30/08/2025
DA DUMI-DUMI: Pantami Ya Biya Kuɗin Rajistar Ɗaliban Jihar Gombe a Jami’ar BUK
Farfesa Isa Ali Pantami, CON (Majidadin Daular Usmaniyya) ya sake yin abin yabo wajen tallafa wa harkar ilimi, inda ya biya kuɗin rajistar dukkan ɗaliban Jihar Gombe da ke karatu a Jami’ar Bayero Kano (BUK).
Lamarin ya biyo bayan rubutun wani matashi a dandalin X (Twitter) da ya bayyana ƙalubalen da ɗaliban ke fuskanta wajen biyan kuɗin rajista. Pantami ya gaggauta amsa kiran tare da ɗaukar nauyin kuɗin gaba ɗaya.
Shugaban ƙungiyar ɗaliban Gombe a BUK (BUK-GOSSA), Muhammad Al Amin Abdulkadir, ya tabbatar da biyan kuɗaɗen a shafinsa na Facebook, yana mai yabawa wannan gagarumin taimako da ya rage wa iyaye da ɗalibai nauyi.
30/08/2025
30/08/2025
30/08/2025
15/07/2025
02/11/2024