Sirrinmune MATA ADON GARI

Sirrinmune MATA ADON GARI

Share

Contact information, map and directions, contact form, opening hours, services, ratings, photos, videos and announcements from Sirrinmune MATA ADON GARI, Tutor/Teacher, Kaduna.

31/01/2018

Shin a ina matsalar rikichi sakani kishiyoyi yakene?
Daga matanne ko mazan?

24/01/2018

Wai mai nene sirrin maza suna tsoron yin aure amma daga sunyi sai kwadayin qarin aure
maike kawo haka?

21/12/2017

Mata bayin Allah idan kaji malami yana wa'azi saide kaji laifukan mata kulawa da miji iya kwalliya iya taku da sauransu
ni anan tambayata wai su mata basu da hokkokinsune akan mazajensu ne?
Maiyasa malamai s**afi nuna matsalar mata su boye na maza kode sun fiye sa'ido wa matane?
Gaskiya akoi abun dubawafa
mai ra'ayinku yan'uwana?

05/08/2017

===>MUGUWAR KISHIYA PART 4 ==>Aisha tana ja da baya, shikuwa abdul yana kara kusantar ta hardai taje karshen bangon daki, abdul yayo kanta gadan- gadan, Aisha tana dubawa gefanta taga wukar da umma take amfani da ita, batayi wata-wata ba ta dasa hannu ta dauko wukar nan ta nuna abdul da ita, tace kada kamatso wallahi zan caka maka wukar nan, wanda tuni idonsa ya rufe yayo kan Aisha, ita kuwa batasan sanda ta labta masa wukar nan akai ba, abdul ya kwalla kara a zube akasa, amarya da fatima s**a jiyo karar abdul su taho aguje, ita kuwa Aisha tuni ta rude sakamakon ganin yadda jini ke zuba daga kan abdul, su amarya s**a karaso suna zuwa s**aga Aisha rike da wuka a hannu, basuyi jinkirin kiran abba ba tare da daukar abdul zuwa asibiti, Bayan sun karasa asibiti ne, likita ya fara duba abdul, su amarya da fatima suna zaune sunyi tagumi, alhaji ya shigo arude, ya nufi wajen likita, yace likita yajikin nasa likita yace da sauki, domin yanxu anyi masa duk abinda ya dace saboda haka zaku iya komawa dashi, alhaji yabiya kudin komai, sannan yadauko su a motarsa yana tafiya yana xage- xage akan Aisha, Amarya tana kara xuga shi, Ita kuwa Aisha tuni hankalinta yagama tashi domin sanin abinda zai biyo baya, tayo waje domin barin gidan kafin abba yadawo, tana zuwa kofa s**ai karo da umma, umma tace lapiya Aisha? Aisha ta fada mata duk abinda ya faru' don haka umma tayi saurin bawa Aisha kudin mota, umma tace kiyi sauri kitafi gidansu kaka idan abin ya lafa saiki dawo, Aisha tace to umma, aiko min da kayana na makaranta, umma tace to, Aisha tayi waje, kana ganinta kasan arude take, Umma tana zaune tayi tagumi, taji shigowar su alhaji ko sallama babu sai masifa yake, yashigo dakin umma yatsaya akanta, yafara magana cikin fushi, Ke ina wannan "yar iskar yar taki? Maganar tayiwa umma xafi matuka, hakan yasa mikewa cikin fushi, tace alhaji duk abinda zakai kada ka kara kiran "yata "yar iska, ga "yan iska nan kana tare dasu wannan yaron yayi kokarin yiwa "yarka fyade amma kuma sai gashi kai kake kare......... Saukar mari umma taji a fuskar ta, tana dubawa taga amarya ce ta zabga mata mari, itama batayi wata- wata ba ta daga hannu ta sharara mata mari, abba dake tsaye yana kallo tuni shima ya daga hannu zabgawa umma mari wanda sai da ya tilastawa umma dafe kumatu, umma ta fashe da kuka mai tsanani wanda duk wanda yaji dole ya tausaya mata, alhaji ya kara da cewa kuma idona idan Aisha sai na karya ta, s**a juya s**a fice daga dakin s**a bar umma tana kukan bakin ciki, Aisha bata tsaya ko ina ba sai gidan kakanninta ta fada musu duk abinda yafaru, hakan yasa kakanta yace gaskiya abin nashi cigaba yake don haka bari naje wajen malam nasanar dashi abinda yafaru, Bayan dare yayi amarya da abba suna zaune, abba yana ta lallashin amarya amma taki, sai abba yace kifadi abinda k**e so nayi miki komai wahalarsa don ki daina fushin nan, amarya tayi murmushi da alama taji dadin maganar abba, sannan tace ni abu hudu nakeso, alhaji yace fade su duka indai kudi ke yinsu kamar angama ne, amarya tace 1 inaso kadawo min da yan uwana mutum takwas gidan nan da zama 2 inaso ka cika min alkawarina na motar da kace xaka sai min 3 inaso mufita kasar waje shakatawa, na hudun kuma baxan fada ba sai mun dawo daga shakatawa,abba yace wannan duk mai sauki ne indai zaki huce, don haka gobe zan tura driver ya dauko "yan uwan naki, mota kuma muna dawowa xaki ganta, don haka wace kasa. K**e so mu tafi? Amarya tace maleyshia, abba yace to kada kidamu tawan, farin ciki ya lullube ta, Abba ya gama shirin tafiya maleyshia shida amaryarsa gida kuma ya cika da "yan uwan amarya, wanda yanxu su goma ne tara daga ciki dukkansu maza ne majiya karfi daya ce mace wato fatima, sai sharholiyar su suke kamar gidan ubansu, umma kuma bata da damar sakewa haka umma tayi ta hakuri tana lissafin dawowar danta Samar wanda kullum takeyiwa addu'a, Yaune ranar tafiyarsu abba da amarya maleyshia don haka ya tara kowa nagidan, yafara jawabi

kijira danji a gaba

16/07/2017

Shin ko make sa mace idan tanason wani saurayi ko bazawari sai ta kasa furta mar?
Maike kawo hakan kuma mai shawara ko dabara na warware wayannan matsalolin?

01/07/2017

Wata masifa da janyowa al'ummomin mu ayau shine yaduwar qungiyoyin .
Yanzu irin wadannan qungiyoyin suna nan suna da yaduwa a al'ummomin mu kamar wutar daji. Musamman ma a jihohin mu na Arewa.
Abun ya kai daga Lagos, wata maccen zata iya turo da ticket din jirgi wa wata yarinyar a kaduna domin ta same ta saboda ayi madigo da ita.
Daga Abuja wata zata iya aikawa wata yarinyar ticket na jirgi ta taso daga Sokoto saboda ayi madigo da ita.
Kuma wani abun ban haushi, mafi-aksari matan manya su s**a daure wa abun gindi. Kamar matan gwamnoni, da matan sanatoci, da matan ministoci, da matan manyan ma'aikatan gwamnati a Abuja da sauran jahohi. Dalili shine, mazajen su basu da lokacin su.
Domin wata matar sai tayi wata shidda bata samu mijin nata ba. Gashi ta qoshi, ga security ta koina, saboda haka ya zata yi ta biya buqatar ta? Sai kaga ta shiga harkar madigo. Ta fara da wadanda suke kusa da ita, sannu ahankali har ta fada cikin irin wadannan qungiyoyin na 'yan madigo.
Sai kaga wata qaramar yarinya taje zata ga matar wani gwamna koh matar wani babban mutum, amma idan ka bincika sai ka samu madigo ya kai ta. Idan aka gama a bata kudi, da turamen zannuwa masu tsada, a siya mata jakar ratayawa kamar ta kimanin dubu hamsin koh ma fiye, da takalma masu tsada, wadanda zata koma cikin qawayen ta ta dinga tada qura.
Sai kaga macce idan mijin ta yayi tafiya, babu abunda zata yi sedai ta shiga group dinsu na WhatsApp koh makamancin sa, ta samu wata yarinya wadda tayi mata, ta fada mata toh fa yau Maigidan baya nan, saboda tana buqatar tazo ta taya ta kwana a madadin shi.
Akwai matar da aka bani labarin cewa idan mijin ta baya gidan, sama da mata goma zata gayyato su taya ta kwana a gidan. Kuma ba wani abu ake yi ba illa wannan tsiyar. Haka zasu yita gurnani sai kace an cika daki da raguna.
Allah ka raba al'ummar mu da wannan bala'in.
Abun ya zama kamar ado. Saboda haka Iyaye, idan kuka ga yarinyar ku da wata yarinyar sun shaqu, basa rabuwa. Kuma ba Qur'ani koh Sunnah ta hada su ba, toh ku bincika kuga me yake faruwa!
Akwai wani Magidanci da yake da mata biyu ashe duk 'yan madigo ne bai sani ba. Ranar nan ya dawo daga tafiya sai ya leqa dakin ta farkon ya samu bata nan. Yana leqawa dakin ta biyun sai ya same su tsirara suna madigo tare.
Shi a da yana ta murna da buga qirji cewa gidan shi lafiya lau ba'a taba fada ba. Da zarar ana maganar matan sai kaji yana cewa 'Wallahi yadda kasan uwa dai uba dai haka matan nan suke' ashe bai sani ba uwar da uban madigo kenan.
Akwai wata yarinya da take karatu a Danfodio university sokoto, wata rana take fada mun cewa taje wajen wata qawar ta, ashe bata sani ba qawar 'yar madigo ce, kuma ta gayyato qawayen ta. Tace Malam wallahi yadda kasan mayu haka s**a yo kaina. Wata da ta rarumo ni na dauka cizo na zata yi. Dakyar na qwaci kaina. Allah yasa ina training, na samu na gudu da kyar.
Abun tambaya, shin madigo alfasha ne a musulunci koh kuwa? Tabbas haramun ne. Kuma ba hujja da maiyi zai cigaba dayi da hujjar wai Allah zai yafe mata. Muddin bata bari ba Allah sai ya qona ta.
Saboda haka iyaye sai ku tashi tsaye, Magidanta kuma haka. Matasa kuma kusan irin matan da zaku aura domin su haifa maku 'ya'ya na gari. Allah ya kiyaye.

27/06/2017

zuwa ga dandalin sirrin mata kutaimakamun da addu'a wallahi inasonta dagaske kuma auranta nakeso

ASSALAMU'ALAIKU
yan'uwa kutayani da addu'a
wallahi akoi yarinyar danake so na aureta dan Allah ku tayani da addu'a Allah ya kawo sanadiyar da zamuyi auren dani da ita
ya Allah kabani sa'a akan wannan niyya tawa kakawo mun sanadin aurennan.

22/06/2017

# Shawarazuwaga Yan Uwa # Mata
Shawara ta 1
In mijinki yai maki wani abu marar kyau. Kiyi qoqari ki tuna da mai kyan da yayi maki a baya. Domin kowane mutum yana da halaye guda biyumai kyau, da marar kyau. Yar'uwata bayanda za'ai ki samu abunda k**eso 100℅, a lahira ne kawai ake samun haka...
Shawarata 2
Yar'uwata kiyi haquri da mijinki, babu abunda haquri baya haifarwa. Musanman a wannan lokaciyar'uwata in kin tuna Allah da kansa yayi magana akan haquri. To ashe ko ba qaramin abu bane. In kikayi riqo dashi zaki samu riba mai tarin yawa. Domin Allah yana tare da mai haquri.Kuma haquri haskene.... Ki riqe wannan
Shawarata 3
Ki zamo mai yawan godia. Komin qarancin kyauta in oga ya baki kiyita zuba godiyazai kiga kullum gurinsa ya kawo miki.
Shawarata 4
Duk halin da k**e ciki a gidan mijinki ki godema Allah, domin akwai wacce ta fiki matsala, amma tana godiya ga Allah. Ki tuna Allah da kansa yace " bayan tsanani sauqi na zuwa" ki gane
Shawara ta 5
In kun shiga yananin rashi ko wani mawuyancin hali. Maimakon wulaqanci da zakiyita yima maigidanki, kamar yanda wasu mata masu qarancin ilimi keyi. Kiyi qoqari ki dage wajen yiwa mai gidnki addu'a domin addu'a itane takobin mumunidomin Allah fa da kansa cewa yayi " alokacin da kuke roqona ni a kusa nake...." Kuma shiya fada " ku roqeni in amsa muku" a cikin hadisi kuwa cewa akai "addu'a wata kebantacciyar ibadace" ki ganeShawarata 6
Yar uwa ki gane zaman aure yana buqatar sirri. Duk abunda ya faru tsakaninki da mijinki kiyi qoqarin yin nasiha. Domin manzan Allah (S.A.W) cewa yayi "Addini nasiha ne" kai qarar miji wajen iyayensa ko naki ko abokansa ko wasu ba shine zai magance muku matsalaba. Fadawa mutane matsalarki tsakaninki da mijinki ba abune mai kyau ba. Zata iya yiwuwa kina da maqiyin boye a cikin wadanda k**e fawa, musanman qawaye. Wata maimakon taji haushi kina cikin damuwa dadi zatajitayita baki miyagun shawarwari harki kashe aurenki. Ko kinsan manzan Allah (S.A.W) yace " miskini! Miskini!! Miskini!!! Namiji marar aure koda yanada tarin dukia" ya kuma cewa " miskiniya! Miskiniya!! Miskiniya!! Macen da bata da miji koda tanada tarin dukiya" kiyi haquri kiyi zamanki da mijinkiqara zamanki a gidanki so dubu da zamanki a gidankubuhaushe dai cewa yayi " komin goma ta lalace tafi biyar albarka"..... Ki farka
Shawarata 7
Ki qudurce a ranki zaman ibada zakiyi. Kuma ki sama ranki sabida Allah zaki zauna da mijinki, ki yadda da qaddara kowane iri a cikin rayuwarku. In har kika riqe haka to bazaki shiga shahun masu cewa " duk wacce tace namiji ubane xata mutu maraya" ki dauka
Shawarata 8
Ki qudurce a ranki mijin mace hudu kika aura. Ko da wasa yar uwa kada ki yi tunani ke daya zaki zauna da mijinki. Duk wacce tace haka to ba qaramar jahila bacekada ki manta kamar yanda in lokacin mutuwa tazo ba makawa zaki mutu, to haka in lokacin auren mijinki yaxo zaiyiko yanaso ko bayasobari in tuna miki yazo fa daga bakinda bai tafa qaryabacewa " tun mutum cikin cikin mahaifiyarsa ake rubuta abunda zaiyi a rayuwarsa" dan haka da kije gun boka da kije gun malam inhar Allah yace mijinki zaiyi aure to ba makawa sai yayi.

09/06/2017

A*o dayawa wasu na daukan duk mace da bata taba aureba a matsayin budurwa alhali abun ba haka yakeba ana iya samun budurwa a wacce aka daura wa aure da wacce ba ayi mata aureba kuma ana samun wacce ba budurwa ba a chikin yanmata wayanda ba a taba musu aureba
shi budurchi wasu na dauka ana rasashine yayinda mace ta sadu da namiji amma abun ba haka yakeba akoi hanyoyin rasa budurchi dadama dan haka kurubuto manasu

03/03/2017

Shin wacece budurwa yaya take ? shin ana iya samu chikin yanmata wayanda basu taba aure ba kuma su kasance ba budareba?

26/01/2017

mata ake kulawa da haqko kin aure ayi ladabi da biyayya sai asamu sakamako maikyau wajen ubangiji

22/12/2016

MACE ME ZAGIN MIJI !!
Duk matar da take zagin mijinta ko cin mutuncinsa
ko gaya masa bakaken maganganu, Agaban idonsa
ko abayansa, To tabbas ta Aikata abinda yake
haramun, mummuna, kuma kaba'ira.
Zagin miji ko cutar dashi da harshe, wannan yana
daga cikin manyan laifuka a Musulunci (wato
Kaba'ira).
Manzon Allah (saww) ya lissafata matan da suke yin
haka acikin Manyan 'yan wuta. (ya Allah ka
tsaremu).
Da yawa akwai matar da zakaji tana cewa mijinta:
NIFA DAMAN BA SONKA NAKE YI BA.
Ko kuma "IDAN KAI DAN HALAL NE ACIKIN
IYAYENKA, KA SAKENI."
Idan kuma taga tayi masa wulakanci mai yawa
amma bai kulata ba, Sai kaji tana ce masa MARAR
ZUCIYA.
Lokacin da Manzon Allah (saww) yaje Isra'i da
Mi'iraji yaga wadansu mataye wadanda ko Qanshin
Aljannar ma ba zasu ji ba, kuma Mala'iku suna
Dandana musu azaba iri-iri. Asakamakon cutar da
mazajensu da s**ayi.
Don haka ya kamata mataye su sanya tsoron Allah
acikin zukatansu, domin kuwa mijinku na aure shine
Aljannarku idan kun bishi. Kuma shine wutarku idan
kuka sa'ba masa.
Ya Allah ka shiryar da matayenmu na wannan
zamani.

Want your school to be the top-listed School/college in Kaduna?

Click here to claim your Sponsored Listing.

Location

Category

Website

Address


Kaduna