GM HAUSA NEWs

GM HAUSA NEWs

Share

Contact information, map and directions, contact form, opening hours, services, ratings, photos, videos and announcements from GM HAUSA NEWs, No. 641 Koki Mariya Sunusi Dantata Street, Kano.

Mun Bude Shafin GM HAUSA NEWS Ne Domin Kawo Muku Labarai Cikin Harshen Hausa Cikin Gida Da Wajen Qasar Nan.

-Burinmu Ku Kasance Tare Damu Koda Yaushe
-Aikinmu Dominku ne
-Tasharmu Takuce

@whatsapp 08093547661,
Kuyi Mana Like Da Share Da Comment Mungode

Photos from GM HAUSA NEWs's post 01/05/2026

‎2027: Sanata Shehu Sani, ya sami karbuwa a wajen shuwagabannin jam'iyya na kananan hukumomin jahar kaduna gaba daya.

‎A wani muhimmin ci gaban siyasa gabanin zaben shekarar 2027, tsohon sanatan da ya wakilci Kaduna ta Tsakiya, Kwamared Shehu Sani, ya kammala wata ziyarar dabarun siyasa a kananan hukumomi bakwai na Jihar Kaduna, inda ya samu gagarumin goyon baya daga shugabannin jam’iyya da masu ruwa da tsaki na kasa.

‎Ziyarar, wacce ta dauki kwanaki da dama, ta bai wa dan gwagwarmayar kare hakkin bil’adama da ya koma siyasa damar ganawa kai tsaye da shugabannin jam’iyya na matakin mazabu da kananan hukumomi, shugabannin al’umma, kungiyoyin matasa da na mata. Kananan hukumomin da aka ziyarta sun hada da Kaduna North, Kaduna South, Igabi, Chikun, Kajuru, Kachia da Birnin Gwari.

‎A kowane wuri, Sani ya gudanar da tarurrukan tuntuba da shugabannin jam’iyyar All Progressives Congress (APC) da sauran masu ruwa da tsaki, inda aka tattauna dabarun tunkarar zabe mai zuwa.

‎A yayin ganawar, tsohon dan majalisar ya bayyana goyon bayansa ga yunkurin sake zaben Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu da kuma Gwamnan Kaduna Uba Sani a shekarar 2027.

‎Masu ruwa da tsakin da s**a zanta da manema labarai sun bayyana tarurrukan a matsayin wani yunkuri na karfafa hadin kan jam’iyya, sake gina amana, da kuma tsara ajandar ci gaba mai cike da hada kai da shugabanci nagari.

‎Shugabannin jam’iyya a dukkan kananan hukumomin bakwai sun kada kuri’ar amincewa da Sani, suna mai yabon tarihinsa a bangaren fafutukar majalisa, ci gaban mazabu, da kuma gwagwarmayar kare hakkin bil’adama.

‎A karamar hukumar Igabi, shugaban jam’iyyar ya bayyana shi a matsayin “gada tsakanin jama’a da gwamnati,” yana mai jaddada saukin samunsa da kuma yadda yake tsayawa kan al’amuran kasa.

‎Shugabanni a Chikun sun yi alkawarin tattara goyon baya, suna bayyana Sani a matsayin “muryar marasa galihu da mai kare darajojin dimokuradiyya,” tare da tuna rawar da ya taka lokacin rikicin da ya shafi shirin rusa unguwar Gbagi-Villa a zamanin tsohon gwamnan Kaduna, Malam Nasir El-Rufai.

‎Irin wadannan kalamai sun fito a Birnin Gwari, inda shugabannin al’umma s**a yaba da gudummawar da ya bayar wajen ci gaban yankin, ciki har da tallafin ilimi da lafiya, da kuma matsayinsa kan matsalar tsaro.

‎A Kajuru kuwa, masu ruwa da tsaki sun tuna da yadda ya yi fafutukar bayyana halin da al’ummomin da rikici ya shafa ke ciki, musamman a lokutan tashin hankali.
‎Kungiyoyin mata da s**a halarci tarurrukan sun kuma bayyana goyon bayansu, suna ambaton shirye-shiryen tallafa musu da aka fara a lokacin da yake kan mulki da kuma fafutukarsa kan adalci da hada kai.

‎Da yake jawabi ga masu ruwa da tsaki, Sani ya sake jaddada kudurinsa na karfafa hadin kan jam’iyya da magance manyan kalubale kamar rashin tsaro, rashin aikin yi, gibin ababen more rayuwa, da kuma bukatar ingantacciyar wakilci.

‎“Dole ne mu sake gina tsarin siyasar mu daga tushe. Karfin kowace dimokuradiyya yana hannun jama’arta. Na zo nan ne domin saurare, koyo, da aiki tare da ku domin makoma mafi kyau,” in ji shi.
‎Ya kuma jaddada muhimmancin hadin gwiwa wajen magance matsalar tsaro, musamman a yankunan karkara, tare da bayar da shawarar manufofin da za su fadada damar tattalin arziki ga matasa.
‎Bayanai sun nuna cewa ziyarar wani shiri ne na sake kusantar jama’a da kuma tabbatar da tasirinsa a sabon yanayin siyasar Kaduna.

‎Haka kuma bincike ya nuna cewa irin wadannan goyon bayan daga matakin kananan hukumomi na da matukar muhimmanci wajen auna karfin dan takara a jihar, wacce aka san ta da hadadden yanayin siyasa mai tsananin gasa.

‎Ko da yake ana kallon Sani a matsayin dan siyasar da ke da tushe a kasa, girman goyon bayan da ya samu yayin ziyarar ya nuna alamar karuwar tasiri kan yiwuwar dawowarsa siyasa.

‎A halin yanzu, sakamakon ziyarar ya sake tabbatar da tasirinsa a siyasa, tare da nuna muhimmancin hulda da jama’a daga tushe a tsarin dimokuradiyyar Najeriya.

01/05/2026

Kullum sai gwamnati takarbi wani abu agurinka toh amma kai metake bakane.hanya asibiti wuta kudin makaranta ko jari.

Munata rigima sai wane sai wane karfa kamanta haryanzu inda kake rayuwa idan kaje asibiti babu wata gudunmawa dakake samu amatsayinka na dan kasa. Hanyoyi da yawa cikin Nigeria baka isa kabisu ta yadda kakeso ba.

Karkamanta yau indai kanada opay ko moniepoint ko other bank sai ancire wani kaso aciki anturawa gwamnati.amma kuma kai har yanzu kakitsaywa kayi focusing akan sana'arka. Bangar siyasa shirmece da ɓata lokaci. Kuma hakan babu abinda yake kawowa saikara tuzurasu suyima akuyanci idan sunhau kujerar mulkin.

Kazabi chanchanta kar dubu goma tarufemaka ido inkuma badama kakoma gefe kayi aiki maikyau wadan nan mutanan mubarsu da allah.

Photos from GM HAUSA NEWs's post 01/05/2026

DA DUMI-DUMI

An sasanta 'yan takarar jihar Borno, Mustapha Gubio, ya zama dan takarar Gwamnan jihar Borno a karkashin jam'iyyar APC.

01/05/2026

Sanata Kaka Lawan ya janye daga takarar gwamnan Jihar Borno, inda ya bayyana goyon bayansa ga Mustapha Gubio, ɗan takarar da Gwamna Babagana Zulum ya zaɓa.

Ya ce ya ɗauki wannan mataki ne domin tabbatar da haɗin kai da zaman lafiya a cikin jam’iyya.

30/04/2026

Masu hankali sun fahimci abunda nake nufi. Masu son a gaya musu abunda zai musu dadi na dan wani lokaci kuma dama ba ta tasu ake ba.

Abunda dai ya zama wajibi shine mu daura damarar yaki da Tinubu domin so yake ko ta wane hali sai ya koma. Maganar hukuncin kotun koli kuma bana kallonsa a matsayin wani abu da zai taimaki ADC.

Hikima Fagge

https://whatsapp.com/channel/0029VbAkaqo6WaKt4Xk6Ky08

Kana Son Kasancewa Cikin Sahun Farko Domin Samun Ingantattun Labarai Kasance Da GM HAUSA NEWs

Photos from GM HAUSA NEWs's post 30/04/2026

Gwamnonin PDP da manyan jagororin jam’iyyar sun shiga taron sirri a Abuja

Rahotanni da suke shigowa yanzu sun tabbatar da cewa gwamnonin jam’iyyar PDP tare da manyan jiga-jigan jam’iyyar suna gudanar da wani taron gaggawa na sirri a birnin tarayya Abuja.

Taron, wanda ke gudana cikin daren yau, na zuwa ne biyo bayan rikicin shugabanci da ya dabaibaye jam’iyyar, musamman bayan hukuncin da Kotun Ƙoli ta yanke wanda ya haifar da sabon salo na muhawara da rashin jituwa a cikin jam’iyyar.

Majiyoyi daga cikin jam’iyyar sun bayyana cewa ana gudanar da taron ne domin tattauna hanyoyin shawo kan rarrabuwar kawuna da ta kunno kai tsakanin mambobin kwamitin ayyuka na kasa, wato NWC, da kuma yadda za a dawo da hadin kai a tsakanin shugabanni.

Rahotanni sun nuna cewa shugabannin na PDP na duba matakan da s**a dace su dauka domin tabbatar da cewa rikicin bai kara lalata tsarin jam’iyyar ba, musamman yayin da ake tunkarar manyan kalubalen siyasa a gaba.

Har zuwa lokacin hada wannan rahoto, babu cikakken bayani daga bakin jami’an jam’iyyar kan matsayar da aka cimma a taron, amma ana sa ran za a fitar da sanarwa bayan kammala ganawar.

Wannan na zuwa ne a daidai lokacin da masu ruwa da tsaki ke kira ga shugabannin jam’iyyar da su hada kai domin kare martabar PDP a matsayin daya daga cikin manyan jam’iyyun siyasa a Najeriya.

Za mu ci gaba da kawo muku karin bayani da zarar mun samu sabbin rahotanni kan wannan lamari.

Ku biyo mu domin samun sabbin labarai masu sahihanci👇

GM HAUSA NEWs

https://whatsapp.com/channel/0029VbAkaqo6WaKt4Xk6Ky08

Photos from GM HAUSA NEWs's post 30/04/2026

Atiku Abubakar ya halarci muhimmin taron shugabanni da jiga-jigan ADC a Gidan Sanata David Mark

Tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa, Atiku Abubakar, ya haɗu da manyan shugabanni da jiga-jigan Jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) a gidan Shugaban jam’iyyar, Sanata David Bonaventure Mark, wanda aka bayyana a matsayin jagora mai jajircewa wajen tafiyar da jam’iyyar.

Wannan taro na musamman ya fara gudana ne domin tattauna muhimman batutuwa da s**a shafi ƙarfafa haɗin kai, daidaita matsaya, da kuma tsara sabuwar hanyar da jam’iyyar za ta bi a gaba.

https://whatsapp.com/channel/0029VbAkaqo6WaKt4Xk6Ky08

Kana Son Kasancewa Cikin Sahun Farko Domin Samun Ingantattun Labarai Kasance Da GM HAUSA NEWs

Photos from GM HAUSA NEWs's post 30/04/2026

Dr. Aminu Yuguda ya Mika Takardan Aniyar sa ta Takaran Gwamna wa Jami'yyar APC a Jihar Gombe.

Babban Akawu na jihar Gombe, kuma 'daya daga cikin 'yan takaran Gwamna a jihar karkashin jami'iyyar APC, Dr Aminu Yuguda ya jagoranci tawaga mai karfi da s**a ha'da da dattawa, 'dinbin magoya baya, 'yan uwa da abokan arziki zuwa sakatariyar jami'yyar APC ta karamar hukumar Gombe, kana daga bisani ya nausa zuwa Sakatariyar Jami'iyyar ta jiha domin mika takardar nuna sha'awa da aniyar sa a hukumance ta takaran kujeran Gwamna a za'ben dake tafe na shekaran 2027.

Irin tagomashi da ayarin tawagar sa tayi yayin tattaki akan manyan hanyoyi na fadar jiha, da kuma irin jigonnin masu ruwa da tsaki a siyasar yau da tawagar ta 'kunsa 'yar manuniya ce cewa lalle Dr Aminu Yuguda, na da goyon bayan al'umma kwarai da gaske.

Ku biyo mu domin samun sabbin labarai masu sahihanci👇

GM HAUSA NEWs

https://whatsapp.com/channel/0029VbAkaqo6WaKt4Xk6Ky08

Photos from GM HAUSA NEWs's post 30/04/2026

DA DUMI-DUMI: INEC ta mayar da sunan David Mark a matsayin Shugaban ADC na ƙasa tare da mambobin NWC a cikin tsarin ta, bayan hukuncin Kotun Koli na yau.

https://whatsapp.com/channel/0029VbAkaqo6WaKt4Xk6Ky08

Kana Son Kasancewa Cikin Sahun Farko Domin Samun Ingantattun Labarai Kasance Da GM HAUSA NEWs

Photos from GM HAUSA NEWs's post 30/04/2026

INNALILLAHI

DA DUMI-DUMI: Dan takarar dan majalisar tarayya na Mani/Bindawa ya zaro bindiga zai harbi wani har barzahu a wurin taron Consensus, da kyar jami'an DSS s**a kwace bindigar.

Photos from GM HAUSA NEWs's post 30/04/2026

Labarai da dumi-dumin su!

Kotun koli da ke babban birnin tarayya Abuja ta tabbatar da shugabancin jam'iyyar ADC bangaren su David Mark.

30/04/2026

Gwamnan Jahar kaduna sanata Uba sani, ya sanyawa shehu sani Albarka bayan Daya Kai masa form dinsa Daya siya na tsayawa takarar kujerar sanata tsakiyar jihar.

Want your school to be the top-listed School/college in Kano?

Click here to claim your Sponsored Listing.

Location

Telephone

Address


No. 641 Koki Mariya Sunusi Dantata Street
Kano
700252