14/03/2024
Attaqwa Islamic Da'awa Group
التقوى ها هنا
14/03/2024
26/09/2023
Ya Ɗan Uwa mai wahalar da kansa wai sai sun gane gaskiya, ka gane ita fahimta datarwace ta Allah. kuma gwargwadon yanda bawa ke nemanta. Akwai waɗanda duk iya bayanin ka baza su fahimce ka ba, domin sunyi isa kan ɓatar da suke kai. Baka ji abun da wani mai waƙa yake cewa ba?:
لَقَد أَسمَعتَ لَو نادَيتَ حَيّاً #وَلَكِن لا حَياةَ لِمَن تُنادي
ولو نارا نفخت بها أضاءت #ولكن أنت تنفخ فى رماد
Ma'ana: " Haƙiƙa ya jika da mai rai kake kira, sai dai kash babu rayuwa ga wanda kake kira, da kuma wuta kake ta hurawa, iyanzu da ya k**a, sai dai kash, toka kake ta hurawa(Kaga she ba ranar da tokan zai k**a da wuta)".
Dan haka ka gane an daɗe ana ruwa ƙasa na shanyewa. Allah ya bamu kyakkyawar Fahimta da maƙal-ƙale wa Sunnar Annabin Rahma Muhammad ﷺ💕💕💕💕💕💕
WASIYYA DOMIN RIBATAR RAMADAN 018
Dan uwana yanda kaga kwanaki na ta gudu haka shin ka lura da wani abu kuwa? Dage kayi tunani sannan ka zage dan kar bayan gushewar wadannan kwanakin masu Albarka ka dunga da na sani, domin bamu da tabbacin sake samun dama irin wannan da muka samu. Sannan ka sani cewa sada zumunci da ziyartar mutanen kirki da guraren kirki shima na cikin ladduban Azumi.
Allah ka datar da mu kasa mu cikin bayinka da za su ribaci wadannan kwanakin masu Albarka.
01/01/2020
Assalamu Alaikum
قال رسول الله صلى الله عليه وسلم:((لا تدخلوا الجنة حتى تؤمنوا،ولا تؤمنوا حتى تحابوا، أولا أدلكم على شيء إذا فعلتموه تحاببتم ؟ أفشوا السلام بينكم)). رواه مسلم، من حديث أبي هريرة رضي الله عنه.
Gaisuwa gareku
Assalamualaikum
Click here to claim your Sponsored Listing.
Location
Category
Telephone
Website
Address
Bulumkutu
Kano