Maj'lisut Ta'alimil Islamiy

Maj'lisut Ta'alimil Islamiy

Share

Majalisut Ta'alim Islamiy is a youth-led Islamic channel focused on education, faith, and moral development through learning and da'wah.

19/08/2026

Wannan Yarinnyan Sunanta Maryam Ibrahim Dan’azumi daga Jihar Gombe, wadda ta zo ta ɗaya a international Musabaka sashen Tafsiri na mata na Hizb 60, ta samu kyautar Riyal 300,000 na Saudiyya, wanda ya yi daidai da kimanin Naira Miliyan 120,000,000 a kuɗin Najeriya.

Wannan babbar nasara ce ga Jihar Gombe da Najeriya baki ɗaya.Allah yasa Al barka

19/08/2026

Allah ya Jiqan Sheikh Jafar Mamod Adam Rahimahullah 😘 Ance Wannan Wasiqa Ne Daya Rubutawa Yar Shi Malama Zainab Ja’afar Mahmud Lokacin Dake Karatu A Sudan, Amma Kuma Naje Shafin Ta Na Gama Dubawa Banga Komai Ba, Duk Dai Ban Sani Ba Ko Posting Din Ya Jima Bane 🥲

👇👇👇👇
CIKAKKEN BAYANI KAN WASIKAR SHEIK JA'AFAR

Daga, Zainab Ja'afar Mahamud" Allahu Akbar...!

Wata Wasika Mai Kwanan Watan 3\2\2002 da Marigayi Sheikh Ja'afar ya rubutawa, yarsa Zainab ja'afar Mahmud, a lokacin da yake karatu a sudan. Ga abunda ita zainab ta rubuta a shafin ta ku karanta.

Shekaru 19 kenan da watanni mahaifina ya rubuto min wasikar nan daga qasar Sudan, lokacin yana karatun shi na masters degree a can.
Yau babu zato babu tsammani na ci karo da ita cikin wasu tsofaffin littafaina, ina karantawa sai na ke jin ina ma ina da damar da zan sake samun irin wannan wasika daga gareshi yanzu amma inaa!! Sai nake jin kamar yanzu ne ya rubuto min ita saboda gamammun sakonnin da ke cikinta da zansu amfane ni tsawon rayuwata.

Ina karantawa cike da tunanin irin yadda rayuwata ta kasance da shi a wancan lokutan, na yi rayuwa mai cike da kulawa, gata, tarbiyyantarwa, bada kariya, ilimantarwa, uwa uba kuma kauna ta musamman daga gareshi wadda ba zan taba mantawa da ita ba har na koma ga Allah😭😭

Ga Wasikar Malam \

Assalamu alaikum wa rahmatullah

Dafatan kina lafiya, yaya karatu? Ina fatan komai yana tafiya Kamar yadda ake fata,

Ina farin cikin sanar da ke cewa na isa Sudan cikin aminci da koshin lafiya, Amma kuma zan sake komawa Saudiyyah a karo na biyu domin yin aikin hajji,

Ina yi miki Wasiyya da TSORON ALLAH, a sarari ko a boye, ina kuma yi miki Wasiyya da yawaita TULAWAR AL'QUR'NI. Tare da kiyaye SALLOLIN FARILLAH, a kan lokaci, da kuma HIMMA wajen neman ILIMI da kuma HARDAR AL'QUR'NI

Haka nan kuma ina yi miji nasiha da BIYAYYA ga MAHAIFIYARKI da hakurin mu'amala da kannenki

Insha allahu zan dawo gida bayan aikin hajji

Na barki lafiya

Mahaifinki
Ja'afar Mahamud Adam
Khartoum Sudan.

Lallai rashin mahaifi babban gibi ne da babu mai iya cike wa mutum shi har abada!!!

Ubangiji Allah Ka ji kan mahaifanmu da s**a rasu Ka sanya Aljanna ce makomarsu,

wadanda suke raye kuma ka kara musu lafiya da imani da tsawon kwana mai amfani amin.

Copied.

19/08/2026

Yadda akayiwa Malam Albani Asiri

11/08/2026

Abin Alfahari 🥰🇳🇬| Waɗannan Mutanen Biyu Wakilan Nigeria 🇳🇬🔥 Sun Fidda Nigeria Kunya A Gaban idon Duniya 🌎✊ Dukkansu Sunyi Karatu Na Ƙwarewa Da Cikakkiyar Nutsuwa 👏 Muna Roqon ALLAH 💪 Yasa Muji ALKHAIRI 🤲

11/08/2026

Abdulmalik Muhammad Inuwa

Tambayoyin Addiraya

10/08/2026

Abdulmalik Muhammad Inuwa

International Musabaka (Qur'anic Recitation Competition)
Complete Video 💯 📸 💯

Riwayat

09/08/2026

Kissar Annabi Musa A.S

08/08/2026

Goni Abdulmalik Muhammad Inuwa Gassol Tare da Sauran Wakilan Nigeria a Airport,
Sunyi boarding, nan da 1:30pm agogon Nigeria zasu Tashi.

Allah ya tsare hanya 🙏

Yana Godiya da Adduoi yanuwa

08/08/2026

Halaccin Istimna'i

02/08/2026

Haramcin Cin Hanci da Rashawa

Want your school to be the top-listed School/college in Jalingo?

Click here to claim your Sponsored Listing.

Location

Category

Telephone

Website

Address


Majidadi Ward Saurara Behind Anguwan Izala Baba Adda Place
Jalingo
660001