Assalamu Alaikum Wa Rahamatullahi Ta'ala Wa barakatuhu.
Mal Muhammad Almustapha Muƙaddam Narkuta Online Tv
NEMAN ILIMI YA ZAMA WAJIBI NE GA KOWANE MUSLIM.
28/02/2019
Ya ALLAH ka kare Musulunci da Musulmi.
Dan Nabiyun RAHMA
Alaihi wa salam
Barka Da Wannan wata mai albarka watan da aka Haifi fiyayyan Halitta Annabi Muhammad Sallalahu Alaihi Wasallam.
WAJIBI NE A HALARTO SALLAN
JUMU'A IDAN TA
HADU RANA DAYA DA IDI.
::
Imamu Malik da Abu Hanifa sun
ce idan sallan
jumu'a da idi sun kasance a
rana daya shari'a
tana umurtan dukkan mutumin
da ya kai hadin
balaga da ya halarci sallan
Jumu'a da na Idi, shi
sallan Idi Sunna ne shi kuma
sallan Jumu'a
farilla ne, domin haka dayansu
ba zai yiwu ya
maye daya ba, wannan shine
asali. Lallai an
samu sabani a wajen Malaman
Mazahabobi
mafiya shahara guda hudu,
amma guda uku daga
cikinsu sun tafi akan cewa
haduwan sallan
Jumu'a da Idi rana daya bai
zamowa hanzarin da
zai saryar da Sallan Jumu'a,
Malaman da s**a
tafi a kan wannan matafiya
sune: Imamu Malik da
Imamu Shafi'i da Abu Hanifa.
babbban dalilin da
jamhurin Malamai suke kafa
hujja a kai shine:
Na farko
Ayan Alqur'ani na cikin Suratul
Jumu'ati Aya Na
09
ﻳﺄﻳﻬﺎ ﺍﻟﺬﻳﻦ ﺀﺍﻣﻨﻮﺍ ﺇﺫﺍ ﻧﻮﺩﻱ ﻟﻠﺼﻼﺓ ﻣﻦ
ﻳﻮﻡ ﺍﻟﺠﻤﻌﺔ
ﻓﺎﺳﻌﻮﺍ ﺇﻟﻰ ﺫﻛﺮ ﺍﻟﻠﻪ
Abun da s**a kafa hujja da shi
shine wannan aya
tana umurni ne da a tafi zuwa
Jumu'a ida aka
kira salla a ranar Jumu'a, kuma
wannan ayan
tayi umumin dukkan ranakun
Jumu'a ba tare da
ta kebance wani rana ba, don
haka bai hallata a
kebance wata rana daban ba
matukar babu wani
ingantacen dalili da ya kebance
wannan nassi
kad'i ba.
Na Biyu
Ba'a samu wani hadisi
ingantace da aka ruwaito
cewa Annabi Sallan Lahu Alaihi
Wasallam ya bar
Sallan Jumu'a saboda ta
kasance rana daya da
Idi ba. An samu hadisi ingantace
daga Nu'uman
bn Bashir yana cewa: Manzon
Allah Salla Lahu
Alaihi Wasallam ya kasance a
cikin Sallan Idi
guda biyu (karamar Sallah da
bubban Salla) da
kuma Sallan Jumu'a yana
karanta suratul A'ala
da suratul Gashiya, ya kuma
kasance idan Idi da
Jumu'a s**a hadu a rana daya
yakan karanta
wadanan surorin a cikin sallan
Idi sannan ya
kuma karantasu a Sallan
Jumu'a. Wannan dalili
ne da yake nuna cewa Annabi
Sallan Lahu Alaihi
Wasallam, yana aikata Sallan Idi
sannan ya kuma
aikata Sallan Jumu'a a rana daya
kowanne kuma
a lokacin shi, don haka duk
abinda ya saba ma
abinda Annabi Salla Lahu Alaihi
Wasallam ya ke
aikatawa ba zai zamo Sunna ba.
Lallai an samu ruhsa ga
wadanda suke zama a
kauyukan da ya wuce mil uku
daga birni, Idan
s**a halarto Idi a ranar Jumu'a
ba sai sun kuma
dawowa Sallan Jumu'a ba
saboda hadisai kamar
haka:
Na Farko:
An karbo daga Abu Hurairata
Radiyallahu Anhu,
Lalle Manzon Allah Salla lahu
Alaihi Wasallam ya
ce “Haqiqah idi biyu sun hadu a
wannan rana,
duk wanda ya so, wannan idin ta
isar masa daga
sallan juma'a, amma mu kam
(Mutanen Madina )
za mu sallaci juma'ar” (Abu
Dawud 1\281),
Na Biyu:
An karbo daga Abi Ubaid Maula
ibn Azhar ya ce
“Na halarci idi tare da Usman bn
Affan, kuma ya
kasance wannan ranar ranar
Juma'a ce, sai ya yi
sallah sannan ya yi Khudba
kuma ya ce “Ya ku
mutane Haqiqah idi biyu sun
hadu maku a
wannan rana, duk wanda yake
so ya saurari
Juma'a daga mutanen kauye ya
saurara, wanda
ya ke so ya tafi, to hakika nayi
masa izni
(Bukhari 7\134, Fathul Bary
10\29 Hadisi na 5572,
Muwatta Malik 1\190). Abin da a
ke nufi da Awali
shi ne, kauyukan da su ke gefen
Madina,
wadanda su ka kai Mil uku ko
fiye da haka.
Daga cikin Malaman
Mazhabobin nan Imamu
Ahmad ne kawai ya yi umumin
wannan ruhsan
cewa har da mutanen da suke
zama a birni ba
dole sai sun yi Sallan Jumu'a a
ranar Idi ba idan
s**a halarci Sallan Idin.
Dole ne mu mabiya Mazhaban
Imamu Maliki
mubi fatawar cewa wajibi ne Mu
halarci Sallan
Jumu'an idan ta kasance rana
daya da Idi,
saboda dalilai kamar haka:
Na Farko
Mu mutanen yamma, muna bin
Mazhaban
Malikiyya ne, kuma a Mazhaban
Malikiya
haduwan Idi da Jumu'a rana
daya bai zamowa
hanzari da zai saryar da Sallan
Jumu'a, Imamu
Khalil mai littafin mukhtasar ya
jero a cikin jerin
abubuwan da ba su zamowa
hanzari na rashin
halartan sallan jumu'a, sai ya ce:
( ﺃﻭ ﺷﻬﻮﺩ ﻋﻴﺪ ﻭﺇﻥ ﺃﺫﻥ ﺍﻹﻣﺎﻡ )
Ko halartan Idi ko da sarkin
musulmi ya yi izini
ga mutane cewa ba sai sun
halarto Idi ba.
Na Biyu
Dole ne mu halarci sallan
Jumu'a a ranar Idi
saboda Annabi Salla Lahu Alaihi
Wasallam bai
taba barin Sallan Jumu'a don ta
zamo rana daya
da Idi ba, kuma wannan al'ada
ita ce muke kanta
a wannan yanki namu, sannan
ma ni ban ga wani
gwaninta ba don mutum bai je
Jumu'a ranar Idi
ba domin ko Malaman da s**a
ce ta saraya ai
ruhsa s**a ce, don haka
halartan Jumu'an ya Fi.
ALLAH YA MUNA MANA WANNAN
RANA (IDIN BABBAN), LAFIYA YA KARAMANA SOYAYYAR MANZON ALLAH (SAW),
AMEEEEEEEEN SUMMA AMEEEEEN.
ILORIN 2017;
;
'Kungiyar 'MAJMA'U AHBABU SHEIKH IBRAHIM
NYASS NIGERIA' Ta Tabbatar Da Ranar ASABAR
(29-April(04)-2017) a Matsayin Ranar Da Za'a
Gabatar Da MAULIDIN MAULANMU SHEHU
IBRAHIM NYASS(R.A) Wanda Aka Saba
Gabatarwa Duk Shekara, Wanda Insha ALLAHU
Bana Za'a Gabatar a Birnin ILORIN(Jihar
Kwara).
;
(Sanarwa Daga; National's P.R.O Sheikh Alhaji
Sani Rogo).
;
YA ALLAH! DON ALFARMAR SHUGABA(S.A.W) KA
NUNA MANA WANNAN LOKACIN CIKIN RAI DA
'KOSHIN LAFIYA, KA HOREWA KOWANNENMU
DAMAR ZUWA WAJEN WANNAN TARON MAI
'DIMBIN ALBARKA AMEEEEEEEEEN.
ASSALAMU ALAIK*M WA RAHAMATULLAHI TA'ALA WABARKATUHU.
Ina yimawa yan'uwa musulmi masoya ANNABIN ALLAH (s.a.w) Murnar shiga sabon watan rabi'ul awwal watan da aka haifi fiyayyan halitta ANNABI MUHAMMADU (S.A.W) . ALLAH kara mana son sa Ameen.
ASSALAMU ALAIK*M WA RAHAMATULLAHI TA'ALA WA BARAKATUHU..
Bayan Sallama irin ta Addinin Musulunci Nake Sanar da Yan Uwa Musulmi,
Fara karatun Tafsirin Al'Qur'ani na watan RAMADAN.
Wanda za a fara daya ga watan RAMADAN:- Wanda za ayi a Babban Masallacin garin Naraguta
INSHA ALLAHU.
ALLAH ya karbi ibadun mu Amin..
Cigaba:-Sakamakon ma,aikaci a cika masa ladansa.Sai ubangiji yace:-ya ku mala,ikuna ina shaida muku haqiqa na sanya landan azumin su, da tsayuwar daren su ya zama samun yardata dasu da gafarata a garesu san ubangiji madaukaki sarki yace yaku bayina ku rokeni na rantsen muku da buyata da girmana ba abun da zaku tambaye ayau na duniyar ku da lahirar ku face saina baku she.. Wassalatu wassalamu ala astaqi qaili wa anjahi sa ilin wa auwali shafa,in wa abdalin mu shafa,in sayyidina MUHAMMADU (S.A.W) ALLAH yabamu zaman lafiya a garin mu da kasar mu baki daya amin RAMADAN MUBARAK JUMA,AT KAREEM
Cigaba:-Sannan ALLAH madaukakin sarki kowacce rana ciki RAMADAN yana yanta mutane dubbai a lokacin bude baki wadanda s**a cancanta ayi musu azaba sannan idan ranar juma'a tayi, kowanne sa,a daya da rana ALLAH yana yanta mutane dubbai wayanda s**a cancanta ayi musu azaba.Haka kuma in ranar karshe tayi ALLAH yana yanta yawan wandanda yantu daga farko zuwa karshe.Sannan idan daren lailatul qadri yayi ALLAH madaukakin sarki zai hori mala'ika jibrilu ya sauko da rindunar mala'iku izuwa kasa da tuta koriya a hannunsa sai yaje ya kafata akan ka'aba she kuma jibrilu yana da fukafukai dari shida(600) biyu daga ciki baya bude su sai ranar lailatul qaddari, inya budesu suna lullube duniya gabar da yamma sai jibril ya aika wannan mala'ikun cikin al,umma su rukayin sallama abisa wanda s**a samu yanayin kowacce ibada kuma suriqayin hannu dasu kuma su dinga tayasu yin addu'a har alfirjir ya keto idan alfijir ya keto sai jibril ya kira dukkan mala'ikun sukuma malaikun sai su tambayi jibril mai ALLAH yayiwa muminai daga alummar Annabi Muhammadu(s.a.w) she kuma jibril sai yace:ALLAH madaukakin ya kalle su yayi musu rangwame yayi gafara a garesu amma banda mutum hudu(4) sai mala'iku s**e ya jibrilu suwaye mutum(4) sai yace: (1)mai shan giya(2)mai sa6awa iyayensa(3)mai yanke zumunci(4)mashaahinun sai sahabai s**a ce ya manzon ALLAH (s.a.w) waye mashaahinu sai manzon ALLAH yace:-mai yin gaba da danuwansa musulmi har ya shige kwana(3).Sannan in daren ranar sallah yayi ALLAH yana kiran wannan daren da cewa daren sakamako in antashi da safiya ranar sallah ALLAH zai aika mala'iku ko wani gari a cikin kasa su tsaya a kofar gari suyi kira da babbar murya kowane mahaluki yana jinsu banda mutane da aljanu sai s**e ya alummar Annabi Muhammadu(S.A.W) ku futo zuwa wajen ubangiji mai girma domin yabaku sakamako mai kauri kuma ya gafarta muku zunubai masu girma sannan idan mutane s**a fito masallaci sai ubangiji mai girma da daukaka yace:-yaku mala'ikuna meye sakamakon ma,aikaci idan yagama aikinsa?sai mala'iku s**eya ubangijinmu ya shugabanmu
A'UZUBILLAHI MINAL SHADANIR RAJIM-BISMILLAHI RAHAMANI RAHIM:-WASSALATU WASALAMU ALA KHAIRIN BARRIYATI TARJUMALUL ASMAI WASSIFATI SAYYADINA WANA BIYINA MUHAMMADIN SALATAN WASSALAMAN DA IMAINI MUTTALA AZIMAINI WASSALAMA TASSLIMA KASIRAN:...Bayan abin daya gabata ASSALAMU ALAIK*M YA JAMA'ATAL MUSLIMINA WA RAHAMATULLAHI TA'ALA WABA RAKATUHU.,Ina taya mu farin cikin shiga cikin wata mai alfarma wato watan RAMADAN saboda haka naga ya cancanta inyi mana albishir da HADISI NA DAYA(1) cikin babi na talatin da tara(39) cikin littafin dana gabatar cikin wassiyar data gabata wanda ABDULLAHI DAN ABBASU ya rawaito:-inda yake cewa naji annabi MUHAMMADU(S.A.W) yana cewa:-Haqiqa aljanna tana alfahari kuma tana ado daga shekara zuwa shekara saboda shiga watan RAMADAN daren farko iska tana motsawa daga karkashin al,arshi anace mata iska.Yayan itace kuma ganye bishiyoyin aljanna suna kadawa,tudun kofofin aljanna suna motsi har ana jin wata murya mai dadi daba a taba jin taba sannan yan matan hurulaini sufito su tsaya akan tudun aljanna suyi kira akan tudun aljanna s**e wa zai nemi auren mu a wajen ubangiji madaudakakin sarki,ubangiji ya aurar masa damu sannan s**e ya riddiwanu wannan wane irin dare ne sai riddiwanu ya amsa musu yace ya khairatul hisanin wannan daren farko ne daga watan RAMADAN sannan ubangiji madaukakin sarki yace:-ya riddiwanu kabude kofofin aljanna ga masu azumi daga al,ummar Annabi Muhammadu(S.A.W) sannan Ubangiji madaukakin sarki yace ya maliku ka kulle kofofin wuta ga masu azumi daga alummar Annabi Muhammadu (S.A.W) sannan ubangiji madaukakin sarki:-yace jibrilu ka sauka kasa ka daure shedanu masu tsauri kai kayi musu qunqumi ka jefa su cikin kogi mai zurfi kada su 6ata azumi al'ummar masoyina Annabi Muhammadu(S.A.W) sannan Ubangiji madaukakin sarki yana kira sau uku cikin kowanne dare yana cewa ko akwai mai roqo in bashi abin da ya roqa ko akwai mai tuba in kar6i tubansa, ko akwai mai neman gafara in gafarta masa sannan ALLAH madaukakin sarki yayi kira yace:-Wa zaiba ALLAH rance nayi masa kyakyawan biya.2b con
ASSALAMU ALAI K*M WA RAHAMATULLAHI TA'ALA WABARAKATUHU YA JAMA'ATAL MUSLIMIN:-Bayan sallama irin ta addinin musulunci. Ina sanar da yan'uwa musulmi cewa idan ALLAH ya kaimu rai da lafiya gobe talata karfe hudu da rabi. zan fara gabatar da tafsirin AL,QUR'ANI mai girma cikin watan azumi.ALLAH ya kaimu lafiya ya kuma karbi ibadun mu amin...
A'UZUBILLAHI MINAL SHAIDANIR RAJIM.
BISMILLAHI RAHAMANI RAHIM.,
WASSALATU WASSALAMU ALA ASHARAFIL MURSALIM...
Bayan abin da gabata...!
ASSALAMU ALAI K*M YA JAMA'ATAL MUSLIMIN WARAHAMATUL TA'ALA WA BARAKATUHU.
Ina tayamu farin ciki zagowar watan,
RAHAMAH.
Watan GAFARA,
Watan Samun Yanci daga azabar ubangiji (Subhanahu Wata Ta'ala), wato watan RAMADAN saboda haka naga ya cancanta in sanar damu hudubar da manzan ALLAH ( Sallallahu Alaihi Wasallam ) Yake yiwa sahabansa in karshe watan sha'aban ya taho domin muyi tattalin yin ibada.
A wata mai Alfarma idan yazo, wato RAMADAN.
Wannan hudubar na ciro tane a cikin littafin (TAMBIHUL GHAFILINA).
Wanda SHEIKH NASRUL BIN MUHAMMADIN ALHANAFIYYI ya tara shi cikin ayoyin ALQUR'AN da HADISAN Manzon ALLAH (Sallallahu Alaihi Wasallam) cikin babi na talatin da tara (39) a cikin hadisi na SHIDA (6) wanda SALMANUL FARISI ya rawaito inda yake cewa:-
Manzan ALLAH (Sallallahu Alaihi Wasallam) yayi mana huduba a ranar karshe daga watan SHA'ABAN.
INDA YAKE CEWA:- Yaku mutane haƙiƙa watan mai girma,mai Albarka,ya lullubeku.watan da ake samun lailatul Ƙadri a cikin sa. Shi kuma Lailatul Ƙadri shine wanda yin bauta a cikin sa yafi zuwa yaqin wata dubu, Shi RAMADAN shine ALLAH ya farralta yin Azumi a cikinsa ya sanya tsayuwar dare ta zama kusanci da ALLAH a cikinsa duk wanda ya nemi kusanci da ALLAH da wani aikin alkhairi a cikinsa zai samu lada kamar ya aikata farillah a cikin wani wata, wanda ya aikata farillah a ciki sa, zai samu lada kamar ya aikata farillah saba'in (70) a cikin wani wata.
Wata Ramadan shine wata Hakuri, Ladan wanda yayi hakuri a cikin sa shine za'a shigar dashi Aljanah.
Watan Ramadan shine watan taimakon bayin ALLAH saboda ALLAH.
Watan Ramadan a cikinsa ne arziki muminai yake karuwa wanda ya ciyar dame azumi a cikinsa yana da lada kamar ya yanta bawa musulmi kuma zai samu gafarar zunubansa.
SALMANUL FARASI yace:-Sai mukace ya Manzan ALLAH (Sallallahu Alaihi Wasallam) Ba kowane bane a cikin mu zai samu abinda zai ciyar da mai azumi da shi ba.
Sai Manzan ALLAH ( Sallallahu Alaihi Wasallam) yace: ALLAH yana bada irin wannan ladan ga wanda ya ciyar da mai azumi da nono zuqa daya ko ya ciyar da mai da mai azumi da dabino daya, ko ya shayar da ruwa Ƙurba daya. Manzan ALLAH (Sallallahu Alaihi Wasallam) Yace:= Wanda ya kosar da mai da mai azumi zai samu gafarar dukkan zunubansa kuma ubangiji zai shayar dashi daga tabkin alkausara ta.
Watan Ramadan?
(Farkon sa Rahama ne)
(Tsakiyar sa Gafara ce)
(Karshen sa yanci ne daga Azabar wuta) ƙarshe Manzan ALLAH (Sallallahu Alaihi Wasallam ) yace: wanda ya rage lokaci aiki ga yaransa ALLAH zai ƴantashi daga azabar wutar sa.
ALLAH ya nuna mana wanna watan mai Albarka.
A cikin lafiya da zaman Lafiya a kasar mu da duniya gaba daya.
ALLAH ya bamu ikon tattalin ibada da yin ibada a cikin wannan wata mai albarka Amiin..
Click here to claim your Sponsored Listing.
Location
Category
Contact the school
Telephone
Website
Address
NARAGUTA JOS
Jos