Isa Usman Mohammed عيسى عثمان محمد

Isa Usman Mohammed عيسى عثمان محمد

Share

#IMAM__STM__COTONOU #عيسى_الغونى_جده I give u Islam as a gift I luv prophet Muhammad (S.A.W) I luv prophet Muhammad Sallalahu alaihi wasallam

Photos from ‎Isa Usman Mohammed عيسى عثمان محمد‎'s post 30/06/2025

ALLAH ZAI CIKA HASKENSA, KO MUNASO KO BAMASO INSHA ALLAH.

Chan na jiyo Yan Izala (Masu saukin cutar Kungiyanci) da Yan Dariku baki dayansu suna ta jerin gwanon addu’a ga kasar Iran (Yan Shi’a), cikin waki’ar da ta abku cikin kwanakin nan, sai ga shafuka duk ana rige-rigen posta Bidiyoyi da Hotuna irin na nasarar da kasar Iran ke samu akan abokiyar gabatarta, wato dai anyi baje kolin nuna yan uwantaka ta Musulunci, da kishin Musulmi, har aka mance da sabani, sai gashi ALLAH ya nuna Capacity irin na Musulmi cikin wannan yaki, sai na lura, ashe dai waki’a na sawa kawuna su hadu, ko da ace wasu na kallon reni da kuma tirjiya ga wanda yake kira zuwa ga hakan cikin dukkan majalisansa a inda suke.

Lallai duk wanda ya bibiyi wannan gagarumin taro da aka gabatar a birinin Kebbi akan wannan manufa ta hadin kai, to hakika zai tabbatar da cewa wannan jagora Maulana Prof. Ibrahim Maqari na samun nasara cikin kiransa, kuma lallai da sannu ko munaso, ko bamaso, dole zamu hadu da juna inda muka hadu, kuma lokaci na zuwa da zamuke yiwa juna uzuri inda aka samu sabani. Har ya zamo maslahar guda cikinmu zai zamo maslaharmu baki daya, haka matsalama.

ALLAH MUNA ROKONKA KA DAUKAKA WANNAN KURA NA HADIN KAI, KA KARAWA MUSULMI DA MUSULUNCI MARTABA DA KIMA ALFARMAR MANZON ALLAH (S.A.W).

ALHAMDULILLAH.

Photos from ‎Isa Usman Mohammed عيسى عثمان محمد‎'s post 29/06/2025

Taron Haɗin Kan Musulmi a birnin Kebb8: Hanya Zuwa Ƙarfafa Ƙawance da Fahimta tsakanin Kungiyoyin addini.

A cikin kokarin ƙarfafa haɗin kai da fahimtar juna tsakanin al’ummar Musulmi, an gudanar da Taron Haɗin Kan Musulmi wanda ya haɗa kungiyoyin addinin Musulunci daban-daban, tare da hadin gwiwar gidauniyar Qafilatul Mahabbah ƙarƙashin jagorancin Maulana Sheikh Prof. Ibrahim Makari.

Wannan taro yana da matuƙar muhimmanci duba da yadda zamanin ke cike da ƙalubale ga Musulmi. An jaddada bukatar gina zuciya ɗaya, kawar da bambance-bambancen da ke raba kawuna, da kuma samar da ingantacciyar fahimta da haɗin kai tsakanin mabambantan ƙungiyoyi.

Allah (SWT) ya ce:

> “Wa’taṣimū bi-ḥablillāhi jamī‘an wa lā tafarraqū.”
“Ku k**a igiyar Allah gaba ɗaya, kada ku rarrabu.” (Surah Āli ‘Imrān: 103)

Manzon Allah (SAW) ya ce:

“Al-Mu’min li al-Mu’min kal-bunyan, yashuddu ba‘ḍuhu ba‘ḍan.”

“Mumin ga Mumin k**ar ginin bango ne, sashe na karfafar sashe.” (Bukhari da Muslim).

Taron ya zama dandalin tattaunawa da gina zaman lafiya tsakanin Musulmi, tare da jaddada mahimmancin mu’amala da juna da girmamawa, da kaucewa rigingimu.

Muna fatan irin wannan taro zai ci gaba da haɓaka, domin Musulunci addini ne na zaman lafiya da haɗin kai.

ALHAMDULILLAH.

29/06/2025

1- Zai girmamaka a matsayinka dan adam ba tare da lura da matsayinka, yarenka, kabilarka ko dangantaka ba.

2- Yadda mahaifiya ke son ci gaban Danta a rayuwa, haka yake son ci gaban matasa. Da kokarin taimakasu cimma mafarkansu.

3- Ko kafi kowa kudi da mulki a Duniya, bai taba mu’amalanta da mu’amala ta neman wani abu wajenka, sai dai ku hadu wajen hidimar al’umma tare idan kana da niyyar hakan.

4- Zai iya haduwa da kowa, ko rabuwa da kowa akan abu guda ‘Gaskiya’ baya cuta, baya niyyar cuta, kuma baya lamuntar ha’inci, yaudara da kuma zamba.

5- Baya cin haramun, baya fita farautarta, haka zalika bata bashi sha’awa kuma masu kalaci da itama basu bashi sha’awa.

Shiyasa ALLAH ya tare masa wani irin kwarjini, duk yadda kake, idan kai Malamine, Sarki ko Mai Mulki ko Attajiri idan ya bayyana gareka sai kaji zuciyarka ta jinjina ganinsa. B***e talakawa da ya zamewa garkuwa.

ALLAH YA KARA KULAWA DASHI.

ALHAMDULILLAH.

28/06/2025

Wannan shine makon farko a wannan shekara ta 1447 bayan hijirar Annabinmu (sallal Laahu alaihi wa aalihi wa sallam).

Ya Allah muna rokonka don albarkacin abinda Alqur’ani ya Qunsa na ayoyi da kalmomi da harrufa da dige-digensa da wasulla da Sirrukan dake cikinsa, Ya Allah ka bamu dacewa da ayyuka nagartattu awannan shekarar, kuma ka kiyayemu daga miyagun ayyuka.

Ya Allah ka bamu babban rabo daga dukkan wata kyauta da baiwa da gafara da rahama da afuwa da falala da daukaka da fifiko da haske da farin ciki da arziki da budi wanda zakayi ma bayinka awannan shekarar.

Acikin wannan shekara da shekrun dake biye da ita, Ya Allah ka kiyayemu daga dukkan wani sharri da musiba da bala’i da Qunci da Qaskanci da talauci da matsi da bakin ciki da ta’bewa da zamewa daga tafarkin imani, afili ko aboye.

Ka tsare mana ga’bbanmu da harasanmu daga sa’ba maka. Ka aiwatar damu cikin neman yardarka Ya Mafi Jin kan masu Jin-kai.

Ka bamu lafiyar ruhi da lafiyar harshe da lafiyar jiki da lafiyar zuciyar da lafiyar aljihu da lafiyar tunani akoda yaushe.

Ya Allah ka rufa asiranmu ka jibinci lamuranmu ka faranta zukatanmu, Ka tsarkakemu daga riya da Zina da dangoginta da munafurci da hassada da Qiyayya da girman kai..

Ka kiyayemu daga dukkan zunubai na fili da na boye, Ka nufemu da aikata ayyuka karbabbu ako yaushe. Ka gafarta dukkan laifukanmu ka shiryemu ka shiryi ‘Ya’yanmu da Qannenmu da Matanmu. Ka kiyayemu daga bin hanyoyin ‘bata.

Allah yi salati mafi girma bisa Fiyayyen Annabawanka Annabinmu Muhammadu tare da iyalan gidansa tsarkaka da dukkan Sahabbansa da Mabiyansu har zuwa ranar sak**ako. Ameen.

DAGA ZAUREN FIQHU (27-06-2025 02-01-1447).

28/06/2025

FALALAR GANIMA GA AL’UMMAR ANNABI MUHAMMADU (S.A.W) A WATAN AL~MUHARRAM.

ANNABI MUHAMMADU (S.A.W) YA FADA YACE: “DUK WANDA YAYI AZUMI A JUMA’A TA FARKON WATAN

ﺍﻟﻤﺤﺮ ﻡ

ALLAH ZAI GAFARTA MASA ZUNUBAN SA WANDA YA WUCE NA SHEKARUN BAYA”.

2. ANNABI (Sallallahu Alaihi Wasallam) YACE: “DUK WANDA YAYI AZUMIN KWANAKI UKU A CIKIN WATAN

ﺍﻟﻤﺤﺮ ﻡ ﺍﻟﺨﻤﻴﺲ = ﻭﺍﻟﺠﻤﻌﺔ = ﻭﺍﻟﺴﺒﺖ =

ALLAH ZAI SA A RUBUTA MAKA/SA LADAN IBADAR SHEKARA DARI BAKWAI (700)”.

3. WANDA YAYI AZUMIN KWANAKI KOMA (10) NA FARKON WATAN “ﺍﻟﻤﺤﺮ ﻡ” ALLAH ZAI BAKA/SA ALJANNA FIRDAUSI MADAU KAKIYA”.

ALLAH KABA MU FALALAR WATAN DA SIRRIN WATAN DAN ALFARMAN ANNABI MUHAMMADU (Sallallahu Alaihi Wasallam)

27/06/2025

FA’I’DAN SABON SHEKARA

Muna Farinkin Zuwan Sabon Shekara Na Musulunci

ASRARUN DA AKEYI NA KARSHEN SHEKARA DAGA HALARAN MAULANMU SHEIK USMAN KUSFA ZARIA

Wanda Yayi Wannan Sirrin Daren Karshe Na Watan Zulhijja Ko Kuma Ranar Farko Na Watan Almuharram,.

ANNABI SAW Yace: Duk Wanda Yayi Allah Zai Mashi Gafaran Dukkan Zunuban Dake tsakaninsa da Allah Ta’alah sannan Kuma Allah Zai Karbi Dukkan Ibadunsa kuma Sheidan Zaije Yana Ihu Yana Kuka Yana Cewa: “YA KAICONSHI YA HASARANSHI YA TABEWANSHI, YA WAHALA TSAWON SHEKARA YANA SANYAKA ZUNUBAI AMMA GASHI KA BATA AIKINSHI A RANA DAYA”

GA YADDA SIRRIN YAKE:

• Mutum Zaiyi Nafila Raka’a Goma (10) a cikin Ko Wace Raka’a Zai karanta Fatiha kafa Daya Ayatul Kursiyyu Goma (10) Qulhuwallahu (10) Goma.

Idan Ya Idar Sai Ya Daga Hannayensa Ya Karanta Wannan Adduan:
“RABBI IGFIRLY , WALIWALIDIYYA WALI JAMI’IL MUMININA WAL MUMINATI AL AHYA’I MINHUM WAL AMWATI ” kafa Goma (10)

Sannan Kuma Ya kara da Wannan Adduan:
“ ALLAHUMMA MA AMILTU FI HAZIHISSANATI MIMMA NAHAITANY ANHU FALAM ATUB MINHU WALAM TARDHAHU WA NASITUHU WALAM TANSAHU WA HALIMTA ALAYYA BA’ABDA QUDRATIKA ALA UQUBATY WA DA’AUTANY ILA TTAUBATI BA’ADA JARA’ATY ALA MA’ASIYATIKA FA INNY ASTAGFIRUKA FAGFIRLY YA GAFURU, WAMA AMILTU FEEHA MIN AMALIN MIMMA TARDHAHU WA WA’ADTANY ALAIHI SSAWABA, FA AS’ALUKALLAHUMMA YA KAREEMU YA ZALJALALI WAL IKRAM AN TATAQABBALHU MINNY WALA TAQDA’A RAJA’I MINKA YA KAREEMU WASALLAHU ALA SAYYIDINA MUHAMMADIN WA ALA ALIHI WA SAHBIHI WASALLIM”
Kafa Uku

Umar Chobbe✍️

Allah ya bamu duk Alkhairan dake shekaran Kuma Yasa Shekaran Farincikinmu ne Albarkacin Annabi Muhammadu SALLALLAHU ALAIHI WASALLAM

27/06/2025

...Ana Karanta 'LAQAD JA'AKUM.....' Ƙafa(1918) a Kwanaki Goman Farko Na Muharram.

Saboda Neman Tsari Daga Dukkan Abin Ƙi, Da Kuma Neman Jalabi a Duk Sabuwar Shekarar(Musulunci) Da Muka Shiga.

Sirri/Izini Daga; Shariff Umar Haidara(R.A).❤️🙏

ALLAH Yasa Mun Shiga Wannan Sabuwar Shekarar(1447Ah), a Sa'a, Ya Kare Mu Daga Sharrin Dake Cikinta, Don Albarkar SHUGABA(S.A.W)🙏

Usman Muhammad✍️

Barkanmu Da Shiga Shekarar 1447Ah👌❤️🙏

26/06/2025

“...(A Matsayinka Na Batijjane); Ya Zama Dole Ka SO ‘Dan-uwanka BATTIJANE, Amma Ba Dole Bane Sai Ka Yi Mu’amala Da Shi”.

~ Sheikh Alhassan Kurgwi(R.A).

ALLAH Ya ‘Kara Mana ‘Kaunar Juna, Ya Bamu Ikon Kiyayewa, Ya Karawa SHEHU ALHASSAN(R.A) Lafiya Da Nisan Kwana🙏🙏💔

25/06/2025

MASU YIN GULMA
********************
Subhanallah!! Hakika Gulma ba Qaramar masifa bace!! Ba karamin bala’I bane. Masu yinta suna cikin asara marar iyaka.

Annabi (saww) yace: “Ranar da akayi Isra’I dani, na Wuce ta kusa da wasu Mutane suna da farce na azurfa, suna yakushin fuskokinsu dashi. Sai nace: “Wadannan kuma su waye Ya Jibreelu?”.

Sai yace “Sune Mutanen da suke Gulmar Jama’a, kuma suna afkawa cikin mutuncinsu”.
(Abu Dawud).

Watarana Annabi Eisa (as) sun hadu da Iblees (L.A) sai ya ganshi rike da zuma ahannunsa guda. A daya hannun kuma Baqar Qasa ce.

Da Annabi Eisa (as) ya tambayeshi game da haka sai yace: “Ita wannan Zumar ina sanyata ne akan harshen masu GULMA, shi yasa da zarar sun fara yinta sai an sauraresu. Kuma idan s**a fara sai sun idar. Ita kuma wannan baqar Qasar, ina sanyata ne akan fuskokin marayu. Ina munana k**anninsu shi yasa zaka ga Mutane suna Kyamatarsu, basu iya yi musu alkhairi”.

Hatamul Asammu (rah) yace: “Masu gulma da masu annamimanci, sune birrai na ‘yan wuta, Makaryata kuma sune karnukan ‘Yan wuta. Masu hassada kuma sune aladun ‘yan wuta”.

Inna lillahi wa inna ilaihi raji’un!!

Ya Allah kayi mana tsari daga sharrin gulma da magulmata da Annamimanci da masu yinsa.

- ZAUREN FIQHU - (16 FEB 2015).

24/06/2025

TAIMAKEKENIYA YANA AKAN AIKIN ALKHAIRI NE KAWAI

Musulmi suyi taimakekeniya akan da’a, aikin alkhairi da kuma fsoron Allah.

Amma babu taimakekeniya akan sabon Allah, zunubi da kuma zalunci.

Want your school to be the top-listed School/college in Maiduguri?

Click here to claim your Sponsored Listing.

Location

Category

Telephone

Address


CLOSE TO ARMY PRIMARY SCHOOL, CUSTOM BARRACKS, DIKECHIRI
Maiduguri
600223