Aqidar SALAF

Aqidar SALAF

Share

Manufarmu itace Gyara...

05/06/2022

Wata rana Ash-Sheikh Ahmad Al-Garkawiy "yana zaune a ofishinsa, sai wata daliba ta shigo"sai tayi sallama tace masa: "Malam na zo duba sakamakon jarabawana ne amma dalibai sun yage takardan, don haka nake so don Allah ka taimaka mun ka roki Exam officer a
nuna mun nawa.

Sai Malam ya tashi ya shiga ofishin Exam officer (mai kula da harkan jarabawan makaranta) yace masa idan babu damuwa kuma ba a
sab'a doka ba, a taimaka a nunawa wannan dalibar sakamakon jarabawanta.

Sai s**a ce ai Malam tunda ta biyo ta wurinka duk da baka san ta ba, amma bari a bata ta duba da kanta.
Bayan an baiwa wannan daliba tana dubawa,tana zuwa kan sunanta keda wuya sai kawai s**a ga ta rufe takardan da sauri ta fashe da kuka ta juya ta fita daga ohishin.

Fitar wannan 'daliba keda wuya, sai Malaman nan s**a ga Malam Ahmad Algarqawiy yana zubda kwalla, har ta kai ga ya kasa mallakan idanuwansa.
Bayan an 'dan natsa ka'dan, Sai Malaman s**a ce ma Sheikh Ahmad" Akramakallahu mu ma kasa zukatanmu sun tsinke saboda ita wannan yarinya ko bamu tambaye ta ba mun san sakamakon jarabawa ce bata yi mata kyau ba,
amma kai kuma sai muka rasa dalili, amma mun san dukkan abin da
zai sanya ka zubda kwalla lallai wannan abun ba karami ba ne.

Sai Sheikh Ahmad, Hafizahullahu, ya ce musu: "Wallahi lokacin dana ga wannan yarinyar ta fashe da kuka sai zuciyata take ce mun "Yanzu inda sakamakon lahiranta ne beyi kyau haka ba yaya kenan ?" Yace wannan shine abin da ya tsorata ni saboda a nan ana iya gyara"

"amma banda Lahira "Saboda haka, mu ma 'yan uwa sai mu "hankalta,mu tuna cewa akwai babban sakamako a qiyama"

Muna rokon Allah yasa muga sakamako mai
kyau a ranar lahira dan tsarkin Sunayensa

Usman Albani Abu Abdilrahman

Profile pictures 27/05/2022

GA AMSOSHIN WADANNAN TAMBAYOYIN KAMAR HAKA

1. Akwai wasu Manyan Annabawa guda uku (3) wadanda Kansu bai ta'ba yin furfura ba.
(Sunayensu yazo acikin Suratu Maryam A.S ) Suwaye wadannan??

ANSWER:
Wadannan Annabawan sune
1) ANNABI HARUNA
2) ANNABI ISMA'I'll
3) ANNABI IDRIS


2. Akwai wasu Annabawa guda Uku (3)
wadanda basu taba yin Aure ba har s**a koma ga Allah (Su ma sunayensu yazo ajere acikin Suratul An-aam). Meye sunansu?

ANSWER:
Wadannan Annabawan sune:
1) ANNABI YAHAYA
2) ANNABI ISAH
3) ANNABI ILIYAS


3. Akwai wasu Annabawa guda biyu, (2)
Sarakuna ne kuma Manzanni ne. Daya daga cikinsu shiya haifi dayan. Meye sunansu?

ANSWER:
Wadannan Annabawan sune:
1) ANNABI DAUDA wanda shi ya haifi
2) ANNABI SULEIMAN


4. Akwai wasu Annabawa Mursalai guda (2) Wa da Qani ne. Shi Qanin an bashi Littafi da Mu'ujizozi. shi kuma yayan an bashi Fasahar harshe. Meye sunansu?

ANSWER:
Wadannan Annabawan sune:
1) ANNABI MUSA (shine karami ) Allah ya bashi littafi mai suna "ATTAURA" kuma ya bashi mu'ojuzoji misali sarrafa "SANDA" Sai kuma
2) ANNABI HARUNA (Shine yayan) Allah ya bashi FASAHAR HARSHE


5. Akwai wani Annabi Mursali (Ba Annabi Adamu bane) amma duk wanda ka gani abayan Qasa, to Jikansa ne. Wani Annabine?

ANSWER:
Wannan Annabi Shine:
Adamu na biyu wato ANNABI NUHU A.S


6. Annabi Ya'aqubu yana da wani suna wanda Allah ya ambaceshi dashi acikin Alqur'ani. Kuma har yanzu ana kiran Zuriyarsa da wannan Sunan.. Shin wanne suna ne wannan?

ANSWER:
An kira su da "ALI YAKUBU" a suratul Maryam, amma kuma an bashi sunan "ISRA'I'll" zuri'ar sa kuma BANU ISRA'ILA


7. Akwai wata halitta wacce Allah yai mata Wahayi. ita ba Mutum bace, ba Aljan bace, kuma ba Mala'ika bace. Shin wacce Halitta ce wannan?

ANSWER:
Wadannan Halittu sune:
1) TURURUWA da kuma
2) QUDAN ZUMA

Allhamdullahi Mungode
Allah yakara mana fahimtar Alqur,ani alfarman Wanda yazo dashi wato ANNABI S.A.W

Katura Zuwa Group 3 Kachal Domin Al'umma Su Amfana ❤️

Photos from Ash-Sheikh Muhammad Awwal Maishago Zaria.'s post 27/04/2022
Want your school to be the top-listed School/college in Kaduna?

Click here to claim your Sponsored Listing.

Location

Category

Telephone

Website

Address


No, 37 U/shanu
Kaduna