Barsher Uthmarn

Barsher Uthmarn

Share

Allah ya cika Muna burukan mu na Alkairi

08/04/2024

πŸ›‘ DA ƊUMI-ƊUMINTA

Anga jinjirin watan shawwal a qasar mu ta Nijar,a garin Bangui dake Ζ™aramar hukumar Madawa ta cikin jahar Taoua (Tawa).
saboda haka gobe xamu tashi da sallah, tare da fatan Allah ya amshi ibadun da mukayi.
ΨͺΩ‚Ψ¨Ω„ Ψ§Ω„Ω„Ω‡ Ω…Ω†Ψ§ΩˆΩ…Ω†Ϊ©Ω… Ψ¬Ω…ΩŠΨΉΨ§

11/12/2023

Wani Bawan Allah yayimin tambaya wai meyasa yan IZALA ke ganin kamar su ne kadai zasushiga aljannah a ranar alkiyama??

Amsa Shine: πŸ‘‡

Zaka shiga aljannah idan kabi Allah da manzon Allah kuma kayi aiki irin na yan aljannah, sai Allah ya gafarta ma yayima rahama.

Ko kana acikin IZALA idan baka bin Allah da manzon Allah, idan kabi son zuciya, kayi aiki irin na yan wuta to ko shakka babu zakashiga wuta.

Kenan kasancewarka dan IZALA bazai hanaka shiga wuta ba har sai kabi Allah da manzonsa.

Kasancewarka dan DARIKA ba zai sa kashiga wuta ba matukar kabi Allah da manzon Allah ka bautata wa Allah shikadai batare da yimasa kishiya ba.

Saboda haka mudaina ruduwa da kungiya ko jinin malanta, WALLAHI duk inda kake, ko waye mahaifinka, ko kai jinin waye, duk karatunka duk iliminka wallahi sai kabi Allah da manzon Allah, kayi aiki irin na yan aljannah sannan zakashiga aljannah.

Manzon Allah saw yana matukar son NANA FADIMA, yarsa ce, kuma yace tsoka ce acikin jikinsa. Amma kuma annabi yace da ita wallahi a ranar alkiyama bazai iya ceton ta daga azabar Allah ba, har sai ta bi Allah anan duniya ta bautata masa.

Manzon Allah fa πŸ€”

To ballantana wani shehi ko gausi ko malami.

Allah ya gafarta mana AMEEN.
Albashirmuhammad

11/09/2023

Zamuyi jarabawa maii Maki takwas 😁😁😁😁

Idan akwance kake karanta sakon karasa Maki Daya πŸ‘Œ

Idan hannunka biyu akan wayanka kake karanta sakon karasa Maki Daya πŸ‘Œ

Idan kana karanta sakon Nan a xuciyarka karasa Maki Daya πŸ‘Œ

Idan a daki kake ko a shago kake karantawa karasa Maki Daya πŸ‘Œ

Idan Kai kadaii kake karantawa karasa Maki Daya πŸ‘Œ

Idan kanka Babu hula ko dankwali karasa Maki Daya,πŸ‘Œ

Maki nawa kasamu Banda karya πŸ™πŸ™πŸ™πŸ˜πŸ˜πŸ˜

09/09/2023

'Yan Zaman Majalisa Ba 'Yan Zaman Banza Bane! Kadan Daga Cikin Amfanin 'Yan Zaman Majalisa:

1. Sallah Bata wucesu

2. Bada taimakon gaggawa idan hatsari ya faru

3. Kula da sabbin puska

4. Kula da kannenku da tarbiyan su

5. Yashe lambatu, gyaran hanya idan Ana aikin kungiya.

6. Kokarin raba fada tsananin Dan Acaba da fasinja

Duk da dai 'yan Mata suna Shan kallo da Kuma gulma idan sunzo wucewa, Amma dai bazasu Bari Kuma wani yaci mutuncin ki ba.

Kina gaishesu kada ki raina su domin sudin dai sune za'a tambaya akan halinki idan anzo neman aurenki.

Kai daukomin bencin nan ka kaishi bakin titi😎

Photos from Barsher Uthmarn's post 09/09/2023

Ga wani dan gajeren labari cikin hotuna.

Mata sunfara yawo da Abun bugun samari Akula guy's 🚢😁🀩

24/07/2023
Want your school to be the top-listed School/college in Kaduna?

Click here to claim your Sponsored Listing.

Location

Telephone

Website

Address


Richifa
Kaduna