BAYANIN YADDA AKE YIN ISTIKHARA IRIN WACCE ANNABI ﷺ YA KOYAR
:
Istikhara wata sallah ce da akeyi domin neman za'bin Allah madaukakin sarki game da wasu al'amura da bawa yake neman zabin Allah a cikin ɗaya daga cikinsu, misali kamar a harkar neman aure dadai sauran wasu al'amuran.
Anan zamu fahimci cewa ashe ita istikhara ibadace kuma Annabi muhammadu ﷺ shine ya koyar da yadda ake yin ta, sabida haka babu inda akace kaje ayi MAKA ita inkuma kaje daya daga cikin wannan zaayi MAKA . bugun kasa ko duban taurari ko akira aljani a tmby shi shikuma ya gaya musu karya da gaskiya sukuma su gayama Allah yabamu Samar bin abinda Manson Allah ﷺ yazo mana dashi .duk wanda yayi wata istikhara ba irin wacce manzon Allah ﷺ ya koyar ba, to ya sani ba istikhara tabbatacciya yayi ba koda ma yayi babu wani tasiri da zatayi domin Allah madaukakin sarki baya karbar duk wata ibada har sai anyita a bisa koyarwar Annabi muhammadu ﷺ .
Sahabi jabir (ra) yana cewa: *MANZON ALLAH ﷺ YA KASANCE YANA KOYA MASU ISTIKHARA A CIKIN DUKKAN AL'AMURANSU KAMAR YADDA YAKE KOYA MUSU SURA DAGA CIKIN AL'KURANI.*
hadisin yana cikin *Sahihul Bukhari*
kunga wannan yake nuna mana ashe ita itikhara annabi ne ya koyar da ita bawai kowa gaban kansa zeyi kawai yaje ya aikata abinda yaga dama a matsayin istkhara ba.
Hal ila yau dai sahabi jabir yana cewa: Annabi yace: *IDAN 'DAYANKU YAYI NUFIN YIN WANI AL'AMARI TO YAYI SALLAH RAKA'A BIYU BA SALLAR FARILLAH BA SANNAN YACE*
اَللَّهُمَّ إِنِّي أَسْتَخِيرُكَ بِعِلْمِكَ، وَأسْتَقْدِرُكَ بِقُدْرَتِكَ، وَأَسْألُكَ مِنْ فَضْلِكَ الْعَظِيم، فَإِنَّكَ تَقْدِرُ وَلا أَقْدِر، وَتَعْلَمُ وَلا أَعْلَم، وَأَنْتَ عَلاّمُ الغُيوبِ، اللّهُمَّ إِنْ كُنْتَ تَعْلَمُ أَنَّ هَذَا اْلأَمْرَ-(((( وَيُسَمِّي حَاجَتَهُ ))))))– خَيْرٌ لِي فِي دِينِي وَمَعَاشِي وَعَاقِبَةِ أَمْرِي، عَاجِلِهِ وَأَجِلِهِ فَاقْدُرْهُ لِي وَيَسِّرْهُ لِي ثُمَّ بَارِكْ لِي فِيهِ، وَإِنْ كُنْتَ تَعْلَمُ أَنَّ هَذَا اْلأَمْرَ شَرٌ لِي فِي دِينِي وَمَعَاشِي وَعَاقِبَةِ أَمْرِي، فَاصْرِفْهُ وَاصْرِفْ
Zauren Fatawa
Amsoshin Fatawoyin (Tambayoyin) da aka tura a whatsapp group mai suna Zauren Fatawa, wadan da Malam Aliyu Abubakar Masanawa yake amsawa.
18/04/2022
FATAWA A KAN TARBIYYA
➖➖➖➖➖➖➖➖
WASU DAGA CIKIN HADISAN DAKE MAGANA A KAN HAKURI, DA KUMA TSAFTA GA MUSULMI
➖➖➖➖➖➖➖➖
Tambaya:
Aslm alaik
Malam dan Allah ayoyi da hadisai nake nema akan hakuri da tsafta ga ya mace a gidan mijin ta
Amsa:
Wa alaikumus Salam wa rahmatullahi wa barakatuh. Alhamdu lillahi rabbil aalamin wassalatu wassalamu alaa rasulillahi wa alaa aalihi wa sahbihi wa man waalaahu ilaa yaumid din.
Ɗan uwa mai albarka babu wani hadisin haƙuri da tsabta da aka keɓance shi ga mace mai aure a gidan mijin ta. Haƙuri da tsabta ababe ne da suke lazimtar ƴan Adam, a ko da yaushe kuma a ko ina suke, mazan su da matan su, gwagware da masu auren su. Don haka duk hadisan dake tallata falalar haƙuri da tsabta tare da umarni da su, sun shafi kowanen su, haka adadin waɗannan hadisan suna da yawa. Sai dai Insha Allahu zan ambaci wasu kamar haka
عن رسول الله - صلى الله عليه وسلم - أنه قال: (إنَّ العبدَ إذا سبقت له من اللهِ منزلةٌ لم يبلغْها بعمله ابتلاه اللهُ في جسدِه أو في مالِه أو في ولدِه ثم صبَّره على ذلك حتى يُبلِّغَه المنزلةَ التي سبقت له من اللهِ تعالى).
أن - النبي صلى الله عليه وسلم - قال: (ما مِن مصيبةٍ تصيبُ المسلِمَ إلَّا كفَّرَ اللَّهُ بِها عنهُ ، حتَّى الشَّوكةِ يُشاكُها).
عن سعد بن أبي وقاص -رضي الله عنه-، أن رسول الله -صلى الله عليه وسلم- قال: (إنَّ اللهَ تعالى طيبٌ يُحِبُّ الطيبَ، نظيفٌ يُحِبُّ النظافةَ، كريمٌ يُحِبُّ الكرَمَ، جوَادٌ يُحِبُّ الجودَ، فنظِّفوا أفنيتَكم، ولا تشبَّهوا باليهودِ)
عن سعد بن أبي وقاص -رضي الله عنه- قال: قال رسول الله -صلى الله عليه وسلم-: (طَهِّرُوا أفْنِيَتَكُمْ، فإِنَّ اليهودَ لا تُطَهِّرُ أفنِيَتَها)
Wallahu ta'ala a'lam.
6/3/2022
Amsawa:
Malam:
Aliyu Abubakar Masanawa✍️
Click here to claim your Sponsored Listing.
Location
Category
Contact the school
Telephone
Address
Kaduna