Nurrul bayan
Darulfikr Qur'an
Gembu brance
18/04/2025
Islam
Annabi muhammadu
16/06/2023
12/06/2023
Ya Allah muna rokonka kakarba mana ibadinmu Ya Allah kakarbana wannan ibadan damuke gabatarwa ya allah kakarbama ayyukanmu na alkhairi kayafemana wanda mukayima kuskure kashiryamu damuda sauran yan uwanmu musulmai kayayemana kuncin duniya da lahira kashigemana gaba ranar gobe kiyama kasakamu a gefen fiyayyen halitta annabi muhammadu s.
Kungiyar Izala tayi kira ga maniyyata aikin hajji da su zama jakadu na gari.
Kungiyar wa'azin musulunci, mai kira a tsaida sunnah, a kawar da da bidi'a, a tarayyar Najeriya, (JIBWIS), tayi kira ga maniyyata aikin hajji da su zama jakadu na gari yayin gudanar da aikin Hajji da saurar ziyarori da shari'a ta shar'nta a lokacin zaman makkah da madina.
Shugaban kungiyar, Sheikh Abdullahi Bala Lau ne yayi wannan kira a garin jimetan jihar Adamawa, ya kara da cewa dan Najeriya mutum ne mai daraja a ko wace kasa dake fadin duniyar nan, ya zama wajibi ga mahajjatan mu da suyi kokarin tsare mana wannan kima da muke da ita.
Shehin Malamin yace ko wane mahajjaci ya kiyayi shiga kasar saudiyya da abubuwan da kasar ta hana, kuma maniyyata su baiwa jami'an tsaron mu na gida hadin kai a filayen jiragen sama dake fadin kasar, irin su NDLE, Kwastam, da dai sauran su a lokacin tantancewa kafin shiga jirgi.
Sheikh Bala Lau, ya sake jan hankalin Alhazai da dagewa da ibada, musamman a manyan masallatai masu alfarma na Makkah da Madina, domin saduwa da lada mai tarin yawa da Allah ya ware a wadannan masallatai masu daraja. Sheikh yace; Hadisi daga Jabir Dan Abdullah Allah ya karamasa yarda yache Annabi (S.A.W) yace: SALLAH A CHIKIN WANNAN MASALLACHI NAWA (MASALLACIN MADINA) YAFI SALLAH DUBU ACHIKIN WANI MASALLACHIN DA BA SHI BA, SAI DAI MASALLACHIN HARAMI NA MAKKA, (MASALLACIN KA'ABA), DUK WANDA YAYI SALLAH A CHIKIN MASALLACHIN KA'ABA NA MAKKA YANA DA LADA DUBU DARI (100,000). Ibn Maja:1406. Dan haka Alhazai a dage da salloli a wadannan masallatai matukar kana da lafiya.
Hakazalika Shugaban na IZALA yaja hankalin Mahajjata da suyi addu'oi akan Allah ya taimaki wannan sabuwar gwamnati na sabon shugaban Naijeriya, Alhaji Bola Ahmad Tinubu da mataimakinsa Alhaji Kashim Shettima. Sheikh Bala Lau yayi addu'oin Allah ya musu jagora akan daidai, ya kuma albarkaci kasar mu baki daya, ya zabo musu wazirai na gari masu gaskiya da rikon amana, wajen ganin sunyi nasara a dukkan abun da s**a a gaba ga kasar mu na alkhairi.
A karshe Sheikh Bala Lau Ya karkare da addu'oin Allah ya kai duk wadanda basu samu zuwa sunyi Hajji ba, wadanda s**a samu zuwa kuma, Allah ya mai da su. Allah yasa ayi aikin Hajji karbabbe, ya bada lafiyar gudanar da aikin ga maniyyata.
JIBWIS NIGERIA 🇳🇬
06/06/2023
Amsoshin tambayoyin ku da kuka aiko
Tare da Prof. Muhammad Sani Umar Rijiyar Lemo Hafizahullah
Shirin da yake amsa tambayoyin da kuka aiko zuwa cikin shirin Fatawoyin Rahma Daga Gidan Radio Na Rahma Radio Kano
Cikakken Bayani mai muhimmanci danna link 👇
https://youtu.be/2AtRwiaQIZ4
Ayi sauraro lafiya
Amsoshin tambayoyin ku da kuka aiko zuwa ga Prof. Muhammad Sani Umar Rijiyar Lemo
Click here to claim your Sponsored Listing.
Location
Category
Address
Taraba
Jalingo