22/07/2024
Zanga zangar ta Sha banban da wacce aka Saba gudanarwa a shekurun baya.
An yi tsarin cewa mutane zasu fito ne daga unguwanninsu sa'an nan su dunguma zawa gidajen duk wanda aka San ya taba taka wani matakin a hukumance tin daga matakin kansila har zuwa gwamna, mutane zasu tisa keyarsu ya kasance sune gaba gaba wajen jagorantar zanga zangar.
Sannan zanga zangar ba irin ta zuwa gidan gwamnati bace gwamna ko wani sakataran gwamnati ya fito yayiwa jama'a wani jawabi a watse, A'a za'a cigaba da zama Daram ne har se anga abin da ya torewa bozo nadi.
Sannan an bukaci ga duk wanda Allah ya horewa da ko biskit, ruwa, abinci, cincin,kulikuli, tabarmin sallah da ruwan alwala,
da duk wani nau'in Abu da ze karfafa guwwar Jama'a da ze hanasu gajiyawa.
Haka zalika an bukaci mutane da su kawar da tsoro da munafurci a zukatansu sa'an nan su nuna da'a da sanin yakamata.
04/04/2024
Muna kira da babbar murya ga shugabanci hukumar bayar da tallafin karatu ta jahar Kano state scholarship board.
A gaggauta daukan mataki akan wani Dan luwadi ma'aikacin hukumar me matakin staff officer,
Saboda korafe korafe sun fara yawa a tsakan kannin dalibai.
09/02/2023
Zan tilassawa Gwamna ya daure ya karasa biyan dalibai kudadensu na Scholarship, saboda yaran nan sun sha bakar wahala wajen neman tallafin nan ga kudinsu da s**a kashe wajen siyan fom da cikewa ta hanyar internet.
Nasiru Yusuf Gawuna.
03/02/2023
Ni da kaina ba zan iya tunkarar Gwamna ba da maganar Scholarships ba, musamman kan daliban da suke cikin masarauta kano.
Gwamna da kansa ya tabbatar mini da cewa har yanzu yana jin zafin abin da yan birni s**a jaza masa a zaben shekara ta 2019 wanda ya harfar da INCONCLUSIVE. Makusancin gwamnan ya bawa daliban shawarar suje su sami matar gwamna ko mataimakin gwamna Nasiru yusuf Gawuna.
20/10/2022
Matsalar Inconculusive da ta gabata a zaben 2019 ta haifarwa da daliban wasu kananan hukumomi cikas wajan cin gajiyar tallafin karatu a jahar kano.
Dalibai suna zargin ramuwar gayyaya gwamnatin jahar kano ta shirya ramawa akan daliban wasu daga cikin kananan hukumomin da gwamnatin ta kasa kai bantanra a zaben 2019 da ya gabata.
16/08/2022
Dan Allah Don Annabi. Gwamna Dr Kadumul islam ka bawa hukumar bayar da tallafin karatu damar biyan daliban da suke karatu a wajen kano a tura musu kudinsu ta Bank account, saboda akwai matsala, dayawa akwai daliban da yan asalin jahar kano ne amma zama ya kai iyayensu wasu jahohin, dayawa wasu bazasu samu damar zuwa wannan sabon tsarin na sikirini din kananan hukumomi ba, sabida akwai matsalar tsaro ba kowane uba ne zai kyale Dansa yazo kano sikirinin ba sannan ya kara dawuwa karbar kudinsa ba, nawa dalibi ze kashe kudin mota, nawa ya kashe wajen neman scholarships, duk da cewa Gwamna ya kara kaso hamsin 50 amma duk da haka idan ka yi la'akari da abin da za'a bawa dalibi zaka ga cewa an wahalar dasu.
Dan Allah a taimaka musu.
08/07/2022
DA DUMI DUMINSA....... Gwamnatin kano ta soke biyan kudin tallafin karatun dalibai da suke karatu a jamo'o'in kasar nan da kwalejoji da sauran makarantu da gwamnati ta ke biya a shekarun baya.
Matakin ya biyo bayan kokawa da gwamnati ta yi kan matsalolin kudi da rashin nagartar dalibai da suke karatu a makarantu jahar da sauran jahohin kasar nan.
14/05/2022
A gaggauta hukunta daliban da s**a kashe Deborah dalibar da ta zagi Annabi.(S A W)
Ba daidai bane mutane su dinga daukar doka a hannunsu, wannan ya sabawa ko wacce irin shari'a, saboda haka ya zama dole gwamnatin jahar Sokoto ta binciko su a hukunta su. Ba zai yu a cigaba da zaman ci barka tai ba.
10/04/2022
Dalibai 'yan asalin jahar Kano sun yi danasanin bata lokacin su akan neman tallafin karatu a gwamnatin Ganduje.
Wasu dalibai sun shaidawa majiyar mu cewa tun da fari se da wasu dalibai da s**a kammala karatu s**a gargade su akan kada su kuskura su sa kudinsu dumin siyan fom din neman tallafin karatu a wannan gwamnatin ta Baba GANDUJE duk da cewa alokacin mulkinsa an samu wata jajirtacciyar shugaba farfesa Fatima tasa ya biya zangon karatu na 1 dana 2 a wancan lokacin duk da cewa shima ba kowanne dalibai aka biya ba.
Muna fatan gwamnati zata dobi wadannan dalibai da idon tausayi ta biyasu kamar yadda gwamnatin ta fara yi a farkon mulkin ta.
25/01/2022
Masha Allah. .
SANARWA ! SANARWA! SANARWA.
Duk dalibin da yasan bank account dinda yayi bacci yaje ya tashe shi, wanda bashi da account yaje ya bude ya gaggauta kaiwa scholarships.
Mai girma Dr. Abdullahi Umar Ganduje kadimul Islam, ze fara biyan dalibai tallafin karatu a karshen wannan wata janeru shekarar 2022.