24/08/2025
Assalamu alaikum, wannan cibiyar Ilimi Mai albarka da ikon Allah da yardar sa, a jiya tayi Hatamar kammala Daura na littafin As’halul Masalik (Sharhin Sirajus Saliki) bayan daukan kusan shekaru sama da uku tana yi, tare da kuma bawa Wa’yanda s**a halarci karatun Ijaza ta halartar karatun, Allah ya amfane Mu da sauran musulmi da abinda muka karanta.
Kuma masu bin mu ta Social Media, Allah ya saka muku da alkhairi.
Ameen
23/08/2025
Muna Gayyatar ‘yan uwa zuwa gurin Hatamar sauke Littafin ASHALUL MASALIKI SHARHIN SIRAJUS SALIKI Wanda BARRISTER SAYYADI ABDULLHI MUAZ RAIHAN AL-AZHARY ya karantar a masallacin TAFIDA TIJJANIYA CENTRAL MOSQUE karkashin jagorancin SHEIKH MUAZU ABDULLAHI MUAZU (Chief Imam Tafida Tijjaniya Mosque).
Date: Asabar 23/8/2025
Lokaci: daga Bayan sallan magariba zuwa Isha (7-8pm)
03/01/2025
Assalamu alaikum, In sha Allah daga gobe zamu ci gaba da karatuttukan mu kamar yanda muka Saba bayan dogon hutu da muka dauka sabida wasu al’amurra da s**a Bijiro mana.
Ga waenda bazasu samu zuwa karatun Ba a inda aka Saba yi, Zamu ci gaba da aiko da recording din karatuttukan cikin group dinmu na WhatsApp, ga masu tambayoyi kuma sai a aiko da tambaya a group kamar yanda aka saba.
Ga waenda basa cikin group ga link din: https://chat.whatsapp.com/C73WrvPPgWi6KrC6S3Wthj
Allah ya taimake mu gabaki daya.
Assalamu alaikum, In sha Allah we will continue our Fiqh Classes tomorrow after the long vacation we took due to unforeseen circumstances.
For those who cannot make it to the physical class, the recordings will be sent to our WhatsApp group.
The group will continue with it usual activities. And questions are to be directed into the group.
For those who are wish to join our WhatsApp group this is the link: https://chat.whatsapp.com/C73WrvPPgWi6KrC6S3Wthj
May Allah help us.
27/10/2023
Assalamu alaikum wa rahmatullah, Cibiyar karatu Mai suna Darul Fiqh Li Ta’alimit Turath wa Ihya’i Ulumid Deen (Wacce ta saba tsara karatuttuka a bangarorin mabanbanta na addini) na farincikin sanar da al’umma cewa zata fara sabon Daura akan RABON GADO nan ba da dadewa ba In sha Allah.
An karbo daga Sayyidina Abdullahi dan Amru Dan Aas, yace manzon Allah yace: “Ilimi guda uku ne, Banda su sauran falalane (wato Banda wannan ilimmai guda ukun, sauran ba dole bane koyan su) Al-Quran mai girma, ko Sunnah tsayayya (Hadisi), ko Adilin Gado (wato sanin ilimin rabon Gado tare da yin adalci).
عَنْ عَبْدِ اللَّهِ بْنِ عَمْرِو بْنِ الْعَاصِ أَنَّ رَسُولَ اللَّهِ صَلَّى اللَّهُ عَلَيْهِ وَسَلَّمَ قَالَ : ( الْعِلْمُ ثَلَاثَةٌ ، وَمَا سِوَى ذَلِكَ فَهُوَ فَضْلٌ : آيَةٌ مُحْكَمَةٌ ، أَوْ سُنَّةٌ قَائِمَةٌ ، أَوْ فَرِيضَةٌ عَادِلَةٌ ).
Akan haka ne muka ga ya kamata mu tsara karatu akan Rabon Gado sabida muhinmancin sa a addini.
Ga mai son yayi musharaka sai ya tuntube mu akan wannan nambar 08023482823.
Za’a kuma iya daukan nauyin wasu domin Kara Karfafa Ma dalibai guiwa gurin neman ilimin addini.
Sauran bayanai na kan flyer. Don Allah a taimaka mana da yin sharing. Wassalam.