03/07/2025
Assalamu alaikum Yan uwa π€
Inaso na sanarwar yan uwa cewa na janje kalamai na da nayi a baya nacewa bazan sake yin zabe ba.
A baya na yanke wannan hukunci ne, saboda yadda yan uwa suke sayar da yan cinsu alokutan zabe, abun baya mini dadi shiyasa ma har na yake cewa na hakura da zabe.
Dalilan da s**a sa na janye kalamai na da kudurina, su ne da yawa daga cikin yan uwa da abokai da suke bi biyan rubutuna sun ja hankali na da tunatar da ni sosai akan kalamai na kuma na fahimcesu matuka, shiyasa na janye kalamai na.
Shi gwagwarmayar da kawo canji ba zai yu ba sai da hakuri, juriya da jajircewa, in sha Allah na lashi takobin gwagwarmaya, da yardan Allah sai mun kawo canji a wannan kasa ta mu mai albarka.
Daga karshe Ina godiya sosai ga yan uwa da abokai na da s**a tunatar dani, Allah ya bar xumunci πππ
Comr Usman Abdullahi Umar βοΈ
β
β
03/07/2025
03/07/2025
24/06/2025