Sunnah vibe

Sunnah vibe

Share

📚Connecting you to the Islamic teachings and traditions.🤲hoping this page will serve as sadaqah.

Telegram: Contact @TambayaDaAnsa 01/04/2024

HUKUNCIN ƊAGA HANNU A SALLAH:
:
𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
:
Ina tambaya ne shin dole ne ɗaga hannu a sallah, misali kaman wurin yin sujjada da ɗagowa. ko kuwa in anyi kabbaran tada sallah shikenan?
:
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
:
Daga hannu a cikin sallah yayin kabbarar harama hakki ne a kan kowane musulmi yayin da ya zo yin Sallah. Haka ma sunnah ne ɗaga hannu yayin yin ruku'i da sujada.

Ya zo a hadisin Ibn Umar (r.a) cewa, Lallai Annabi Sallallahu Alaihi Wasallam ya kasance ya na ɗaga hannunsa kusa da kafadunsa yayin da zai buɗe (fara) sallah da lokacin da zai yi kabbara don yin ruku'i da lokacin da ya ɗago daga ruku'i. Bukhary da Muslim.

Tun da kuwa har ya kasance Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallam na ɗaga hannu lokacin kabbarar harama, da ruku'i da ɗagowa daga ruku'i wannan ke nuna muma hakki ne a kan mu, mu yi riko da wannan sunnah. Domin Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallam ya ce: “Ku yi sallah kamar yadda kuka ga Ina yin Sallah”

Saboda haka 'yar uwa ana ɗaga hannu a dukkan Waɗannan wuraren uku da muka ambata.

WALLAHU A'ALAM.

✍🏿Ayyoub Mouser Giwa.
08166650256.

Zauren Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah. Ku kasance Damu...
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇
https://t.me/TambayaDaAnsa

ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ

Telegram: Contact @TambayaDaAnsa

Telegram: Contact @TambayaDaAnsa 01/04/2024

SHIN ANA FITAR DA ZAKKAR FIDDA-KAI DA GERO?
:
𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
:
Assalamu Alaikum. Malam game da zakkar fidda Kai da ake yi ana iya fitarwa da gero alhali mutum na da shinkafa, dalilin da ya sa za su fitar da gero saboda su ma shinkafa wata rana tana buwayarsu. amma lokutan ba ya suna fiddawa ne da shinkafa, amma shinkafar su ma ba su cika sonta ba. Kuma an ce ba a ba Allah abun da ba ka so, shin suna iya fitarwa da gero?
:
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
:
Wa'alaikumus Salámu, 'yar uwa bayani yalwatacce ya gabata a Amsoshin Tambayoyinku a kan hukunce-hukunce masu alaqa da Zakkar Fid-da-kai, kina iya komawa can domin samun qarin bayanai. A hadisan da s**a yi magana game da zakkar fidda-kai sun tabbatar cewa Annabi Sallallahu alaihi Wasallam ya farlanta a fitar da zakkar fidda-kai da wasu nau'o'i na abinci, sai malamai s**a fassara hakan da cewa:

Mutum zai fitar da zakkar fidda-kai ne da nau'in abincin da aka fi ci a garinsu, wato ba dole ne sai nau'in abinci guda ɗaya tal ba, mutum zai lura da nau'in abincin da aka fi ci ne a garinsu, kuma ya zama nau'i ne da yake da halin fitar da zakkar da shi. Don haka babu laifi idan kun fitar da zakkar fidda-kai da gero, saboda shi ma yana daga cikin abincin da ake yawaita ci a qasar Hausa.

Allah S.W.T ne mafi sanin daidai.

Jamilu Ibrahim, Zaria.

Zauren Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah. Ku kasance Damu...
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇
https://t.me/TambayaDaAnsa

ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ

Telegram: Contact @TambayaDaAnsa

Telegram: Contact @TambayaDaAnsa 01/04/2024

LOKACIN FITAR DA ZAKKAR FIDDA-KAI:
:
𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
:
Assalamu alaikum Malam. Da Wanne Lokaci Ake Fitar Da Zakkar Fidda-kai?
:
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
:
Wa'alaikumus Salam Warahmatullahi Wabarkatuhu.

Abunda yake wajibi shine fitar da zakkar fidda-kai kafin fita zuwa sallar idi, saboda hadisin Abdullahi dan Abbas yardar Allah takara tabbata agareshi yace: Manzan Allah sallallahu Alaihi wasallam ya wajabta zakkar fidda-kai dan tsarkake mutane daga kazantar zancen banza da s**ayi da kuma na sha'awa lokacin azuminsu da kuma ciyar da miskinai, wanda ya bayar da ita kafin sallar idi lallai zakkace karbabbiya, wanda yabayar da ita bayan sallar idi to sadakace daka cikin sadakoki) Abu dauda( 1609) da Ibnu majah ( 1827) Albani ya ingantashi acikin sahihu Abu dauda.

Wannan hadisi ya nuna da zarar limamin dake yiwa mutane sallah ya idar da sallah lokacinta yafita.

Saidai idan wajen daba'a sallar idi kamar kauyuka misali, to zasuyi amfani da lokacin fitarwar mutanen garin dake kusa dasu.

Albuhti yace: Abunda yafi shine fitar da ita kafin fita zuwa sallar idi, ko kuma qaqqara lokacin dayake kafin fita sallah aguraren daba'a sallar idi, Domin Annabi sallallahu Alaihi wasallam yayi umarni afitar da ita kafin mutane su fita zuwa sallar idi, acikin hadisin ibnu umar.

Malamai s**ace: Abunda yafi shine fitar da ita yayin da mutum zai fita zuwa sallah, Kashshaful Qina'i ( 2/252).

WALLAHU A'ALAM.

Zauren Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah. Ku kasance Damu...
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇
https://t.me/TambayaDaAnsa

ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ

Telegram: Contact @TambayaDaAnsa

26/03/2024

This Ramadan, I believe it will be one of the most difficult times for those struggling to find enough to eat. We can seize this opportunity to help ourselves by reaching out to those in dire need of food.

Imam Ghazali teaches us in his book, Ihya Ulum ad-Din, that when we engage in such activities, we are helping ourselves, not just those receiving the charity. Charity is purification, and hence it is the poor person who has done us the favor.

Maulana Imam Maqary emphasized in his lecture last week that we should all understand that nothing is too small when it comes to charity. This is the best way to show gratitude to Allah (SWT) for the blessings bestowed upon us, more pragmatic than simply mentioning “Alhamdulillah” in zikr, because genuine intention is found in action.

In my personal opinion, I would advise that when helping people this Ramadan, we should endeavor to do it ourselves, if possible, rather than just sending a token to a charity organization. This will not only ensure accountability but also give us firsthand experience of the challenges people are facing, prompting reflection on the blessings of Allah upon us.

The Buddhist monks have a practice called Dhutanga, an ascetic practice undertaken to cultivate renunciation and simplicity. It is a voluntary act of offering food to the community directly as an expression of generosity and compassion. The act of giving out directly helps demonstrate generosity and empathy in action.

Finally, among the five matters that Imam Ghazali mentioned that we should be vigilant about regarding charity is secrecy. We should not turn the misery of others into a show. The Prophet (SAW) said in a hadith that is in al-Bukhari:

"The one who gives charity with his right hand while the left hand does not know, is one of the seven whom Allah will shade on the Day when there is no shade except His shade."

May Allah grant us the opportunity to witness Ramadan and enable us to benefit from the blessings that accompany it. Ameen.

Rayyan Tilde

Tambaya Da Amsa 20/03/2024

HUKUNCIN WANDA AKA ƊIBA JININSA ALHÃLI YANA AZUMI:
:
𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
:
Assalamu Alaikum
Malam dan Allah in mutum yana azumi aka debi jinin sa za'ayi gwaji, Shin azumin sa ya karye??
:
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
:
Idan aka ɗebi jinin mutum domin yin gwaji da rana a yayin da yake azumi, hakan baya karya azuminsa, kasancewar jinin da ake yin gwaji dashi dan kaɗan ne.

Haka kuma duk wani jini da ake ɗiba daga jikin mai azumi, Toh azuminsa yana nan, matuqar dai jinin ɗan kaɗan ne aka ɗiba. Amma idan jinin mai yawa ne aka ɗiba, Toh anan Malamai s**ace sai ya rama azumin wannan ranar domin fita daga shakka na saɓanin ra'ayin Malamai.
(Fataawa Al-Lajnatul Daa'imah, 10/263)

An tambayi Shaykh Abdul-Azeez bin Baaz (rahimahullah) akan mutumin da aka ɗebi jininsa da rana a Ramadan saboda ayi gwaji?
Sai ya amsa da cewa: Irin Wannan gwaji (test) baya karya azumi, Allah yana yafe masa, domin abu ne na larura, kuma baya cikin Ababen da aka sani cewa suna karya azumi.
(Fataawa Islamiyyah, 2/133)

Shaykh Ibn Jibrin yace: Idan Mutum ya bada jininsa, kuma aka ɗebi jini mai yawa, Wannan yana karya azuminsa, a qiyasance kamar yin qaho (Hijaamah) ne, shine sanya jini ya gudana a jijiyoyi a fito dashi domin sauqaqa wani ciwo ko kuma a ajiye shi domin amfani na gaggawa. Amma idan jinin da aka ɗiba ɗan kaɗan ne, Toh wannan baya karya azumi, kamar jinin da ake ɗiba da allura domin yin gwaji.
(Fataawa Islamiyyah, 2/133)

WALLAHU A'ALAM

Zauren Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah. Ku kasance Damu...
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇
https://t.me/TambayaDaAnsa

ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ

Tambaya Da Amsa Mun Buɗe wannan Channel ne domin Amsa Tambayoyin Al'ummar Musulmi baki ɗaya. Duk mai tambaya zaibi Admin ta private.

Tambaya Da Amsa 20/03/2024

TAFIYA TA K**A NI A TSAKIYAR YINI, KO ZAN IYA KARYA AZUMINA ?
:
𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
:
Assalamu Alaikum. Mutum ne zai je Umara cikin Azumi, sai ya zama jirginsu zai tashi ƙarfe biyu na ranar, shin zai kame baki ne daga safe zuwa lokacin tashin ko kuwa ba zai yi Azumi ba kwata-kwata a ranar?
:
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
:
Wa alaikum assalam. Zancen mafi yawan Malaman Hanafiyya da Malikiyya da Shafi'iyya shine: Idan mutum yayi tafiya a tsakiyar yini, to ba zai ci abinci ba, saidai idan ya shiga wahalar da ba zai iya jurewa ba. Amma a wajan Malaman Hanabila ya halatta, saboda Allah ya halattawa matafiyi cin abinci a suratul Baƙara kuma bai bambanta tsakanin wanda yayi tafiya a farkon yini ba da wanda yayi a tsakiya.
Don neman ƙarin bayani duba: Al'insaf, 3/205

Allah ne mafi sani.

Dr. Jamilu Yusuf Zarewa

Zauren Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah. Ku kasance Damu...
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇
https://t.me/TambayaDaAnsa

ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ

Tambaya Da Amsa Mun Buɗe wannan Channel ne domin Amsa Tambayoyin Al'ummar Musulmi baki ɗaya. Duk mai tambaya zaibi Admin ta private.

Tambaya Da Amsa 20/03/2024

SHIN CIN NAMAN MUTANE DA ZAGI SUNA KARYA AZUMI?
:
𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
:
Shin, Cin naman mutane (yi da mutum) da zagi suna daga abubuwan da ke ɓata azumin mutane?
:
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
:
Yi da mutum, baya cikin abubuwan da su ke ɓata azumi, Shi ne kuma: ambaton mutum da abinda ya ke qi, saboda faɗinsa Mabuwayi da ɗaukaka:

يَا أَيُّهَا الَّذِينَ آمَنُوا اجْتَنِبُوا كَثِيرًا مِّنَ الظَّنِّ إِنَّ بَعْضَ الظَّنِّ إِثْمٌ ۖ وَلَا تَجَسَّسُوا وَلَا يَغْتَب بَّعْضُكُم بَعْضًا ۚ أَيُحِبُّ أَحَدُكُمْ أَن يَأْكُلَ لَحْمَ أَخِيهِ مَيْتًا فَكَرِهْتُمُوهُ ۚ وَاتَّقُوا اللَّهَ ۚ إِنَّ اللَّهَ تَوَّابٌ رَّحِيمٌ
Yã kũ waɗanda s**a yi ĩmãni! Ku nĩsanci abu mai yãwa na zato. Lalle sãshen zato laifi ne. Kuma kada ku yi rahõto, kuma kada sãshenku yã yi gulmar sãshe. Shin, ɗayanku nã son yã ci naman ɗan'uwansa yanã matacce? To, kun ƙĩ shi (cin nãman). Kuma ku bi Allah da taƙawa. Lalle Allah Mai karɓar tũba ne, Mai jin ƙai. (suratul Hujurat Aya ta 12)

Haka kuma annamimanci da zagi da karya dukkansu basa cikin abubuwan da su ke ɓata azumi, Sai dai manya-manyan saɓo ne wanda ya zama wajibi a kiyaye su, mai azumi da wanda ba mai azumi; su nisance su ba, kuma lallai suna kawo gibi ga azumi, kuma su rage masa ladansa; wannan kuma saboda fadin Manzon Allah (Sallallahu alaihi Wasallam): "Duk wanda bai bar zancen karya da aiki da shi, da wauta ba, to Allah bashi da buqatar ya bar cin abincinsa, da abin shansa" Bukhariy ya rawaito shi a sahihinsa.

Da kuma saboda faɗinsa: "Azumi garkuwa ne, idan ranar azumin ɗayanku ya zo, to kada ya yi batsa b***e jima'i, kada kuma ya yi shewa, idan wani ya zage shi, ko ya nemi faɗa da shi, to ya ce: Ni mai azumi ne" Bukhariy da Muslim s**a ruwaito. Kuma Hadisai kan wannan mas'ala suna da yawa.
MAJMU'U FATAWA WA MAKAALAAT MUTANAWWI'AH, (15/ 320).

ALLAH NE MAFI SANI.

Zauren Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah. Ku kasance Damu...
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇
https://t.me/TambayaDaAnsa

ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ

Tambaya Da Amsa Mun Buɗe wannan Channel ne domin Amsa Tambayoyin Al'ummar Musulmi baki ɗaya. Duk mai tambaya zaibi Admin ta private.

30/12/2023

No missed salah in 2024, in sha Allah

Want your school to be the top-listed School/college in Jalingo?

Click here to claim your Sponsored Listing.

Location

Category

Website

Address


Jalingo