17/07/2026
YAU JUMA’A - 17th July, 2026
Ranar Juma'a nada tauraron Zahara (Venus) kuma sa'idin rana ce, tana da tasiri mai ƙarfi a fannin al-ḥubb soyayya. Wannan rana tana da ƙarfin ruhaniya (قُوَّة رُوحَانِيَّة) da ke taimakawa wajen haɓaka dangantaka tsakanin ma’aurata.
Za'a samu nasara sosai idan akayi ayyukan mallaka (ملْك) da nufin ƙarfafa soyayya da aminci tsakanin ma’aurata a wannan rana. Tauraron yana taimakawa wajen tabbatar da haɗin kai da jin daɗin zaman aure.
Haka kuma, Juma’a rana ce dake dacewa don kulla sabbin soyayya (عَلاقَات حُبّ) ko mayar da tsohon aure zuwa sabuwar fahimta da haɗin kai. Wannan tasiri yana taimaka wajen warware matsaloli da rashin jituwar ma’aurata.
Bugu da ƙari, duk wanda s**a rabu da matar sa a irin wannan rana ake zuwa biko (اِسْتِخْدام السِّحْر) na al’ada ko na ruhaniya (Asirin kiranyen ta dawo) suna iya samun tasiri a wannan rana, musamman idan ana yin su don kyautata rayuwar aure da soyayya cikin halal da nagarta, Sannan kuma dukkan aikin da za'ayi sai an haɗa sa da sadaqa mai ƙarfi,shine tasirin sa zai inganta.
ADDU'AR DA AKEYI A WANNAN RANA!
Wannan rana ta Juma'a mai tauraron Zahara da kuma albarkar wannan rana da Allah Ya ɗaukaka fiye da sauran ranaku. Wannan rana ce da ake samun haɗin kai da nasara a al’amuran soyayya, zaman lafiya, da dukkan ni’imomin rayuwa.
Bayan an kammala Sallar Juma’a ko kuma bayan Sallar Magariba, ana yin wannan wuridi. Ba a buƙatar ƙarin nafila a nan, domin manufar shi ne tsarkake zuciya da nufin samun dacewa.
Wuridin shi ne, a karanta Kalmar Shahada (لَا إِلٰهَ إِلَّا اللَّهُ مُحَمَّدٌ رَسُوْلُ اللَّهِ) kafa 1111. Wannan addu'ar tana da ƙarfi wajen buɗe ƙofin soyayya, albarka, zaman lafiya, da haɗin kai a tsakanin ma’aurata da dukkan al’umma.
Bayan an kammala karatun, sai a ɗaga hannu a yi addu’a bisa ga duk wani buƙata ta alkhairi; kamar samun ƙauna da jituwa a aure, nasarar harkokin kasuwanci, tsira daga fitina, ko samun ƙarfin zuciya da kwanciyar hankali.
Wajibi ne yin sadaqa mai ƙarfi bayan kammala sirrin, domin ita ce ke ƙarfafa tasirin wuridin da kuma jawo rahamar Allah. Duk wanda ya yi wannan a ranar Juma’a da niyya mai kyau, zai ga sakamako da yardar Allah cikin sauƙi.
Izininsa ayi Salati ga Annabi (SAW) Sannan a turawa yan'uwa su amfana.
Moussa Alfalaky Almus'haweey
WhatsApp: +2347035259161