Jibwis Jakusko,

Jibwis Jakusko, Contact information, map and directions, contact form, opening hours, services, ratings, photos, videos and announcements from Jibwis Jakusko,, Tutor/Teacher, Jakusko.

09/02/2022

GAYYATA GAYYATA

Assalamu Alaykum.

Ana Gayyatar Dukkanin Yan uwa musulmai Na cikin garin Jakusko Da kewaye zuwa Wurin Karatu na Lecture da SHEIKH DR MUHAMMAD RABIU COLLEGE, Zai gabatar anan cikin garin Jakusko.
Venue = Central Masjid Na Bakin kwalta.
Time= Bayan Magrib.
Allah ya bada ikon halarta.

Sanarwa
Director JSM Jakusko
Laminu Alhaji Ibrahim.

03/01/2019
23/11/2018

ASSALAMU ALAYKUM YAN UWA MUSULMI.

01/11/2018

ALHAMDULILLAH WE ARE NOW AVAILABLE.

19/10/2015

MANUFAR KAFA KUNGIYAR # IZALA A NIJERIA DA SAURAN
KASASHE!!!
Kungiyar kawar da Bidi’ah da tsayar da Sunnah.
Dandalin mu na # Jibwis # Nigeria ya dan waiwaya baya
kadan ya gutsuro muku wasu daga cikin manufofin kafuwar
kungiyar tun asali.
Wannan qungiya ta al’ummar musulmi an kafa ta ne tun a
shekarar 1978 a Najeriya, kuma shugabanta na farko shi ne
Alhaji Musa Maigandu Muhammad, a qarqashin kulawar
Malam Abubakar Mahmud Gumi, tare da Sheikh Isma’il Idris
bn Zakariyya, a matsayin shugaban majalisar malamai na
farko na kungiyar.
Wannan Kungiya ta musulunci ce, wacce musulmi s**a
kafa kuma tana da hedkwata a Jos, Jihar Pilato, Sannan
tana da liaison office a Babban birnin tarayya Abuja, inda
anan ne ofishin Shugaban ta na kasa yake a halin yanzu,
kungiyar bata da alaka ko wace iri ce, da wata kungiyar
asiri, darika ko kuma kungiyar Siyasa.
Wannan kungiya tana kan tafarkin musulunci ne wanda ta
dogara ga Qur’ani da hadisan Annabi Muhammad (SAW)
Bisa fassarar Magabata. Babu bambanci a cikin kungiya in
dai har mutum musulmine da yayi Imani da ‘Allah’ kamar
yadda Annabi Muhammad (SAW) ya karantar. Kungiya na
maraba da irin wannan mutum da kuma shawarwarinsa
masu amfani wadanda s**a dace da musulunci.
Qungiyar ita ce irinta ta farko a tarihin yada addinin
musulunci a Najeriya, hadi da harkar ilmantarwa, tare da
daukaka darajar harkokin addinin Musulunci ba tare da
wani tsoro ba. Don haka ne sai kungiyar ta sanya wasu
ginshiqan # MANUFOFI da take so ta cimma domin kai wa
Ga gaci.
Daga cikin muhimman manufofin wannan kungiya sun hada
da:
- Kawar da duhun jahilci daga cikin al’umma, wanda ya yi
wa al’umma katutu.
- Hada kan al’ummar musulmi a bisa koyarwar Alqur’ani da
Sunnar Manzon Allah (SAW),
- Wayar da kan al’ummar musulmi game da al’amuran
addini, domin a gudu tare a tsira tare.
- Fadakar da al’ummar musulmi domin a yi watsi da wasu
miyagun littattafai da suke tura mutane cikin halaka.
- Tabbatarwa da cewa Annabi (SAW) ya kammala isar da
sakon Allah (SWT).
- Duk wanda ya yi da’awar annabta, ko kuma yake riya
cewa Annabi (SAW) yana ziyartarsa da wani sako, to
wannan zunzurutun makaryaci ne.
- Yada Musulunci a Najeriya da wajen Najeriya.
- Yin da’awa a kan fadin Manzon Allah (SAW) cewa: “duk
wanda ya ga abin qi, to ya sauya shi da hannunsa, idan ba
zai iya ba, to da harshensa, in ba zai iya ba, to da
zuciyarsa, amma wannan shi ne mafi raunin imani.”
- Kar a boye hujja in dai har ta tabbata daga littafin Allah
Madaukakin Sarki, ko sunnar Manzon Allah (SAW).
Wasu daga cikin ayyukan kungiyar sun Hada da:
Kasancewar wannan kungiya ta shahara sosai a kasashe
daban-daban na duniya, wannan ya sa aka samar da
kwamitoci daban-daban domin gabatar da ayyuka da yawa.
Kadan daga cikin kwamitocin kungiyar sun hada da:
- Kwamitin Da’awah.
- Kwamitin Ayyuka.
- Kwamitin Kula da Marayu
- Kwamitin Ilimi.
- Kwamitin Sulhu da fatawa da ladabtarwa.
- Kwamitin Taimakon Gaggawa.
-Kwamitin Masallatai.
-Kwamitin MANARA.
-Kwamitin yanar Gizo.
-kwamitin yada labarai
Da Sauran wasu kwamitoci.
Shugaban kungiyar IZALA na kasa a wannan lokaci shi ne
Ash-Sheikh Imam Abdullahi Bala Lau, khalifa na farko a
sashin Shugabancin kungiyar tun bayan kafa ta, wanda
tsohon mataimakin shugaban kungiyar ne bayan rasuwar
Marigayi Sheikh Imam Ikara, duk a lokacin zamanin
shugabancin marigayi Alh. Musa maigandu Muhammad,
kuma ya gaji shugabancin kungiyar ne bayan rasuwar
Shugaba Musa Maigandu Muhammad.
- Sheikh Usman Isah Taliyawa Gombe: Mataimakin
Shugaban Kungiya Na Kasa na daya.
-Sheikh Abbas Muhammad Jega: Mataimakin Shugaban
Kungiya na kasa na biyu.
- Sheikh Muhammad Kabir Haruna Gombe: Babban
Magatakardan kungiyar na kasa.
- Sheik Dr. Ibrahim Jalo Jalingo: Shugaban Majalisar
Malamai na kasa.
- Sheik Barrister Ibrahim Sabi'u Jibia: Mataimakin Shugaban
Majalisar Malamai na Kasa.
- Engineer Mustapha Imam Sitti: Shugaban Rundunar Yan
Agaji na Kasa
- Alhaji Muhammad Kabir Sa'id Gusau: Mataimakin
Shugaban Rundunar Yan Agaji na kasa a bangaren (Training
and operation)
-Alhaji Abdullahi A. Diggi: Mataimakin Shugaban Rundunar
Yan Agaji na kasa a bangaren (Admin and Finance)
kungiyar ta samu karbuwa a sassa daban-daban na duniya.
A Najeriya tana da rassa a dukkanin jihohin Najeriya 36 da
birnin tarayya Abuja. Haka kuma saboda irin yadda
kungiyar take kokarin ilmantar da al’umma, wannan ya sa
har ta sami kutsawa zuwa ga wasu kasashe, kamar su;
Kasar Saudi Arabia, Amurka, Ingila, Nijer, kotonu, Mali,
Senegal, Togo, Kamaru, Chadi, Burkina faso, Gini, da
sauransu.
Wasu daga cikin abubuwan da kungiyar ta mayar da hankali
wajen yin su, sun hada da:
- Koyarwa a bisa tafarkin Manzon Allah (SAW) ba tare da
bin son zuciya ko kuma yin makauniyar biyayya ga wani ba.
- Tsantsar karantar da hakikanin ilimin addinin Musulunci.
- Gabatar da wa’azin kasa a duk makwanni Uku ko hudu
don tunatar da mutane abin da s**a manta ko kuma lokutan
da s**a dace.
- Kafa makarantu domin koyar da ilimin addini da na boko,
da sauran fannonin ilimi.
- Kai Ziyara Zuwa gidajen marayu, fursina da asibitoci,
domin tallafawa musulmai marasa galihu.
- Samar da taimakon gaggawa a duk lokacin da bukatar
hakan ta taso.
kungiyar ta samar da hamshaqan malamai a sassa
wadanda s**a sami daukaka ta ilimi a fadin duniya baki
daya, saboda jajircewa da kokarin bin tafarkin Manzon
tsira, Annabi Muhammad (SAW), sau da kafa.
Dan haka nema kungiyar take rubuta "LAA ƊAA'ATA
LIMAKHLUƘIN FII MA'ASIYATIL KHALIƘI." A dukkan
kadarorinta data Mallaka, irin su motoci da sauran su, Tun
farkon kafa kungiyar har zuwa yau dinnan kungiyar bata
chanza ba.
Haka kuma ta ko wacce fuska tarihin izala zaizo dogo ko
gajere, ba za a taba mantawa da irin gudummar da
marigayi Sheikh Isma'ila Idris Ibn Zakariyya (Shugaban
Majalisar Malamai na farko) ya bayar dan kafuwar wannan
kungiya mai albarka ba, da irin Su Marigayi Sheikh
Abubakar Mahmud Gumi, Marigayi Sheikh Ibrahim Bawa
Maishinkafa, Marigayi Sheikh Hudu Chikaji Zariya, Marigayi
Sheikh Adam Mai Shafi, Marigayi Sheikh Abubakar Imam
Ikara, Marigayi Sheikh Musa Maigandu Muhammad da
Marigayi Alhaji Ali Ibrahim Tofa (Tsohon Shugaban yan
agaji na kasa), koda Kuwa ba manufarmu mu zayyana
sunan kowa ba.
Suma sauran Matasan Malaman da a baya s**a bada
Gudunmawar su dan kungiyar ta cimma manufofinta,
wanda a yanzu sun zama Dattawa, a farkon tafiya gashin
su baki ne, amma yanzu ya rikide ya zama fari sol, kuma
ba'a daina yin wa'azin ba, irin su Sheikh Dr. Alhassan Sa'id
Adam jos, wanda shine Alaramman kungiyar na farko mai
jan baki a bisa mimbari yayin wa'azi, da Sheikh Yakubu
Musa Hassan Katsina, wanda a farkon tafiya shine
Mataimakin Shugaban Majalisar Malamai na biyu, Sheikh
Rabi'u Aliyu Daura, Sheikh Usman Isah Taliyawa Gombe,
Sheikh Abbas Muhammad Jega, Alaramma Abubakar Adam
Katsina da da Sheikh Habibu Yahaya Kaura wanda ake
masa lakabi da dan autan masu wa'azi, sabo da kankantar
sa, gashi yanzu shekaru sun cimmasa, da sauran wadanda
suke raye ake fafatawa da su a halin yanzu.
Daga karshe Muna addu'a ga dukkan wadanda s**a
sadaukar da dukiyoyin su da kuma rayukansu akan wannan
harka taci gaban addini, Allah ya saka musu da gidan
Aljanna ya hada mu dasu a babban matsayi a lahira. Amin.

01/10/2015

HAJJIN BANA!
30/09/2015 JIRGIN MAX AIR MAI LAMBA VM2010 YA
TASHI DAGA FILIN JIRGIN SAMA NA JEDDAH DA ALHAZAN
JAHAR SOKOTO DA ZAMFARA DA MISALIN KARFE 10:00
YA KWASHI MAHAJJATA 530
30/09/2015 JIRGIN FLYNAS MAI LAMBA XY8904 YA TASHI
DAGA FILIN JIRGIN SAMA NA JEDDAH DA ALHAZAN
JAHAR KADUNA DA PLT DA MISALIN KARFE 13:45 YA
KWASHI MAHAJJATA 292
30/09/2015 JIRGIN MEDVIEW MAI LAMBA VL3219 YA
TASHI DAGA FILIN JIRGIN SAMA JEDDAH DA ALHAZAN
JAHAR LAGOS DA OSUN DA MISALIN KARFE 19:15 YA
KWASHI MAHAJJATA 323
30/09/2015 JIRGIN MAX AIR MAI LAMBA VM2014 YA
TASHI DAGA FILIN JIRGIN SAMA NA JEDDAH DA ALHAZAN
JAHAR SOKOTO DA DA ZAMFARA DA MISALIN KARFE
21:35 TA KWASHI MAHAJJATA 530
01/10/2015 JIRGIN MEDVIEW MAI LAMBA VL3217 YA
TASHI DAGA FILIN JIRGIN SAMA NA JEDDAH DA ALHAZAN
JAHAR LAGOS DA OSUN DA MISALIN KARFE 00:25 YA
KWASHI MAHAJJATA 201
01/10/2015 JIRGIN MAX AIR MAI LAMBA VM2016 YA
TASHI DAGA FILIN JIRGIN SAMA NA JEDDAH DA ALHAZAN
JAHAR GOMBE DA MISALIN KARFE 05:43 YA KWASHI
MAHAJJATA 554
ZUWA YANZU ADADIN ALHAZAN NAJERIYA DA S**A
DAWO GIDA YA KAI ADADIN MUTUM 7, 305.

24/09/2015

Ass. mun gabatar da sallah lafia anan garin jakusko in banda ruwan sama da ya sakko ya hana gabatar da khuduba a filin idin. Allah ya maimaita mana ameen.

22/09/2015

Mahajjatan Nijeriya 20 Ne S**a Rasu A
Makkah
Hukumar kula da mahajjata a Nijeriya a yau
Latinin ta tabbatar da cewa kimanin
mahajjatan Nijeriya ashirin ne s**a rasu a
kasar Saudiyya tun daga lokacin da aka
soma gudanar da ibada a bana.
Shugaban hukumar, Alhaji Abdullahi
Mukhtar, shi ya bayyana hakan a taron
gudanar da Arfa da aka yi a garin Jeddah.
Ya ce sha hudu sun rasu ne sakamakon
kamuwa da ciwo yayin da shida s**a rasa
ransu a hadarin masallacin Ka'aba. Inda
kuma uku daga cikin su s**a samu rauni

18/09/2015

Ass. Muslim brothers an sisters needs ur Pryer. we are in jibwis social media metting prsnt now.

16/09/2015

Jibwis Nigeria
IZALA APPLAUDS SAUDI GOVERNMENT
OVER STEPS TO COMPENSATE VICTIMS OF
THE RECENT CRANE CRASH AT HARAM
This was contained in a statement signed by
the national chairman of the organization,
sheikh Abdullahi Bala Lau. The chairman
further commended the efforts of king Salman
for taking urgent and commendable steps of
which include, the compensation fee of
1Million Saudi Riyals (equivalent to
60Million Nigerian Naira) for the families of
the victims who either lost their lives or
sustained severe injuries,while 500Million
Riyals (equivalent to 30Million Nigerian
Naira) will be given to the victims who
sustained partial injuries. The Saudi
authorities further directed that 2 relatives of
the victims that died be sponsored to perform
Hajj . The statement from saudi authorities
added that a certain number of relatives of
the injured victims are allowed to visit the
hospital to console them.It was also
gathered that King Salman has ordered an
immediate halt of contracts earlier awarded
to the Ben Laden Contractors handling the
projecs within the Haram complex as
investigations have revealed that the
company may share part of the blame for the
tragedy.
Shaikh Lau, added that this kind gesture by
the saudi authority under king Salman is
worthy of commendation and emulation as it
advocates Justice and fairness to victims.
On the concluding point, The JIBWIS national
chairman, Shaikh Abdullahi Lau, offered
special prayers to the departed souls and
fast recovery to the hospitalized.He also
prayed that Almighty Allah will protect the
entire pilgrims to perform sound hajj and
return home safely.
Sheikh Abdullahi Bala Lau
02/Dhul-Hijjah/1436
16/September/2015 — with Shuaib

03/09/2015

In sha Allahu Ta'ala gobe Juma'ah 20/11/1436
H, 4/9/2015 M Kungiyar Jama'atu Izalatil
Bid'ah Wa Iqamatis Sunnah (JIBWIS) za ta
bude sabon masallacin Juma'ah a unguwar
Tafare, a bayan Primary Board cikin garin
Jalingo.
Muna rokon Allah Madaukakin Sarki da Ya
taimake mu Ya yada wannan Addini namu na
Musulunci cikin ko wane lungu na Duniya, Ya
kuma tausaya wa wannan Al'ummah Islamiyyah
Ya cusa son yin aiki da sunnar manzon Allah
mai tsira da amincin Allah cikin zukatansu a
cikin dukkan wata Ibadah da shar'anta masu.
Ameen.

Address

Jakusko

Telephone

+2347067945800

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Jibwis Jakusko, posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Shortcuts

Share

Category