Clip 1
Darul Qadiriyya riyadul jannah
Dan Neman Karin bayani KO bada shawara
25/04/2026
Alhamdulillah!
Malam dai ya hannata case a hannun wannan lauya da Kotu ta bashi shawarar ya hannatawa mutum ne me Amana sai yan makaranta a shagala da ruwan Hasbunallahu wani'imal wakilu da cigaba da kaiwa Allah kuka.
25/04/2026
23/04/2026
Shari’ar Sheikh Abduljabbar: Kotu Ta Kori Ɗaukaka Ƙara, Ta Mayar Da Maganar Gaban Babban Alƙalin Jihar Kano (Chief Judge)
Aliyu Samba
Babbar Kotun Ɗaukaka Ƙara da ke Kano, ƙarƙashin jagorancin alƙalai uku, Mai shari’a Mohammed Lawal-Shuaibu, tare da Mai shari’a Abubakar Mu’azu-Lamido da kuma Mai shari’a Ahmad Ramat-Mohammed, ta umarci a mayar da shari’ar Malam Abduljabbar Nasiru Kabara gaban Babban Alƙalin Jihar Kano (Chief Judge) domin sake duba ta bisa ƙa’ida, bayan gano kura-kurai a takardun da aka shigar.
A zaman kotun na ranar Alhamis, an tafka muhawara mai zafi tsakanin malamin, wanda ya bayyana cewa zai kare kansa da kansa, da kuma lauyoyin gwamnati.
Sheikh Malam Abduljabbar ya roƙi kotun da kada a mayar da shi gidan gyaran hali na Kuje da ke Abuja, inda ya yi zargin cewa rayuwarsa tana cikin haɗari a can. Haka kuma, malamin ya nuna shakku kan takardun da aka kai masa gidan yari, inda ya zargi cewa lauya ne ya kai masa maimakon ɗan aiken kotu.
Sai dai kotun ta tabbatar masa da cewa wanda ya kai takardar ɗan aikenta ne na halal, ba lauya ba.
Lauyoyin Gwamnatin Jihar Kano, Barista Bashir Sale da Barista I.A. Garba, sun buƙaci kotun da ta kori ɗaukaka ƙarar malamin baki ɗaya. Sun hujjatar da cewa an shigar da ƙarar ne ba tare da bin ƙa’idojin shari’a ba, don haka babu dalilin ci gaba da sauraron ta.
Ita ma kotun, bayan bincike, ta amince cewa takardun da duka ɓangarorin biyu s**a shigar ba su tafi daidai da tanadin doka ba.
Kotun ta tunatar da Malam Abduljabbar cewa wannan kotu ce ta ɗaukaka ƙara, ba kotun da aka yi masa shari’a a baya ba. Alƙalan sun bayyana cewa Har yanzu akwai sauran shari’a a gaban kotun ƙasa wadda ba a sanya ranar ci gaba da ita ba. Sannan Akwai bayanan cewa wani lauya, Barista Adamu Abubakar, ya riga ya shigar da ƙara a madadin malamin a kotun ƙasa.
Kotun ta nanata wa malamin cewa doka ta ba shi damar neman lauya, kuma idan ba shi da hali, gwamnati tana da nauyin samar masa da lauyan da zai kare shi saboda nauyin shari'ar.
Bayan duka ɓangarorin biyu sun amince cewa a koma kotun ƙasa domin yin gyara, kotun ɗaukaka ƙarar ta yanke shawarar mayar da maganar gaban Babban Alƙalin Jihar Kano. Kotun ta bayyana cewa tun da babu wani takamaiman hukunci da aka riga aka yanke a yanzu, kuma takardun kowa na ɗauke da kuskure, gara a bi hanyar da doka ta tanada domin yi wa kowa adalci.
Wannan mataki ya kawo ƙarshen zaman na yau, yayin da ake jiran mataki na gaba daga ofishin Babban Alƙalin Jihar.
Allah ya tsare gabanku da bayanku, Allah ya tsare damanku da hauninku, Allah ya tsare mutuncinku, Allah ya cigaba da kubanceku da sirrin HASBUNALLAHU WA NI'IMAL WAKEELU, Ubangiji ya dami damuwarku, ya tabar, ya rushe magautanku, ya kara muku galaba, nasara da rinjaye, ya karfafeku da kudurarsa, Alfarmar Sayyidatu Nisa'il Alameena da Abbanta SAWW
Alhamdulillah!
Kotu tayi umarnin a kawo malam gabanta ranar Alhamis 23/04/2026.
A yayin cigaba da shari'ar Sheikh Abduljabbar kabara yau jami'in tsaro sun cika harabar court of Appeal Kano Division
19/04/2026
Gobe idan Allah ya kaimu court of Appeal Kano Division dake Audu bako sakateriya zata zauna zaman sauraran Case din Maulana Amirul wa'izina (H).
Allah ya jiyar damu alkairi yasa karshen case din kenan.
07/04/2026
Takai taccen sakon Dr abduljabbar na yau
Sheikh Abduljabbar Ya Shigar Da Sabon Korafi Gaban Kotun Daukaka Kara
Fitaccen malamin nan na birnin Kano, Sheikh Abduljabbar Sheikh Nasir Kabara, wanda ke tsare a gidan gyaran hali na Kuje da ke Abuja, ya sake mika wata sabuwar takardar korafi zuwa ga Kotun Daukaka Kara da ke zamanta a Kano (Kano Division).
Malamin ya shigar da wannan korafi ne sakamakon wani sako da ya ce ya samu daga hannun Shugaban Sashin Shari’a (H.O.D Litigation) na kotun ta wayar tarho a ranar 31 ga watan Maris, 2026, inda aka sanar da shi cewa kotun za ta aika masa da sanarwar ranar zama (Hearing Notice).
Abubuwan Da Takardar Ke Kunsa
A cikin takardar mai shafuka biyar, wadda wakilan kwamitin shaidunsa (Eye-witnesses committee) s**a mika wa kotun a ranar Talata, 7 ga Afrilu, 2026, Sheikh Abduljabbar ya bayyana damuwarsa kan yadda shari’ar ke tafiya.
Manyan korafe-korafensa sun hada da:
• Batun Sauya Kurkuku: Malamin ya koka kan yadda aka canja masa wurin tsarewa daga Kurmawa da ke Kano zuwa Kuje da ke Abuja a ranar 14 ga Oktoba, 2025, ba tare da barinsa ya kwashi muhimman takardunsa na shari’a ba.
• Rashin Takardun Shari'a: Ya bayyana cewa ya shafe watanni biyar bai san halin da takardunsa suke ciki ba, kuma mahukuntan gidan yarin ba su ba shi damar duba su ba yayin da ake shirin mayar da shi Abuja.
• Hakin Kare Kai: Ya dogara da sashi na 36 (6) na Kundin Tsarin Mulkin Najeriya na shekarar 1999 (kamar yadda aka yi wa gyara), wajen neman kotu ta ba shi damar tsayawa ya kare kansa da kansa.
Bukatun Sheikh Abduljabbar
Daga karshe, malamin ya bukaci Kotun Daukaka Kara da ta amince masa da abubuwa guda uku kafin a ci gaba da sauraron karar:
• A mayar da shi gidan gyaran hali na Kurmawa da ke Kano domin ya tantance halin da takardunsa suke ciki.
• Idan an samu wasu daga cikin takardun sun bace ko an sauya su, a ba shi damar maido da su yadda suke.
• Sai ya tabbatar da cewa takardunsa suna nan daram, sannan kotu ta ba shi sanarwar ranar zama (Hearing Notice) da kuma takardar sammaci (Warrant) na halartar zaman kotun don gabatar da hujjojinsa (Adoption).
Sheikh Abduljabbar ya karkare takardar tasa da cewa tunda aka tsare shi a ranar 16 ga Yuli, 2021, bai taba aikata wani laifi ba, kuma yana rokon kotun da ta duba lamarinsa cikin adalci.
Ya zuwa lokacin hada wannan rahoton, kotun ba ta riga ta ba da wata sanarwa a kan wannan sabon korafi ba
03/04/2026
Allah muna rokon ka da sirrin da Annabi Yunusa ya rokeka dashi kai masa ɗauki a yayin da yake cikin kifi.
Allah muna rokon ka da kalmomin da Annabi Ayuba ya rokeka dasu kai masa ɗauki a sanda yake fama da jinya.
Allah muna rokon ka da kalmomin da Annabi Musa ya rokeka dasu kai masa lamunin abunda ba kowa kaiwa ba.
Allah muna rokonka da sirrin da Annabi S.A.W ya kira dasu ka kubance shi da kariya daga cutarwa mutane.
Allah kaiwa bawan ka ɗauki ka yaye mana wannan jarabawa a kusa ka kubutar mana dashi cikin izza da madaukakiyar ɗaukaka tare da tabbaciyar nasara.
Allah mun tashi da kewar bawan ka da bakin cikin zaluncin da mahukuntar Kasar nan ke gwada masa Allah babu wani karfi a saman naka babu wani mulki a saman naka babu wata buwaya a saman taka babu wata cika da kasaita bayan taka Allah kai ka kasance kafin komai kuma kai kaɗai zaka wanzu bayan komai Allah muna kawo karar duk wani azzalumi wajen ka.
Allah ka gwada musu kaine Allah me yadda yaso a sanda yaso Allah ka hana bukatarsu biya ka saukar musu da bala'i da musibun da zai tafi da mulkin su ka jefa su cikin razani da bakin cikin da zasu gwammace mutuwar su Allah gaka ga masu mulkin kano da Najeriya 🤲🙏🥺
Click here to claim your Sponsored Listing.
Location
Category
Contact the school
Telephone
Website
Address
Kano