QURUCIYA DA TSUFA......
Akwai wani lokaci can da muka je wani qauye a irin family house din nan na karkara Muna wani bangare a gidan Muna hira da Matan gidan, sai mu ka ji ana Kira a fito Malama tazo za a fara karatu sai Matan duk s**a fita s**a tafi wurin Malamar daukan karatu
Ina zaune sai yaro ya shigo wurin da nake, nake tambayar Shi WACECE malamar dake karatun
Sai yaron yace wata tsohuwa ce
Sai na tafi wurin masu karatun Don naji irin karatun nasu
Allah ya sani naje ne naji irin karatun nan na tsofaffin qauye da suke wa Mata na shirme
Hasbunallahu wani'imal wakeel wani irin shocking naji a jikina Yayin da naje wurin naga yanayin shekarun malamar da kuma irin karatun da take koya musu
Baiwar Allahn ta TSUFA sosai Don ko tafiya da Sanda take yi,
Sayyidil istigfar take koya musu, wasun Su kuma Addu'ar neman tsari daga shirka take koya musu,
Wallahi karatu ne cikin nutsuwa duk Wanda yayi kuskuren harafi sai ta gyara musu
bayan sun gama ta tafi nake tambayar wata cikin Matan game da malamar,
Take sanar Dani shekarun malamar sun haura a Dari, Amma baiwar Allah n tana cikin nutsuwa baza ka taba jingina Mata rikitar TSUFA ba
Mashaa Allahu da gani kasan akwai kyakkyawan zaton baiwar Allah n tayi kyakkyawar quruciya, Shi yasa tsufan ta ma yayi kyau
Haka na karanta cikin wani littafi mai suna MESSAGE TO EVERY YOUTH nasihohi masu ratsa zuciya GA Matasa Wanda har sai da na zubda hawaye, Mai littafin ya hakaito wani Labari acikin littafin yace wani matashi ya bashi labarin mahaifin sa ya Kai shekaru 120 a duniya, Amma yace sallar jam'i bata kubce masa, haka nan haqoran sa Ko guda daya bai fadi ba, haka idanuwan sa tas yake gani, haka kunnuwan lafiya lau yake ji, yace Amma game da quruciyar sa mutumin qwarai ne yana da kyakkyawar mu'amala Kuma yana damuwa da al'amuran addini sosai
Nasan kowanne matashi zai yi burin Idan Allah ya qaddaro masa shekaru masu yawa a rayuwar sa to ya samu kyakkyawan tsufa,
Shi kuma kyakkyawan tsufa yana biyo bayan kyakkyawar quruciya ne
Dandalin Tunatarwa
It is all about islamic religion Fazhakkir fa inna zhikra tanfa'ul mu'uminoon
WADANDA MALA'IKU SUKE YIWA SALATI:
Allah ya bamu labari acikin alqur'ani mai giram,lallai Mala'ikunsa suna yin Salati ga Annabi s.a.w. Allah yana cewa:
{Lallai Allah da Mala'ikunsa suna yin Salati ga Annabi"S.A.W" Yaku Wadanda s**ayi Imani kuyi Salati agareshi.....}.
Ahzab.
Kuma Allah yana bamu labari cewa Mala'iku suna yin Salati ga Mumminai. Allah yana cewa:
{Allah shine yakeyin Salati agareku,da kuma Mala'ikunsa, dan yafitar daga duffai zuwa ga Haske}.
Ma'anar Salatin Mala'iku:
Salatin Mala'iku ga Mutane yana nufin nema masu gafara da yimasu Addua awajan Allah.
# ﻈﺮ : ﻓﻀﻞ ﺍﻟﺼﻼﺓ ﻋﻠﻰ
ﺍﻟﻨﺒﻲ [ 1 / 79 ].
Annabi s.a.w ya bayyana mana wadansu mutane da Allah ya sanya Mala'iku suyi masu Salati,ga kadai daga cikinsu:
1-Duba Marar Lafia:
Annabi s.a.w yana cewa:
[Babu wani Musulmi da zai je duba marar Lafiya Musulmi, face sai Allah ya aiko Masa Mala'iku guda 70,000 suna yi masa Salati akowane lokacin na yini yaje dubasa, har sai yakai yammaci,idan kuma da dare har sai sunkai safiya].
# ﺻﺤﻴﺢ ﺍﻟﺘﺮﻏﻴﺐ ﻭﺍﻟﺘﺮﻫﻴﺐ [ 3/197
2-Wadanda suke yiwa Annabi s.a.w Salati:
Annabi s.a.w yana cewa:
[Babu wani bawa da zaiyi Salati agareni,face Mala'iku sunyi masa Salati,Matuqar yayi mani Salati,Sai bawa ya yawaita yi mani Salati ko ya takaita].
# ﺻﺤﻴﺢ ﺍﻟﺠﺎﻣﻊ
[ 5/174
3-Masu yin Sahur:
Annabi s.a.w yana cewa:
[Lallai Allah da Mala'ikunsa sunayin Salati ga Masu shan Sahur].
# ﺻﺤﻴﺢ ﺍﻟﺘﺮﻏﻴﺐ ﻭﺍﻟﺘﺮﻫﻴﺐ [ 1 257/
# ﺻﺤﻴﺢ ﺍﻟﺘﺮﻏﻴﺐ ﻭﺍﻟﺘﺮﻫﻴﺐ
[ 1/258
4-Masu koyar da Mutane alkhaairi:
Manzon Allah s.a.w yana cewa:
[Lallai Allah da Mala'ikunsa da Ma'abuta cikin sama da kasa,hatta tururuwa acikin gidanta da kifi acikin ruwa sunayin Salati ga Wadanda suke koyar da Mutane alkhairi].
# ﻭﺻﺤﻴﺢ ﺍﻟﺘﺮﻏﻴﺐ
ﻭﺍﻟﺘﺮﻫﻴﺐ [ 1 / 19.
5-Masu cike Sahun Sallah:
Annabi s.a.w yana cewa:
[ Lallai Allah da Mala'ikunsa sunayin Salati ga Masu sadar da sahu].
# ﻣﺸﻜﺎﺓ
ﺍﻟﻤﺼﺎﺑﻴﺢ [ 1 / 241
Abinda ake nufi da sadar. Da Sahu:shine mutum yaga wani gurbi asahun gabansa sai ya matsa ya sadar da shi yacikesa.
6-Wadanda Suke yin Sallah a Sahun farko:
Manzon Allah s.a.w yana cewa:
[Lallai Allah da Mala'ikunsa suna yin Salati ga masu yin Sallar a Sahun farko.......].
# ﺻﺤﻴﺢ ﺍﻟﺘﺮﻏﻴﺐ ﻭﺍﻟﺘﺮﻫﻴﺐ [ 1 / 58
# ﺻﺤﻴﺢ ﺍﻟﺘﺮﻏﻴﺐ ﻭﺍﻟﺘﺮﻫﻴﺐ
[ 1 118/
7-Masu jiran Sallar bayan sallah acikin Masallaci:
Annabi s.a.w yana cewa:
[............Kuma Mala'iku suna yi masu Salati matukar dai suna cikin innda s**ayi Sallah,suna cewa: Allah kayi masa gafara Allah kayi masa rahama,Allah ka karbi tubansa, sunayi masa hakan matukar baiyi hadasi ba].
# ﺻﺤﻴﺢ ﺍﻟﺠﺎﻣﻊ [ 1 / 728
Allah ka sanya mu cikin bayinka wadanda ka keyiwa Sallati da Mala'ikunka.
23/08/2021
SADAKA TANA HANA ZAFI DA KUNCI QABARI
Qabari shine masaukin farko daga cikin mas**ai na ranar Alqiyama idan mutum ya tsira acikinsa to abinda zai biyo bayansa zaizo masa mafi sauki,amma idan ya tabe acikinsa to abinda zai biyo bayansa yafi tabewa da wahala.
Qabari yana zama Dausayi daga cikin dausayin Aljanna,Allah ya sanya namu ya zama haka,ko ya zama rami daga cikin ramika cikin wuta,to Allah ya karemu daga wannan.
Hakika ana samun kunci da wahala da kuma jin dadi da ni'ima acikinsa da rahama,daga cikin abubuwan da suke sanyawa mutum ya kubuta daga kuncin qabari da azabarsa bayan Imani da Addu sai SADAKA.
*SADAKA NA MAGANIN KUNCIN QABARI*
Manzon Allah
صـلى الله علـيه وسـلم:
Yace;
*(Lallai Allah yana karbar Sadaka,yana amsartane da Hannunsa na Dama,sai ya reni wannan Sadakar wannan,k**ar yanda dayanku yake renon dan karamin raquminsa har ya girma,har sai kaga Sadakar Loma guda takai girman dutsen Uhudu)*
@صحيح الترغيب (٨٥٦)】
Manzon Allah
صـلى الله علـيه وسـلم:
Yana cewa;
*(Lallai Sadaka tana Tunkudewa mai yinta kunchi da zafin Qabari,Kuma masu Sadaka suna cikin Inuwar sadakarsu a ranar Alqiyama)*
@صحيح الترغيب (٨٧٣)
✍الإمـام ابـنُ القَـيّم رَحِمَـهُ الله;
Yana cewa;
"Lallai Sadaka tana da Tasibi da Al'ajiba mai yawa,wajan tunkude bala'i da masifa ga kai yinta,koda mai yin sadakar Fajirine ko Kafirine"
@لـوابل الصيب صــ (٣۱)
Allah ne mafi sani
Allah ka karemu daga Azabar qabari da Azabar wuta da Azabar ranar alqiyama.
KA KYAUTATAMA MAKWABCINKA ZAKA ZAMA MUMINI........
Daga Hasan daga Abi Hurairata Allah ya kara masa yarda, Annabi s.a.w yana cewa:
(Wanene zai yi roko da wadansu halaye guda biyar daga cikin al'ummata yayi aiki dasu,kuma ya sanarwa wanda
zaiyi aiki dasu???sai nace gani ya Manzon Allah.sai Annabi s.a.w ya k**a hannuna ya kirga min,sannan yace:
1-Ka kiyaye abubuwan da Allah ya haramta,sai kazama mafi yawan ibada daga cikin mutane.
2-Ka zama mai yarda da abinda Allah ya baka,zaka zama mafi wadatal mutane.
3-Ka kyautatawa makwabcinka zaka zama mumini.
4-Kasowa mutane irin abinda make soma kanka zaka zama cikakken musulmi.
5-Kada ka yawaita yin dariya domin yawan dariya yana busar da zuciya.).
@ﺃﺧﺮﺟﻪ ﺃﺣﻤﺪ ( 2/310 ، ﺭﻗﻢ 8081 ) ، ﻭﺍﻟﺘﺮﻣﺬﻱ( 4/551 ، ﺭﻗﻢ 2305 ) ، ﻭﻗﺎﻝ : ﻏﺮﻳﺐ ، ﻭﺍﻟﺒﻴﻬﻘﻰﻓﻲ ﺷﻌﺐ ﺍﻹﻳﻤﺎﻥ ( 7/78 ، ﺭﻗﻢ 9543 ) .ﻗﺎﻝ
ﺍﻷﻟﺒﺎﻧﻲ ﻓﻲ "\ ﺍﻟﺴﻠﺴﻠﺔ ﺍﻟﺼﺤﻴﺤﺔ "\ 2 /
637 : ﺃﺧﺮﺟﻪ ﺍﻟﺘﺮﻣﺬﻱ ( 2 / 50 ) ﻭ ﺃﺣﻤﺪ ( 2 /310 ) ﻭ ﺍﻟﺨﺮﺍﺋﻄﻲ ﻓﻲ "\ ﻣﻜﺎﺭﻡ ﺍﻷﺧﻼﻕ "\ ﻗﺎﻝﺍﻟﺸﻴﺦ ﺍﻷﻟﺒﺎﻧﻲ : ( ﺣﺴﻦ ) ﺍﻧﻈﺮ ﺣﺪﻳﺚ ﺭﻗﻢ : 100 ﻓﻲ ﺻﺤﻴﺢ ﺍﻟﺠﺎﻣﻊ .
Hakika musulunci ya kwadaitar akan kyautatama makwabta, sannan ya sanya hakan acikin hanyar tabbatuwar imanin bawa,kuma hakika Allah ya bayyana girma hakkin makwabci kuma yayi nunin hakan acikin littafinsa,kuma ya wajanta kyautata masa. Allah yana cewa:
(ﻭَﺍﻋْﺒُﺪُﻭﺍﺍﻟﻠَّﻪَ ﻭَﻻ ﺗُﺸْﺮِﻛُﻮﺍ ﺑِﻪِ ﺷَﻴْﺌﺎً ﻭَﺑِﺎﻟْﻮَﺍﻟِﺪَﻳْﻦِ ﺇِﺣْﺴَﺎﻧﺎً ﻭَﺑِﺬِﻱﺍﻟْﻘُﺮْﺑَﻰ ﻭَﺍﻟْﻴَﺘَﺎﻣَﻰ ﻭَﺍﻟْﻤَﺴَﺎﻛِﻴﻦِ ﻭَﺍﻟْﺠَﺎﺭِ ﺫِﻱ ﺍﻟْﻘُﺮْﺑَﻰﻭَﺍﻟْﺠَﺎﺭِ ﺍﻟْﺠُﻨُﺐِ ﻭَﺍﻟﺼَّﺎﺣِﺐِ ﺑِﺎﻟْﺠَﻨْﺐِ ) [ﺍﻟﻨﺴﺎﺀ 36
Malamai suna cewa:
" Makwabtaci kala ukkune-3:
1-Makwabci Dan uwanka kuma musulmi.wannan kwabcin yana da hakki guda ukku-3
-Hakkin makwabci
-Hakkin Yan uwantaka
-Hakkin Musulunci.
2-Makwabci musulmi,wanda babu yan uwantaka ta jini. Wannnan yana da hakki guda biyu-2:
-Hakkin makwabci
-Hakkin Musulunci.
3-Kwabaci kafiri wanda babu yan uwantaka ta jini ko ta musulinci.wannan yana da hakki guda daya kadai-1
-Hakkin makwabci
Wadannan makwabta suna da Hakkin akan kowa da kowa wanda musulunci ya tsara,kuma wajibine kowa yayi kokarin sauke wannan hakkokin.
Mala'ika Jibrilu s.a.w bai gusheba yana jaddadawa wasiyya ga Annabi s.a.w akan Hakkin makwabci akan makwabci har sai da Annabi s a w yayi tsammanin makwabci zai iya gadon Dan uwansa makwabci.
ﻗَﺎﻝَ ﺭَﺳُﻮﻝُ ﺍﻟﻠَّﻪِﺻﻠﻰ ﺍﻟﻠﻪ ﻋﻠﻴﻪ ﻭﺳﻠﻢ : ﻣَﺎ ﺯَﺍﻝَ ﺟِﺒْﺮِﻳﻞُ ﻳُﻮﺻِﻴﻨِﻰ ﺑِﺎﻟْﺠَﺎﺭِ ﺣَﺘَّﻰ ﻇَﻨَﻨْﺖُ ﺃَﻧَّﻪُ ﺳَﻴُﻮَﺭِّﺛُﻪُ . ﺃَﺧْﺮَﺟَﻪُ ﺃﺣﻤﺪ 2/85 ( 5577 ) ﻭ "\ﺍﻟﺒُﺨَﺎﺭِﻱ "\ 8/12 (6015 ﻭ "\ ﻣﺴﻠﻢ "\ 8/37 (6
Saboda da wannan wasiyyane Annabi s.a.w ya sanya kyautatawa makwabci acikin alamar imani da cikar imani, sannan ya sanya mai kyautatawa makwabci shine mumini.
Annnabi s.a.w yana cewa:
(..........Duk wanda yayi imani da Allah da ranar lahira to ya kyautatawa makwabcinsa.........)
@ﺃﺧﺮﺟﻪ "\ ﺃﺣﻤﺪ "\ 4/31 (16484 ) ﻭ "\ ﺍﻟﺪﺍﺭِﻣِﻲ "\2036 ﻭ "\ ﻣﺴﻠﻢ "\ 1/50 ( 8
Annabi s.a.w ya kuma sanya imani yana samuwane cikin kyautatawa makwabci. Annabi yana cewa:
(imanin dayanku baya cika har sai ya soma makwabcinsa irin abinda take soma kansa).
Mai kyautatawa makwabcinsa shine mafi alkhairin mutane awajan Allah. Annabi s.a.w yana cewa:
(Mafi alkhairin aboki shine wanda yafi kyautatawa abokinsa,kuma mafi alkhairin makwabci shine wanda yafi kyautatawa makwabcinsa).
@ﺃﺧﺮﺟﻪ ﺃﺣﻤﺪ 2/167 (6566 ) ﻭ "\ ﺍﻟﺪﺍﺭِﻣِﻲ "\2437 ﻭ "\ﺍﻟﺒُﺨَﺎﺭِﻱ "\ ﻓﻲ "\ ﺍﻷﺩﺏ ﺍﻟﻤﻔﺮﺩ "\ 115 ﻭ"\ ﺍﻟﺘِّﺮﻣِﺬﻱ "\ 1944
Mu hadu a Darasi na biyu-2 insha Allah.
AZUMIN TASU'A DA ASHURA
Ashura itace ranar goma ga watan almuharram,yin azumi a wannan yini Sunna ce ta Manzon Allah SAW.
Manzon Allah S.A.W yana cewa:
*(Wanda yayi Azumin ranar Ashura, an yi masa gafara ta shekara daya)*
@صحيح لغيره : أصله عند مسلم، وسبق تخريجه، وهذه رواية الطبراني في ( الأوسط )
Manzon Allah S.A.W yace:
*(........ Yin azumin ranar Ashura, ina fatan Allah ya kankare zunubin shekarar da ta gabata sanadiyyar shi)*
@([15]) ــ رواه مسلم ( 1162 )، وأبو داود ( 2425 )، والترمذي ( 752 )، وابن ماجه (1730 )، وابن حبان ( 3632 ) .
Ƴan uwana masu albarka mu rabautu da azumtar wannan yini dan samu wannan falala mai girma da kuma koyi da Manzon Allah SAW.
Manzon Allah S.A.W ya kasance yana kirdadon wannan yini na Ashura dan ya azumci wannan yini, Abdullahi dan Abbas R.A yana cewa:
*_Babu wani yini da Manzon Allah SAW yake kirdadon yin azumi a cikin sa k**ar yinin Ashura indai ba azumin watan Ramadan ba_*
@رواه البخاري ( 2006 ).
AZUMIN TASU'A YANA HAƊE DA ASHURA
Sunnar Manzon Allah SAW shine ka azumci ranar Tara da goma watan Almuharram
Ibn Abbas R.A yana cewa:
"Manzon Allah SAW yayi azumin Ashura kuma yayi Umarni akan yinsa,sai aka ce ya Manzon Allah SAW ranar Ashura yini ne da Yahudawa suke girmama shi, sai Manzon Allah SAW yace:
*(Idan Allah ya raya mu zuwa shekara mai zuwa, zamu azumci ranar tara ga wata)* shekara bata dawo ba Manzon Allah SAW yana raye ba.
@ رواه مسلم ( 1134 ).
Hujjar yin azumin tara da goma gaba daya shine:
*_Manzon Allah SAW yayi Niyya tare da Azamar yin tara sannan goma ga wata idan Allah ya kai shi shekara mai zuwa,sai Allah ya karbi rayuwar sa kafin shekara ta dawo, sai wannan yake tabbatar da Allah ya raya Manzon Allah SAW da ya cika wannan niyyar tasa_*
@صحيح مسلم بشرح النووي ( 8 / 16 ) طـ ( مؤسسة قرطبة ).
Ibn Abbas R.A yana cewa:
*_ku azumci TASU'A da Ashura gaba daya, ku saɓawa yaduwa_*
@إسناده صحيح : رواه عبد الرزاق ( 7839 ) ، والبيهقي في ( الكبرى ) ( 8404 ).
Dan haka sunnar cikakkayi shine ka azumci tara da goma ga wata, *_tara da goma ga watan Almuharram a Nigeria zai kasance ranar LARABA DA ALHAMIS wanda yayi daidai da 18 da 19 ga watan August 2021_*
Allah ne mafi sani
AZKAR LOKACIN SAUKAR RUWAN SAMA
Akwai nau'in azkar guda Ukku da s**a tabbata a Sunnar Manzon Allah s.a.w ,wanda ake karantawa a lokacin saukar Ruwan sama
*1-Azkar kafin saukar ruwan Sama
Wato lokacin da Hadiri ya hadu kuma aka ga alamar saukar ruwa sai ace;-
*"ﺍﻟـﻠـﻬـﻢ ﺍﻏـﺜـﻨـﺎ"*
"ALLAHUMMA AGHITHNAA"
@ﺃﺑﻮ ﺩﺍﻭﺩ (1/303)[ﺑﺮﻗﻢ( 1169 )]،ﻭﺻﺤﺤﻪ ﺍﻷﻟﺒﺎﻧﻲ ﻓﻲ ﺻﺤﻴﺢ ﺃﺑﻮ ﺩﺍﻭﺩ( 1/216 )
*2-Azkar lokacin da ruwan yake tsakiyar sauka*.wato lokacin da ake ruwan sai a karata wannan;-
*ﺍﻟﻠﻬﻢ ﺍﺟـﻌـﻠـﻪ ﺻﻴﺒًﺎ ﻧﺎﻓﻌًﺎ*
"ALLAHUMMA JAHALHU SAYYIBAN NAFI'AN".
3-Azkar bayan an dauke ruwan sama.
Wato ana so bayan ruwan sama ya dauke sai mutum yace:
*ﻣﻄﺮﻧﺎ ﺑﻔﻀﻞ ﺍﻟﻠﻪ ﻭﺑﺮﺣﻤﺘﻪ*
"Mudhirnaa bi Fadhlil llahi warahma tihi".
Allah ka bamu damuna mai albarka.
SHINE MAFI GIRMAN HANYAR KANKARE ZUNUBI
Tuba shine dawowa daga sabon Allah da kyetara iyakokinsa tare da na dama akan abinda ya gabata na zunubai da komawa zuwa ga biyayya da dha'a zuwa ga Allah da kiyaye dokakinsa,kuma kayi hakan ne da ikhlasy tare da niyyar barin zunuban har abada.
Allah yana cewa:-
(وَمَن تَابَ وَعَمِلَ صَالِحًا فَإِنَّهُ يَتُوبُ إِلَى اللَّهِ مَتَابًا).
*(Kuma wanda ya tũba, kuma ya aikata aiki mai kyau, to, lalle ne sai ya tũba zuwa gaAllah).
@الفرقان(71)Al-Furqaan
Manzon Allah ﷺ yana cewa:
*(Yin nadama akan zunubi tubane,kuma wanda ya tuba daga zunubai k**ar wanda bai aikata zunubi bane)*
@الألباني - صحيح الجامع 6803
Ibn Taimiya RHA yana cewa:
*"Dan Adam yana samun kubuta daga laifukansa ya sami kankarar zunubansa ta daya daga cikin hanyoyi guda goma,na farko Tuba......)*
@مجموع الفتوي
Muna rokon Allah ya gafarta mana dukkan zunuban mu baki daya.
SUNNONIN MANZON ALLAH ﷺ GUDA ƊARI(100)
SUNNA TA UKKU-(3)
*_Yin Tasbihi da Akbari da Tahmidi lokacin kwanciya barci_*.
Wato faɗar:
SUBHANALLAH 33
WALHAMDULILLAH 33
WALLAHU AKBAR 34, lokacin da ka kwanta barci.
Daga Aliyu bin Abi Dhalib رضي الله عنه, yana mai cewa Lallai Manzon Allah صلى الله عليه وسلم ya faɗa, a lokacin da Nana Fadhimatu رضي الله عنها ta nemi ya bata mai yi mata Hidima saboda aiyukan gida sun yi mata yawa, sai yace:
*_(Shin bazan faɗan mu abin da yafi alkhairi fiye da mai yi maku hidima ba, idan kun zo kwanciya barcin ku, ko idan kun kwanta a wajan barcin ku, sai ku faɗi: ALLAHU AKBAR 34,SUBHANALLAH 33, ALHAMDULILLAHI 33,fadar wannan lokacin kwanciya barci ya fi alkhairi fiye da mai yi maku hidima da kuka nema)_*.
@متفق عليه: 6318 – 6915
Sayyadina Aliyu bn Abi Dhalib R.A yana cewa:
*"Ban taba kwanciya barci ba face sai na karanta wannan zikiri tun daga ranar da naji Manzon Allah SAW ya fada mana......."*.
@صحيح الجامع.
A cikin wannan Hadisi yana bayyana mana cewar, dukkan wanda ya lazamci yin waɗan nan Tasbihi lokacin kwanciya, zai sami sauki da rashin kunchi a rayuwar sa da yardar Allah, domin a hadisin a bayyana mana cewa Nana Fadhidma R.A ta koke ne ga Manzon Allah SAW akan wahalar da take sha na aiyukan gida, sai Manzon Allah SAW ya fadawa mata abin da zata aikaka domin samun saukin hakan
Allah ne mafi sani
SUNNONIN MANZON ALLAH ﷺ GUDA ƊARI(100)
SUNNA TA BIYU-(2)
*_Karanta surorin Qulhuwa, Faqi da Nasi lokacin kwanciya barci_*
Daga Nana A'isha رضي الله عنها, tana cewa:Manzon Allah صلى الله عليه وسلم ya kasance idan ya zo kwanciyar barcin sa a kowane dare yana haɗa hannunwansa guda biyu masu albarka, sai yayi tofi acikin su kuma sai ya karanta surorin, QULHUWA da FALAQI da NASI, sannan ya shafi abinda ya saukaka a jikin sa, yana fara shafawa daga kansa zuwa ƙasar jikin sa, yana aikita hakan sau uku
@رواه البخاري: 5017.
Malamai sun karawa juna sani akan shin za'a fara karantarwa ne sannan ayi tofi, ko kuma ka fara tofi sannan ka karanta??
Ibn Uthaimeen رحمه الله yana cewa:
"Wannan al'amari ne mai fadi, ko ka fara tofi sannan ko karanta ka shafa, ko ka fara karantarwa sannan kayi tofi sannan ka shafa, duk wanda kayi kayi daidai".
*"Zahirin Hadisin yana nuni akan sai ka fara tofi sannan ka karanta, sai dai yadda al'amarin yake kowanne ka fara yayi daidai"*
@لقاء الباب المفتوح" لقاء رقم (139) .
Allah ne mafi sani
IDI A MUSULUNCI
Fitowa ta Uku-(3)
*_Daga Hukunce-Hukuncen Idi_*
1-An karhanta sallar nafila kafin sallar idi da bayanta, sai dai in a masallaci za a yi ta, to sai a yi gaisuwar masallaci idan an shiga
2-Sunna ne idan sallar idi ta wuce,ko wani ɓangarenta ya kubce wa mutum, ya ramata k**ar yadda take, ya sallace ta raka’a biyu da kabbarorinta, haka ma abin da ya rasa daga cikinta ya rama shi k**ar yadda take.
3-Allah Maɗaukakin Sarki ya shar’anta wa bayinsa a qarshen Ramadan su yi masa kabbara, Allah ya ce:
*{Don ku cika adadin kwanakin (Azumi) kuma don ku yi wa Allah kabbara a kan abin da ya shiryar da ku} *
-baqrah : 185.
Ma’anar ku yi wa Allah kabbara shi ne, ku girmama shi a cikin zukatanku da harsunanku.
Lafazin kabbarar shi ne : *_Allahu Akbarul Lahu Akbar, La’ilaha Illal Lahu, Wal Lahu Akbar, Allahu Akbar, Walillahil Hamdu_*.
4-Sunna ne maza su ɗaga muryarsu da waɗannan kabbarori, mata kuwa za su ɓoye, saboda an umarci mace ta sassauta muryarta.
5-Zai fara kabbarar idi tun daga faɗuwar ranar daren idin, idan ya san da shigowar wata kafin faɗuwar rana, k**ar a ce mutane sun cika azumi kwana talatin, ko an ga jinjirin watan Shawwal.
Zai dakata da kabbara idan mutane sun fara sallar idi. *_Da babbar salla zai fara kabbara ne tun daga bayan sallar asubar ranar Arafa, zuwa sallar la’asar ɗin kwana ukun yanyane, daga ranar arfa zuwa ranar 13 ga wata_*
*_Faɗakarwa_*
1-Ana son musulmi su yi wa junansu murnar idi.
2-Ana son bayyana farin ciki da idi, da yi wa ‹yan uwa da masoya da makusanta murna.
3-Idi wata dama ce da ya wajaba a ribace ta don sada zumuncin da aka yanke, da sulhunta wa tsakanin masu husuma.
4-Ba shar’anta ziyarar maqabarta ba a ranar idi, don hakan ya saɓawa farin cikin da annashuwar cikin idi.
5-An shar’anta yalwata wa iyali da tufafi da abinci da kayan cin daɗi, waɗanda Allah ya halatta, a ranar idi, saboda idi kwanaki ne na farin ciki da annashuwa.
Allah ya ce, “Ka ce da falalar Allah da rahamarsa ku yi farin ciki, shi ne ya fi alheri a kan abin da suke tarawa”. (Yunus : 58)
Allah ne mafi sani
BAYANI AKAN LAYYA
Fitowa ta Uku-(3)
*_Aibin Dabbobin Layya_*
1-Aibin da yake hana a yi layya da dabba
*Mai ido ɗaya*
wadda idon ɗaya yake da aibi, wadda ba ta gani ta shiga, kuma hakan ya bayyana a fili.
*Gurguwa wadda bata iya tafiya*
*Ramammiya, ita ce wadda bata da kitse*
*Mara lafiyar da rashin lafiyarta ta bayyana*.
Dalilin haka shi ne hadisin Bara’u ɗan Azib – Allah ya yarda da shi – ya ce, Manzon Allah ( صلى الله عليه وسلم ) ya ce:
*(Layya bata halatta da dabba mai ido ɗaya, wadda rashin idon ɗayan ya bayyana, da gurguwar da ɗingishinta ya bayyana, da maras lafiya wadda rashin lafiyar ya bayyana, da ramammiya wadda bata da mai)* Wannan hukunci ya haɗa da duk wani aibi irin wannan ko wanda ya fi shi”
ne ya rawaito shi.
2-Aibin Da Baya Hana Layya
*Dabbar da bata da jela*
*Dabbar da bata da qaho*
*Dabbar da aka fiɗiye
*_Faɗakarwa_* :
Duk abin da aka ambata dangane da layya,na abin da yake isar wa da wanda baya isar wa,haka abin yake a wajen hadaya da fansa.
*_Raba Naman Layya_*
An shar’anta wa mai layya ya ci kashi ɗaya bisa uku na layyarsa, ya yi kyauta da kashi ɗaya, ya yi sadaka da kashi ɗayan, ya halatta ya yi sadaka da layyar gabaɗaya, in kuma ya ci mafi yawanta to ya halatta, babu komai
*_Faxakarwa - 2_*
1-Ya k**ata mai layya da hadaya ya yi qoqarin amfanuwa da naman kada ya watsar da shi a banza, k**ar yadda wasu alhazai suke yi, s**an yanka hadayar su barta a wurin yankan ba tare da fiɗa ba ko yanyankawa ba, ba wanda zai amfanu da shi.
2-Wanda duk ya yi niyyar layya to kada ya rage gashin kansa, kada yanke farcensa ko fatarsa, idan watan zul-hajji ya shigo, har sai ya yanka layyarsa, saboda hadisin Ummu Salamata – Allah ya yarda da ita – ta ce, Manzon Allah ( صلى الله عليه وسلم ) ya ce:
*(idan goman farko ta watan zulhajji ta shigo, kuma ɗayanku ya yi niyyar yin layya, to kada ya taɓa komai daga jikin gashinsa ko fatarsa) *
ne ya rawaito shi.
Amma wanda yi masa layya za a yi, k**ar iyalai, ‘ya’ya, to waɗannan ba a haramta musu rage komai ba.
Dabbar da take da tsaga a kunne ko qahonta ya karye
Allah ne mafi sani
IDI A MUSULUNCI
Fitowa ta biyu-(2)
*_Yadda Ake Sallar Idi Biyu_*
Sallar idi raka’a biyu ce, ba a kiran sallah, ba a yin iqama, ana bayyana karatu a cikinsu, ga yadda ake yin su :
*1-Raka’ar farko Liman zai yi kabbara bakwai, bayan ya yi kabbarar harama, ya yi addu’ar buɗe sallah, kafin ya yi A’azu ya fara karatu*.
*2-Bayan ya yi A’uzu ya yi bismillah, sai ya karanta fatiha da sura bayanta. Sunna ne ya karanta suratul *‹A’ala a raka’ar farko bayan ya yi fatiha, ya karanta suratul Gashiyah a raka’a ta biyu, ko kuma suratu Qaf a raka’ar farko, suratul Qamar a raka’a ta biyu*.
*3-Zai yi kabbara biyar a raka’a ta biyu, bayan kabbarar ɗagowa. Zai ɗaga hannayensa a kowace kabbara*
4-Zai godewa Allah, ya yabe shi, ya yi salati ga Annabi *( صلى الله عليه وسلم )*a tsakanin kabbarori
*5-Idan ya yi sallama, sai ya hau minbari, ya yi huɗuba biyu, ya zauna ɗan kaɗan a tsakaninsu. Zai buɗe huɗubar farko da kabbarori tara, ta biyu da kabbara bakwai*.
6-Mustahabbi ne a sallar qaramar sallah ya tunatar da mutane hukunce-hukuncen zakkar fidda kai, a babbar sallah kuma hukunce-hukuncen layya.
*_Wurin Da Ake Sallar Idi Biyu_*
A sunna dai shi ne a yi sallar idi a filin sallah ba a masallaci ba,in akwai buqata aka sallace ta a masallaci to babu laifi.
*_Abubuwan Da Ake So A Idi_*
1-Maza su yi ado da kyawawan kayansu,mata kuwa su fita sallah ba tare da ado da turare ba.
2-Mamu su sammakon zuwa, su shiga sahun farko
3-Ya tafi da wata hanya, ya dawo ta wata hanyar daban, a kan qafafunsa – in zai iya -. An karɓo daga Jabir – Allah ya yarda da shi – ya ce, *(Manzon Allah ya kasance ranar idi, yana canza hanya) *
ne ya rawaito shi.
4-Ya ci dabino uku ko biyar kafin ya fita sallar qaramar sallah. Amma a babbar sallah kada ya ci komai har sai ya dawo.
5-Ana son a ɗan jinkirta sallah idin qaramar sallah, saboda musulmi ya samu damar bayar da zakkar fidda kai, ta isa zuwa waɗanda s**a cancance ta. Amma babbar sallah ita ana so a yi ta da wuri.
Allah ne mafi sani
Click here to claim your Sponsored Listing.
Location
Category
Website
Address
Kano