07/09/2025
Abubuwa guda 4 da zasu faru idan mata s**a daina hakuri da talaucin mazajensu
1) tausayin mata zai futa daga zuciyar mazajensu, mata zasu daina samun tarairaya da kulawa daga mazajensu. Domin idan namiji yasan matarsa bata tausaya masa shima bazai tausaya mata ba.
2) Zubewar kima da mutunci. Kimar mace na zibewa agun namiji yayinda ya fahimci matarsa bata mutunta abinda ya kawo mata na rayuwar yau da kullun.
3) Ficewa a rai. Mace na fita aran namiji ya fara tinanin sake auren wata, koda bashi da kudin sake auren, a tinaninsa ko zai dace da mai hakuri.
4) Idan mazan da basu da aure s**a fahimci mata basa hakuri da talaucin mazajensu, kamar yadda s**anji masu magana nacewa " ABU BIYU BASA ZAMA WAJE DAYA " wato "MACE DA BABU" to zasu daina shaawar yin auren har sai sun samu kudi. Sannan wannan zaisa mata sudaina samun masu aurensu.To daganan sai zinace zinace suyi yawa. Shikkenan alumma ta lalace.
Kusani mata hakurin da Allah ya ce kuyi yana da muhimmanci wajen inganta Alumma baki daya.
Nura Mustapha