19/08/2026
Wannan Yarinnyan Sunanta Maryam Ibrahim Dan’azumi daga Jihar Gombe, wadda ta zo ta ɗaya a international Musabaka sashen Tafsiri na mata na Hizb 60, ta samu kyautar Riyal 300,000 na Saudiyya, wanda ya yi daidai da kimanin Naira Miliyan 120,000,000 a kuɗin Najeriya.
Wannan babbar nasara ce ga Jihar Gombe da Najeriya baki ɗaya.Allah yasa Al barka
19/08/2026
Allah ya Jiqan Sheikh Jafar Mamod Adam Rahimahullah 😘 Ance Wannan Wasiqa Ne Daya Rubutawa Yar Shi Malama Zainab Ja’afar Mahmud Lokacin Dake Karatu A Sudan, Amma Kuma Naje Shafin Ta Na Gama Dubawa Banga Komai Ba, Duk Dai Ban Sani Ba Ko Posting Din Ya Jima Bane 🥲
👇👇👇👇
CIKAKKEN BAYANI KAN WASIKAR SHEIK JA'AFAR
Daga, Zainab Ja'afar Mahamud" Allahu Akbar...!
Wata Wasika Mai Kwanan Watan 3\2\2002 da Marigayi Sheikh Ja'afar ya rubutawa, yarsa Zainab ja'afar Mahmud, a lokacin da yake karatu a sudan. Ga abunda ita zainab ta rubuta a shafin ta ku karanta.
Shekaru 19 kenan da watanni mahaifina ya rubuto min wasikar nan daga qasar Sudan, lokacin yana karatun shi na masters degree a can.
Yau babu zato babu tsammani na ci karo da ita cikin wasu tsofaffin littafaina, ina karantawa sai na ke jin ina ma ina da damar da zan sake samun irin wannan wasika daga gareshi yanzu amma inaa!! Sai nake jin kamar yanzu ne ya rubuto min ita saboda gamammun sakonnin da ke cikinta da zansu amfane ni tsawon rayuwata.
Ina karantawa cike da tunanin irin yadda rayuwata ta kasance da shi a wancan lokutan, na yi rayuwa mai cike da kulawa, gata, tarbiyyantarwa, bada kariya, ilimantarwa, uwa uba kuma kauna ta musamman daga gareshi wadda ba zan taba mantawa da ita ba har na koma ga Allah😭😭
Ga Wasikar Malam \
Assalamu alaikum wa rahmatullah
Dafatan kina lafiya, yaya karatu? Ina fatan komai yana tafiya Kamar yadda ake fata,
Ina farin cikin sanar da ke cewa na isa Sudan cikin aminci da koshin lafiya, Amma kuma zan sake komawa Saudiyyah a karo na biyu domin yin aikin hajji,
Ina yi miki Wasiyya da TSORON ALLAH, a sarari ko a boye, ina kuma yi miki Wasiyya da yawaita TULAWAR AL'QUR'NI. Tare da kiyaye SALLOLIN FARILLAH, a kan lokaci, da kuma HIMMA wajen neman ILIMI da kuma HARDAR AL'QUR'NI
Haka nan kuma ina yi miji nasiha da BIYAYYA ga MAHAIFIYARKI da hakurin mu'amala da kannenki
Insha allahu zan dawo gida bayan aikin hajji
Na barki lafiya
Mahaifinki
Ja'afar Mahamud Adam
Khartoum Sudan.
Lallai rashin mahaifi babban gibi ne da babu mai iya cike wa mutum shi har abada!!!
Ubangiji Allah Ka ji kan mahaifanmu da s**a rasu Ka sanya Aljanna ce makomarsu,
wadanda suke raye kuma ka kara musu lafiya da imani da tsawon kwana mai amfani amin.
Copied.
11/08/2026
Abin Alfahari 🥰🇳🇬| Waɗannan Mutanen Biyu Wakilan Nigeria 🇳🇬🔥 Sun Fidda Nigeria Kunya A Gaban idon Duniya 🌎✊ Dukkansu Sunyi Karatu Na Ƙwarewa Da Cikakkiyar Nutsuwa 👏 Muna Roqon ALLAH 💪 Yasa Muji ALKHAIRI 🤲
08/08/2026
Goni Abdulmalik Muhammad Inuwa Gassol Tare da Sauran Wakilan Nigeria a Airport,
Sunyi boarding, nan da 1:30pm agogon Nigeria zasu Tashi.
Allah ya tsare hanya 🙏
Yana Godiya da Adduoi yanuwa