuhafatil Adayibil Anfas).
Subhanallahi, don ka ji mai karatu duk
wanda ya ga shehu Tijjani to ya ga
Allah, Ma’ana da Allah da Shehu Tijjani
duk abu daya ne!!!.
Wannan kadan kenan daga cikin akidun
da suke cikin littattafan wadannan
sufaye, kuma a kansu ne suke kokarin
renon mabiyansu, wanda har akwai
wata tarbiyya da ake wa muridi, wadda
bayan ya yi ta, sai zama Allah, kuma
komai ya zama Allah a wurinsa, Sheikh
Dahiru Mai gari (Allah Ya Yi masa
Rahama) ya yi rubuta akan wannan
tarbiyya da darika, ya tabbatar da
wadannan abubuwa.
Don yan uwa in ana so a magance ci
gaba da faruwar irin wadannan wakoki
to dole ne sai an wancakalar da
wadancan littattafai, kuma an dawo kan
koyarwar Alkur’ani da Hadisi a bisa
fahimtar magabata na Kwarai. Allah ya
tsare mana Imaninmu Ameen.
Community Awareness and Youth Empowerment
Dan karantar da sunnan manzon allah s.a.w,da kawadda bidi'a ,mu yan izala muna kafa hujja neda QUR'ANI DA HADISI da maganganun manya manyan malamai
بسم الله الرحمن الرحيم
عمدةالأحكام من كلام خيرالأنام صلى الله عليه وسلم
DAGA ZAUREN
KITABU WAS SUNNAH
Cigaba da karatu acikin littafin UMDATUL AHKAM
Hadisi nabiyu
وعن أبي هريرة رضي الله عنه قال :قال رسول الله صل الله عليه وسلم لا يقبل الله صلاة أحدكم اذا أحدث حتى يتوضأ
اخرجه البخاري ،٦٩٥٤
و مسلم ف الطهار
والترمذي٧٦
وابوداود والطبراني
2 Hadisi daga Aby huraira sunashi ABDULRAHMAN IBN SAQAR AD DAUSY
yace manzon Allah SAW yace. Allah baya karban Sallar dayanku idan yayi hadasi harse yayi alwala
Bukhari da Muslim da turmizy da abu dawuda da dabarany sun ruwaito wannan hadisin cikin littafansu
Abunda hadisin yake karantar damu shine duk mutuminda yayi alwala toh kafin yayi sallah sekuma yayi tusa misali toh idan yazo zeyi sallah wajibine seyasake yin alwala inkuma besakeba toh bashida sallah
Lallai yan,uwa tsarki yanada babban matsayi acikin addini don haka wajibine murika kulawa sosai da al,amarin tsarki
Allah yasa mudace
SUBHANAKALLAHUMMA WABI HAMDIK ASHHADU ANLA,ILAHA ILLA ANTA ASTAGFITUKA WA,ATUBU ILAIKA
Wassalamu,alaikum
ASSALAMU ALAIKUM
Islam around the world
Republican front-runner Donald Trump called for "banning Muslims from the United States "
in Tuesday night’s presidential debate, but his plan was brushed aside as unserious by his rivals as they outlined their own approaches for preventing attacks in the United States.
“Donald is great at the one-liners, but he’s a chaos candidate and he’d be a chaos president,” former Florida Governor Jeb Bush said as the fifth Republican presidential debate opened in Las Vegas.
Florida Senator Marco Rubio said of Mr. Trump’s proposal, “It isn’t going to happen.”
Mr. Trump insisted he wasn’t seeking to discriminate against Muslims.
“We are not talking about isolation, we’re talking about security,” he said. “We are not talking about religion, we are talking about security.”
Tuesday’s debate was the first for Republicans since the attacks in Paris and San Bernardino, California, that increased concerns about terrorism in the United States. Hours before the debate was to begin, officials in Los Angeles closed all schools after an email threat that was later deemed a hoax. ( probably engineered by Donald tump and his likes to show to the United States that terrorism is around the corner so theat their anti Muslim suggestions would be used to accelerate their political campaign )
It is not too long ago that a republican presidential aspirant en Carson delivered his verbal attacks to the Muslims saying "I would not advocate we put a Muslim in charge of this nation, I absolutely would not agree with that"
But won't they be ashamed about how their words clearly proves that they are so ignorant to even know the us constitution but they dear to aspire for presidency
Article 4 of the us constitution states : no religious test shall ever be required as a qualification to any office or publi trust under the United States "
It also says " congress shall make no law respecting the establishment of religion or prohibiting the free exercise thereof"
Isn't this worh disqualification for arson and Donald??
What have other candidates said about Ben Carson's anti Muslim comments ??
Marco Rubio - " I personally do not believe that your religious denomination should disqualify you from serving office, that's why voters decide on a variety of issues including the values of someone"
Jen bush - " article 4 of the us constitution is clear, it prohibits religious tests for presidency"
Lindsey graham - " Carson is not ready to be the commander in chief, America is an idea not owned by a particular religion, Carson needs to appologize to American Muslims, he is a good doctor but clearly not prepared to lead a great nation"
Ted Cruz - " you know the constitution specifies there shall be no religious test, I am a constitutionalist "
Bobby jindal - "if you can find me a Muslim candidate who is a republican, who will fight hard to protect religious liberty, who will respect the jeudo Christian heritage of America I will be happy to consider voting him or her "
HILLARY CLINTON- " can a Muslim be president of the United States of America ? In a word: yes now let's move on"
Allah (s.w.t) said " سنريهم ءاياتنا في الآفاق وفي أنفسهم حتي يتبين لهم انه الحق"
"Soon will We show them our Signs in the (furthest) regions (of the earth), and in their own souls, until it becomes manifest to them that this is the Truth. Is it not enough that thy Lord doth witness all things?"
UMAR ALIYU ABUBAKAR (ALBANI)
ASSALAMU ALAIKUM WA RAHMATULLAH
MARKAZUSSALAFIYYAH - aqidun musulunci tabbatattu daga alqur'ani da sunnah (1)
Wajibi ne mu kadaita Allah Muna masu Neman da cewa Akan hakan, Allah shi kadai ne bashida abokin tarayya, babu komai k**arsa, kuma baya gazawa Akan komai, daddadde ne ba da farau ba, kuma ze dawwama bashi da karshe, kuma babu abunda yake awkuwa se abunda ya ga dama, baya k**a da halitta, kuma rayayye ne baya mutuwa, yayi halitta ba dan Yana da bukata ba, Yana bayarwa kuma baya Nema, Yana kashewa ba tare da tsoro ba kuma ze tayar ba tare da ya ji wahala ba, dama can Yana da suffofinsa tun kafin yayi halitta, kasancewar halittu be canja musu komai ba, kuma k**ar Yadda suke tun tuni bazasu taba canja wa ba har abada, ba wai bayan yayi halitta bane ya Zama mahalicci, shi ake bautawa kuma baya Bauta wa kowa, shi yake halitta ba a halicceshi ba, k**ar Yadda shi me rayawa ne tun kafin ya raya matattu, mahalicci ne shi tun kafin ya halicci halittu, Allah Yana da iko Akan komai, kuma kowa talaka ne a wajenshi, komai a wajenshi me sauqi ne kuma baya bukatar komai, babu komai k**arsa kuma shi me ji ne me gani ne, ya halicci halittu kuma ya halicci ayyukansu, kuma ya tsara musu kaddararsu sannan ya Sanya musu ajali, Allah ya San komai daga ayyuka da dabi'un yan Adam tun kafin ya haliccesu, sannan ya umarcesu da yi masa da'a ya hanasu aikata sabo, komai Yana gudana Akan kaddararsa da ganin damansa, komai se Allah ya so yake faruwa, Yana shiryarda Wanda yaso, ya kiyaye Wanda ya so, ya batar da Wanda ya so, ya jarrabi Wanda yaso, komai Yana yawo a cikin falalarsa da adalcinsa, ya girmi kishiya ya girmi' sa a, babu me canja masa kaddara, babu me ja da hukuncinsa, babu Wanda ya isa ya rinjayi Al'amarinsa, wallahi nayi Imani da wannan duka kuma Ina da yakinin cewa duk daga gareshi ne..."zamu ci gaba inshaallah"
08100006272
Assalamu alaikum
Karatun littafin:
MURSHIDUD DULLAAB ILAA MA'ARIFATUS SAHAAB na Daya(1)
DAGA:DARUT TAUHEED
بسم الله الرمان الرحيم
س-ماالدليل علي تحريم سب الصحابة رضي الله عنهم؟
ج-قول النبي صلي الله عليه و سلم:لا تسبوا أصحابي فو الذي نفسي بيده لو أنفق أحدكم مثل أحد ذهبا ما بلغو مد أحدهم ولا نسيفه.
Tambaya:shin wani Dalili ne ya haramta a zagi sahabbai Allah ya kara musu yarda?
Amsa:shine fadan sa tsira da amincin Allah su tabbata a gareshi:"kada ku zagi sahabbaina na rantse da Wanda raina yake hannunshi da ace dayanku ze bayarda kwatan kwacin Dutsen uhudu na zinari ,baze kai mudu daya nasu ba(sahabbai) kai ko rabinshi ba ze kai ba.
***Da wannan hadisin da wasu masu k**a dashi zamu san ramcin zagi na sahabbai Allah ya kara musu yard ,
Kuma da wannan ne zamuga wani qima da daraja da Allah ya musu.
***Allahu akbar!!! Lallai sahabbai sunada daraja lallai sahabbai sunada Qima,kuma lallai Allah ya yarda dasu kuma suma sun yarda dashi
Allah ka kara mana San sahabbai
Anan zan takaita se mun hadu a darasi na gaba
Inda mukayi daidai Allah yabamu lada inda mukayi kuskure Allah ya gafartamana
SUBHANAKALLAHUMMA WABI HAMDIK NASH HADU AN LA'ILA ANT NASTAGFIRUKA WANA TUUBU ILAIK
Wassalamu alaikum.
بسم الله الرحمن الرحيم
عمدةالأحكام من كلام خيرالأنام صلى الله عليه وسلم
DAGA ZAUREN
KITABU WAS SUNNAH
Cigaba da karatu acikin littafin UMDATUL AHKAM
٦٣- وعن عائشة رضي الله عنها قالت: "لم يكن رسول الله صلى الله عليه و سلم على شيء من النوافل أشد تعاهدا منه على ركعتين الفجر"
و في لفظ لمسلم: "ركعتا الفجر خير من الدنيا وما فيها"
63- wa an Aisha radiyallahu anha qalat: lam yakun rasulullahi sallallahu alayhi wa sallam ala shay'in minan nawafili ashadda ta'ahudan minhu ala rak'ataynil fajri"
Wa fi lafzin li Muslim: " rak'ataal fajri khayrun minad dunya wa ma fiha"
Daga Aisha Ra tace manzon Allah saw bekasance mafi tsananin riko akan wata nafilaba k**ar yanda yarike raka,o,i biyu na alfijir
Awani lafazi na Muslim Raka,o,i biyu na alfijir sunfi dukkun duniya da abunda ke cikinta
Wannan hadisi yana kara nuna mana falala da matsayi Raka,atal fajri
Kamar yanda mukayi bayani abaya ita wannan sallah raka,a biyuce kuma anayintane bayan alfijir yafito kafin ayi sallar asuba
Amma idan mutum yamakara toh babu laifi seyayisu bayan yayi sallar asuba k**ar yanda akasamu sahabbai sunyi haka kuma Annabi saw behanasuba
Allah yasa mudace
Haza huwa ma indana wabillahit taufiq
DAGA ZAUREN KITABU WAS SUNNAH
BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM
INNAL HAMDU LILLAHI NAHMADUHU WANASTA,INUHU WANASTAGFIRUHU WANATUBU ILAIK
WANA,UZU BILLAHI MIN SHURURI AMFUSINA WAMIN SAYYI,ATI A,AMALUNA
Amma ba,ad
Assalamu,alaikum warahmatullahi wabarakatuhu
Karatu acikin littafin UMDATUL AHKAM
na babban Malami Allama
TAQIYUDDEEN ABDULGANIYU ALMAQDISI RH
wanda yarasu shekara ta Dari shida bayan hijira yau kimanin shekaru Dari takwas da talatin dashida da mutuwarshi
Allah madaukakin sarki yagafarta mishi
Abunda Malamin yabude littafin dashi shine yace
كتب الطحرة
Ma,ana littafin tsarki
Toh shikansa tsarki yakasu kaso biyune akwai
1طهر معنوية
2 طهرحسين
1 tsarkin ma,ana
2 Tsarkin zahiri
Tsarkin ma,ana shine mutum yatsarkake akidarsa da halayensa da ayyukansa akan wannan akwai aya cikin suratu tauba Allah yace Ka karbi sadaka DAGA cikin dukiyarsu don atsarkakesu da ita wannan sadakar wato zakka kenan
Idan muka duba zakka aiba ruwa bace Amma gashi Allah yace tana tsarkake mutane
Wannan yanuna tsarkin zuciya ake magana bawai tsarki na ruwa ko wani abuba
Awata ayar kuma Allah yace Lallaisu mushirikai najasane
Toh amma gashi suna wanka suna wanki kuma muna Mu,amala dasu dukda cewa su najasane
Meyasa idan s**a taba jikinmu bama wanke Inda s**a taba?
Amsa saboda su najasace ta ma,ana wacce ruwa baya iya wanketa imani shine kadai yake iya wanke wannan najasar tasu
Shi kuma tsarki hisiyyan shine duk wata najasarda ido yake ganinta harma hannu yatabata toh itace najasa hisiyyan tsarkinta kuma yazama dahara hisiyyan
Wannan itace najasarda ruwa yake iya kauda ita
Kamar fitsari ko bayan gida irinsu bola dasauran kazanta wayannan dukansu najasane hisiyyan
Amma hatta janaba itama najasace ma,anawiy tunda baganinta akeyi da idoba amma ansan akwaita
Itama haila najasace ma,anawiy amma jinin hailar shikuma najasane hisiyyan
Shi jinin anaganinshi harma ana tabashi donhaka yazama hisiyyan
Amma ita hailar ba,a ganinta tayanda dazarar kaga wacce take haila zaka gane donhaka itakuma ma,anace saboda bazaka ganeba sedai idan itace tagaya maka
Abunda kawai akeso Mugane shine
Duk wata najasarda ido yake ganinta. Toh itace najasa hisiyyan. Tsarkinta zezama dahara hisiyyan
Itakuma wacce ido baya ganinta amma antabbatarda ita kuma ansan lallai akwaita sedai ganintane ba,ayi
Toh tazama najasar ma,ana tsarkinta kuma Dahara ma,anawiy
Sekuma bambancin hadasi da khabasi
Hadasi shine duk wata najasarda take fita daga jikin mutum k**ar fitsari ko jinin haila ko maziyyi dasauransu
Khabasi kuma shine duk wata najasarda take fadowa jikin mutum daga waje k**ar ruwan kwata ko wata najasa wacce take shafar jikin mutum ko tufafinsa
Bayan haka kuma akwai karamin hadasi da babban hadasi
Karamin hadasi shine wanda yake wajabta tsarki k**ar fitsari ko bayan gida
Babban hadasi kuma shine take wajabta wanka k**ar janaba ko haila misali
Allah yasa mudace
Inda mukai kuskure Allah yayafe mana
SUBHANAKALLAHUMMA WABI HAMDIK. NASHHADU ANLA,ILAHA ILLA ANTA NASTAGFIRUKA WANATUBU ILAIK
Assalamu,alaikum
بسم الله الرحمن الرحيم
حصن المسلم- من أذكار الكتاب و السنة
DAGA ZAUREN
KITABU WAS SUNNAH
Cigaba da karatu acikin littafin HISNUL MUSLIM
MUQADDIMAH- iii
Alhamdulillahi wakafa, wasallillahumma wa sallim ala ibadhillazeenas dafa wa ba'adu;
Mun tsaya ne a falaloli na addu'a a darasin baya, wadda ayau za mu tashi ne akan
LOKUTAN DA AKAFI AMSAR ADDUA.
Yana da kyau mutum muslmi ya riqa qoqarin kitatar wadannan lokuta da addoi domin dacewa da biyan buqatun sa.
Duk da cewa manzon Allah sallallahu alayhi wa sallam yana ambaton Allah a duk halin dayake ciki.
To se mu fahimci cewa wadannan azkar da annabin rahma yakeyi a dukkanin lokuta, wayannan azkar ne lawazim wato na lazimi wadda ko ince dua ibadah, irin su adduoin bayan sallolin farilla, adduar bacci, adduar shiga ban daki da na fita, na shiga gida da na Fita, da dai sauransu.
Amma a babin lokutan da aka fi amsar addo'i, to ana maganar du'au mas'alah ne Wanda ake Neman biyan buqatu a wurin Allah ta'ala.
Kamar Neman arziki, aljannah, haihuwa, ilmi da sauransu.
Dangane da wadannan, an samu riwayoyi daga manzon Allah sallallahu alayhi wa sallama wadanda ke nuni da wasu kebantattun lokuta Wanda aka fi amsa addu a aciki; wadanda su ne أوقات الإجابة
Awqatul ijabah, a larabce. Daga cikinsu akwai:
1- kashi daya bisa ukun dare na qarshe. Kamar yadda manzon tsira ya ce Allah madaukaki yana saukowa saman duniya a kowace dare alokacin da ya rage yankin dare na qarshe yana cewa: wa ze roqe ni in amsa masa, wa zai tambaye ni in bashi, wa zai nemi gafara ta in gafarta masa.
2-LOKACIN SUJUDAH, k**ar yadda manzon Allah yace a cikin sujuda Ku yawaita addu'a.
3-A WANI SA'AH RANAR JUMU'AH
An rawaito manzon Allah yace a ranar jumu'ah akwai wata yar lokaci Wanda ba za ta riski musulmi yana tsaye yana sallah, yana kuma roqon Allah a cikinta, fyace Allah ya biya masa.
4- TSAKANIN KIRAN SALLAH DA IQAMAH:
manzon Allah sallallahu alayhi wa sallam ya ce,
Ba'a maido da adduan da akayi ta tsakanin kiran sallah da kuma iqamah.
5-LAILATUL QADRI:
Allah madaukaki ya ce "lailatul qadri khayrun min alfi shahrin" Daren lailatul qadri ta fi watanni dubu alkhayri hakanan adduar da aka yita a wannan dare karbabbe ne.
6-ADDUAR SHUGABA ADALI: manzon Allah ya qirga mutane uku da ba a maido da adduar su, dayansu shine shugaba adali, da mai azumi, da kuma Wanda aka zalunta.
7-ADDU,AR DA AKA YI WA MUTUM A BOYE:
manzon Allah yace adduar mutum musulmi ga Dan uwansa karbabbiya ce.
8-YAYIN FITO NA FITO DA MAQIYA :
Annabi s.a.w ya qirga abubuwa biyu da ba a dawo dasu, dayan su shi ne lokacin gwabzawa don daukaka Kalmar Allah.
9-ADDUA BAYAN SALLOLIN FARILLA:
abi umamah r.a ya tambayi manzon Allah sallallahu alayhi wa sallam wane addua ne aka fi amsa? Sai Annabi yace " cikin dare, da kuma bayan kowacce sallar farillah.
Anan za mu dakata inshaa Allahu, a darasin gaba zamu ji bayanai akan adduoi da aka hana yi dakuma Wanda ba a amsa adduoin su.
Subhanakallahumma wa bihamdik, ash-hadu an la ilaha illa anta astaghfiruka wa a tubu ilayka.
Wassalamu alaykum
بسم الله الرحمن الرحيم
عمدةالأحكام من كلام خيرالأنام صلى الله عليه وسلم
DAGA ZAUREN
KITABU WAS SUNNAH
Cigaba da karatu acikin littafin UMDATUL AHKAM
Hadisi nadaya
١ عن عمر بن الخطاب رضي الله عنه قال: سمعت رسول الله صلى الله عليه وسلم يقول: انما الأعمال بالنيات وفي رواية بالنية وإنما لكل امرئ ما نوى فمن كانت هجرته الى الله ورسوله فهجرته الى الله ورسوله ومن كانت هجرته الى دنيا يصيبها أوامرأة يتزوجها فهجرته الى ما هاجر إايه
1 An umar bn khaddab RA Qala Sami,itu Rasulallahi SAW Yakulu
INNAMAL A,AMALU BINNIYATI
wafi riwayatin BINNIYAH. WA,INNAMA LIKULLI IMRI,IN MANAWA. FAMAN KANAT HIJRATUHU ILALLAHI WARASULIHI FAHIJRATUHU ILALLAHI WARASULIHI. WAMAN KANAT HIJRATUHU ILA DUNYA YUSIBUHA AWIMRA,ATIN YATAZAWWAJUHA AU YANKIHUHA FAHIJRATUHU ILA MA HAJARA ILAIHI
Daga umar dan khaddabi yace naji manzon Allah SAW yana cewa LALLAI AYYUKA SUNA MANNE DA NIYYOYI. awata riwaya SUNA HADE DA NIYYA. KUMA LALLAI KOWANNE MUTUM YANATAREDA ABUNDA YAYI NIYYA DUK WANDA HIJIRARSA TAKASANCE ZUWAGA ALLAH DA MANZONSHI TOH SAKAMAKON HIJIRARSA TANA WAJEN ALLAH DA MANZONSHI WANDA KUMA YAYI HIJIRA SABODA WATA DUNIYA DAZE SAMU KO WATA MACE WACCE ZE AURA TOH SAKAMAKON HIJIRARSA YANAKAN WANNAN ABUN
Abinda hadisin yake karantarwa shine. Duk wani aikinda mutum zeyi toh yayishi saboda Allah yatsarkake zuciyarshi banda riya toh idan har akasamu mutum yayi aikine badon yaburge wani ko wasuba kawai yayine saboda Allah. Toh ladan wannan aikin zesameshi awajen Allah
Amma idan kayi aiki don kaburge wani kowata ko wasu toh komai kyawun aikinda kayi bakada lada awajen Allah sedai kanemi ladanka awajen wayannan mutanen wayanda kayi don kaburgesu
Dalilin dayasa Manzon Allah yafadi wannan hadisin shine
Lokacinda tsanani yayiwa musulmai yawa agarin makka Wanda yasa akai hijira zuwa madina. Toh yan madina sun yiwa musulmai gata. Idan kayi hijira zuwa madina se mutumin madina yaraba gidanshi biyu yabaka rabi kuma yasaki matarshi guda daya yabiya maka sadaki kai ka,aureta kokuma yabaka auren yarshi kuma yabaka Gona. Toh jin irin wannan alherin seyasa wasu s**aita yin hijira suna komawa madina domin suma susamu irin waccan garabasar
Shine manzon Allah yace Wanda duk yayi hijira saboda addini toh ladan hijirarda yayi zesameshi awajen Allah da Manzon Allah SAW
amma Wanda yayi hijira kawai domin yasamu irin wayancan abubuwan toh shikuma bashida sak**akon komai awajen Allah koda kuwa besamu anbashi garabasarba
Zan buga misali da wannan ZAUREN na KITABU WAS SUNNAH
Wanda yabude wannan ZAUREN idan yabudene saboda ayada Addinin Allah kuma don Allah. Toh sak**akon wannan aikin dayayi yana wajen Allah
Amma idan yabudene don aci mutuncin wani ko wata ko wasu mutane ko kungiya ko wata darika. Kokuma don yaburge wasu ko akare muradin wani ko wata. Toh bashida ladan komai awajen Allah
Sannan kuma nikaina Wanda Allah cikin ikonsa yasa nine nake jagorantar al,amuran wannan Zaure na KITABU WAS SUNNAH
Idan inayine domin bata ran wani ko wata kokuma inburge wata ko wani ko domin ace na,iya ko domin ayabeni ko don insamu kudi ko wata tasoni. Toh wallahi nayi aikin banza banida ladan komai awajen Allah
Amma idan inayine don Allah kuma don Insanarda mutane gwargwadon Abinda Allah yasanardani na addini toh wannan shine kadai abunda zesa insamu wani sak**ako awajen Allah
Wanda abisa wannan daliline yasa nake yawaita addu,ar Allah yasa mudace kusan duk karshen abunda hannuna yarubuta
Kuma shine yasa nake addu,a Allah yasa kar wannan aiki yazama musiba akaina nidaku
Kuma nake rokon Allah yasa wannan aiki yazama hujja garemu ba hujja akanmuba ranar alkiyama
Sannan kuma ita niyya ba furtata akeyi da bakiba
Ana kudurcetane azuciya
Acikin usulus SUNNAH na imamul humaidi
Yace da magana da aiki basayin amfani dole seda niyya sannan kuma koda ansamu niyyar mekyau toh batada amfani dole seta dace da SUNNAH
Kuma wannan maganar tana cikin akhdary. Hak**a risala
Sannan soda yawa yan,uwa muna fahimtar niyya abaibai
Sekaga mutum yana aikata sabo kokuma ana aikatamai sabo amma idan anyi magana seyace ai bada niyya yayiba
Toh wannan karyane. Ba,a fakewa da niyya adinga aikata mummunan aiki
Allama ibn salihul usaimin
Yace duk mutuminda yazo zeyi wani aiki seya bayyana niyya abaki toh hakika yayi bidi,a
Misali ada yanda mukeyi idan anzo wankan janaba kafin afara sai ance Nawaitu anil gusulil janabati. Har zuwa karshe
Toh wannan furicin bidi,ane
Ita niyya batada muhalli abaki sedai zuciya kadai a can ake kudirceta
Kuma ita niyya badole sai afannin aikiba
Hatta wajen magana niyya tanada muhimmanci
Duk maganarda zakayi Dan uwa lallai kayita da kyauktawar niyya
Kuma kayi kokari niyyarka da aikinka sudace da sunnar Annabi muhammad
Komai kyawun niyyarka da aikinka inhar s**aci karo da sunnar annabi toh hakika kayi aikin banza kuma wannan aikin da niyyar taka zasu zama hujja akanka ranar Alkiyama
Allah madaukakin sarki yatsaremu
Wannan hadisinda muka karanta
Bukhari yafitardashi awajaje bakwai cikin littafinsa. Sannan kuma shine hadisin farko cikin sahehul bukhari din
Abu dawuda 2201
Tirmizi 1637
NASA,I da ibn majah da ahmad cikin musnad da daru quduni, da baihaki duk sun ruwaito hadisin cikin littafansu
Sedai imam shafi,I kadaine yaruwaitoshi daga imam malik
Zamu dakata anan
Allah yasa mudace
Inda mukai kuskure Allah yayafe mana
SUBHANAKALLAHUMMA WABI HAMDIK. NASHHADU ANLA,ILAHA ILLA ANTA NASTAGFIRUKA WANATUBU ILAIK
Assalamu,alaikum
21/12/2015
KARATUN SUNAN IBN MAJAH NA YAU LAHADI 20/DEC/2015 DAGA DARUL-HADITH DAKE KANO AUDIO MP3
Sheik Dr. Ahmad Ibrahim B.U.K,
•Wannan shine Karatun Sunan Ibn Majah na Yau Lahadi wanda Sheik Dr. Ahmad Ibrahim B.U.K Yake Gabatarwa duk Mako a Darulhadith Foundation dake Unguwar Tudun Yola a Kano,
http://darulfikr.com/ #!/shared/3202
•Ga masu matsalar downloading sai subi ta wannan link dake kasa:
http://darulfikr.com/mobile/ #!/shared/3202
•Ayi sauraro lfy•
Ku cigaba da kasancewa damu a Darulfikr.com domin cigaba da samun karatukan maluman Sunnah.
Darulfikr.com Ta kuce Domin Yada Sunnah.
•Shiga wannan Rubutun na Kasa Kayi Like na wannan shafin Mai Al-barka:
•Like Basheer Journalist Sharfadi Abu Hafsah
www.facebook.com/abbanhafsah
•Ka Danna Kasa Domin Gayyatar Abokanan
Ka:
https://m.facebook.com/1696162707261773/invite_friends/?cancel_uri=%2Fabbanhafsah&ref=entries
© Copyright:
Basheer Journalist Sharfadi (Abu Hafsah).
09/03/1437 Ah. 20/12/2015Ac.
www.darulfikr.com
www.sahabbai.faa.im
Darul fikr Islamic Data Bank Free Access to Download Share of Islamic Lectures, Tafsir , Muhadarats
بسم الله الرحمن الرحيم
عمدةالأحكام من كلام خيرالأنام صلى الله عليه وسلم
DAGA ZAUREN
KITABU WAS SUNNAH
Cigaba da karatu acikin littafin UMDATUL AHKAM
٦٢- وعن عبد الله بن عمر رضي الله عنهما قال: صليت مع رسول الله صلى الله عليه و سلم ركعتين قبل الظهر، و ركعتين بعدها و ركعتين بعد الجمعة، و ركعتين بعد المغرب، و ركعتين بعد العشاء، وركعتين قبل الفجر"
62- wa an abdullahi bn umar radiyallahu anhuma qala: "sallaytu ma'a rasulillahi sallallahu alayhi wa sallam rak'atayni qablaz zuhri, wa rak'atayni ba'daha, wa rak'atayni ba'adal jumu'ati, wa rak'atayni ba'dal maghribi, wa rak'atayni ba'adal ishaa'i, waraka,ataini qablal fajri"
62 Daga Abdullahi Dan Umar Ra yace Nayi sallah tareda manzon Allah saw raka,o,i biyu kafin azahar, raka,o,i biyu bayanta, daraka,o,i biyu bayan juma,a daraka,o,i biyu bayan magriba, da raka,o,i biyu bayan isha,i, da raka,o,i biyu kafin azahar
Wannan hadisi yana karantardamu sallolin manzon Allah amma nafila watoh sune yakeyinsu haka amma banda rawatib su zamuyi bayaninsu can karshe insha,allahu saboda masu tambaya
وفى لفظ: " فأما المغرب والعشاء والجمعة: ففى بيته"
Wa fi lafzin: " fa'ammal maghribi wal isha'i wal jumu'atu: fa fi baytihi"
Awata magana Amma magriba da isha,i da juma,a agidanshi
Shikuma wannan bayanin yana warware mana wancan nafarkone cewa manzon Allah saw yanayin nafilar bayan magriba, da isha,i data bayan juma,a agidanshi
Sedai wannan baya nuna kwata kwata ba,ayinsu amasallaci ammadai ayisu agida shine yafi k**ala
وفى لفظ أن ابن عمر قال" حدثنى حفصة: أن النبي صلى الله عليه و سلم كان يصلى سجدتين خفيفتين بعد ما يطلع الفجر، وكانت ساعة لا أدخل على النبي صلى الله عليه وسلم فيها"
Wa fi lafzin Anna ibn umar qala " haddasani hafsah: annan nabiyya sallallahu alayhi wa sallam kana yusalli sajdtayni khafifatayni ba'ada ma yadlu'ul fajru wa kanat sa'atan la adkhulu Alan nabiyyi sallallahu alayhi wa sallam fiha".
Awata magana daga bukhari lallai Abdullahi dan umar yace hafsah tabani hadisi Lallai manzon Allah saw yakasance yana sallatar raka,o,i biyu (nan wajenda tace SAJDATAINI toh ba sujjadu biyu ake nufiba Raka,o,i biyu yanada kyau mugane gabar dakyau) raka,o,i biyu saukaka bayan alfijir yaketo hafsat tace wannan wani lokacine wanda bana shiga wajen manzon Allah acikinta
Atakaice shikuma wannan bayanin yana sanardamu muhimmancin raka,atal fajri sannan kuma yana nuna cewa ba,ayinsu se alfijiri yafito
Hadisi nagaba shine zekaramana haske gameda yanda akeyin raka,atl fajr
Sekuma maganar Rawatib
Yanda akeyinsu shine raka,o,ine guda 12 anayinsu k**ar haka
Raka,a biyu kafin sallar asubahi
Hudu kafin azahar
Biyu bayan azahar
Biyu bayanmagriba
Biyu bayan isha,i
Wayannan sune rawatib
Amma babu laifi afarayin biyu kafin azahar sekuma abiyu bayanta daguda hudu
Amma hudun anayinsune k**ar yanda akeyin sallar azahar da la,asar wato raka,a hudu tahiya biyu sallama daya
Allah yasa mudace
Haza huwa ma indana wabillahit taufiq
SUBHANAKALLAHUMMA WABI HAMDIKA ASH HADU ANLA ILAHA ILLA ANTA ASTAGFIRUKA WA ATUBU ILAIKA
Wassalamu Alaykum
Click here to claim your Sponsored Listing.
Location
Category
Website
Address
Maiduguri