15/06/2026
😭😭INNA LILLAHI WA INNA ILAIHI RAJI’UN
Waɗannan su ne fuskokin wasu daga cikin al’ummar ƙaramar hukumar Dandume Jihar Katsina da s**a rasa rayukansu sakamakon hare-haren ‘yan bindiga.
A ranar Asabar, 13/06/2026, al’ummar Dandume sun wayi gari cikin alhini, jimami da baƙin ciki sakamakon wannan mummunan lamari da ya yi sanadiyyar salwantar rayukan bayin Allah marasa laifi.
Mutuwar su babban rashi ne ga iyalansu, abokan arzikinsu da kuma daukacin al’ummar Dandume. Zukata sun yi nauyi, idanu sun cika da hawaye, yayin da aka rasa mutane waɗanda s**a fito neman halaliyarsu da kula da iyalansu.
Ba abin da ya fi ciwo kamar ganin rayukan bayin Allah suna salwanta ba tare da wani laifi ba. Wannan lamari ya sake barin tabo mai zurfi a zukatan jama’a tare da ƙara tunatar da mu cewa rayuwa amana ce daga Allah, kuma kowane rai mai ɗanɗanar mutuwa ne.
Muna roƙon Allah Maɗaukakin Sarki Ya jiƙan waɗanda s**a rasu, Ya gafarta musu kura-kuransu, Ya sanya Aljannatul Firdausi ta zama makomarsu. Allah Ya ba iyalansu haƙurin jure wannan babban rashi, Ya kuma kawo ƙarshen matsalar tsaro da ke addabar al’ummarmu.
Allah Ya jiƙan su baki ɗaya, Ya sa ƙarshen wahalarsu hutu ne, Ya kuma kare sauran al’umma daga irin wannan masifa. Amin. 🤲🏽💔😭