Fassarar Al-qur'ani Da Hausa

Fassarar Al-qur'ani Da Hausa

Share

Fassarar Al-qur'ani Da hausa

24/05/2022

Fassarar Ayar Qur'an.

Surah An-nisa'i/سورة النساء
Chapter: 4 Verse 136.

بسم الله الرحمن الرحيم
Da Sunan Allah Mai Rahama Mai Jinqai.

يَا أَيُّهَا الَّذِينَ آمَنُوا آمِنُوا بِاللَّهِ وَرَسُولِهِ وَالْكِتَابِ الَّذِي نَزَّلَ عَلَى رَسُولِهِ وَالْكِتَابِ الَّذِي أَنْزَلَ مِنْ قَبْلُ وَمَنْ يَكْفُرْ بِاللَّهِ وَمَلَائِكَتِهِ وَكُتُبِهِ وَرُسُلِهِ وَالْيَوْمِ الْآخِرِ فَقَدْ ضَلَّ ضَلَالًا بَعِيدًا
MA'ANA:
Ya ku waɗanda s**a yi imani Ku yi Imani da Allah da Manzonsa, da Littafin da (Allah) Ya sassaukar ga ManzonSa (Muhammad SAW, shine Al-qur'ani) da (Kuma) Littafin nan wanda Ya saukar daga gabanin (sa, wato sune dukkan littafen allah Wanda ya saukar wa annabawa kafin zuwan Annabi Muhammad SAW, misali attaura,linjila,zabura.) To, wanda (Kuma) ya kafirta (ai, yaqi bada Gaskiya) da Allah da mala'ikunSa, da LittattafanSa, da ManzanninSa, da Ranar Lahira, to, lalle ne (wannan bawan) ya ɓace, ɓata mai nisa (ma'ana ai ya nisantar da kanshi daga Allah mahaliccin Shi, amma Kuma ya saurayi zuwan al-amarin Allah agareshi, a Domin kuwa yanada wata irin rayuwa mai kunci a anan duniya da baqin ciki na har abada a lahira)

SHARHINTA ATAQAICE...
shine Bawa ya sani cewa idan ya kuskura yabi wani a anan duniya dasunan wai bauta ko biyayya a gareshi, matuqarde ba Allah ne ba Ubangijin sammai da Qassai to, yayi hasara.

Haka Nan Kuma idan bawa ya bi wani mutum ko ya kwaikayi wani mutum, ba daya daga cikin Annabawan Allah ba Kuma ba Annabin Qarshen zamani ba(wato Annabi Muhammad SAW) to haƙiƙa yayi asarar ayyukan shi tin anan duniya.

Kuma kowa ya k**a ya k**a iska, a domin baze amfaneshi da komaiba aranar tashin Al-qiyama.

Ya Allah ka tsaremana imanin mu ka shiryar damu ka dawwamar damu akan hanyar ka madedeciya, ka Al-qur'ani ya zamo hujja agaremu ba akan muba.
AMINN.

+2348168311092
tambayoyi akan darasi.

18/04/2022

FASSARAR AL-QUR'ANI ME GIRMA.

Surah An-nur/سورة النور
Chapter: 24 Verse 24-26.

بسم الله الرحمن الرحيم
Da Sunan Allah Mai Rahama Mai Jinqai.

Ubangiji Subhanahu wata'ala Yana cewa"
يَوْمَ تَشْهَدُ عَلَيْهِمْ أَلْسِنَتُهُمْ وَأَيْدِيهِمْ وَأَرْجُلُهُمْ بِمَا كَانُوا يَعْمَلُونَ
MA'ANA:
A ranar da harsunansu da hannayensu, da ƙafafunsu suke bayar da shaida a kansu, game da abin da s**a kasance suna aikatawa.(su mushrikai, ko Kuma su kafirai, kode su masu aikata sabo)

Allahu SWT yace"
يَوْمَئِذٍ يُوَفِّيهِمُ اللَّهُ دِينَهُمُ الْحَقَّ وَيَعْلَمُونَ أَنَّ اللَّهَ هُوَ الْحَقُّ الْمُبِينُ
MA'ANA:
A (Wannar) ranar (ne ta Al-qiyama wad) da Allah Yake cika musu sak**akonsu (ai, yake musu hisabin ayyukan su) tabbatacce (da s**a aikata marasa kyau, ya kuma sakankamusu da maras kyau wato shine ya sasu a Wuta) kuma (hakika) suna sanin (cewa) lalle Allah, Shine Gaskiya bayyananna (ai, tabbas suna sanin cewa lalle ne wannan hukuncinda Allah yayi akan su shine dede a Domin sun cancanci ayi musu hakan a Saboda kafircewar su ga Allah da ayoyin shi da manzannin shi da Sukayi a gidan Duniya).

Shine Sai gaba Allah yake cewa"
الْخَبِيثَاتُ لِلْخَبِيثِينَ وَالْخَبِيثُونَ لِلْخَبِيثَاتِ وَالطَّيِّبَاتُ لِلطَّيِّبِينَ وَالطَّيِّبُونَ لِلطَّيِّبَاتِ أُولَئِكَ مُبَرَّءُونَ مِمَّا يَقُولُونَ لَهُمْ مَغْفِرَةٌ وَرِزْقٌ كَرِيمٌ
MA'ANA:
(Sanide kawai su) Miyagun mata domin miyagun maza suke, kuma (su) miyagun maza domin miyagun mata suke (hakanan) kuma tsarkakan mata domin tsarkakan maza suke kuma tsarkakan maza domin tsarkakan mata suke. waɗancan su ne waɗanda ake barrantawa daga abin da (masu ƙazafin nan) suke faɗa (akan matar Annabi SAW Wato syydn Aisha) kuma suna da gafara da arziki na karimci (ma'ana ai su wa 'yanda akayi ƙazafin akan sunada gafara agun Allah kuma da arziqi wato Shi aljanna, ko Kuma su wassu dag sahaban nan wanda s**a rinjaya akan kazafin nan, amma Kuma se daga baya s**a kafimci Gaskiyar magana cewa lalle sayyidina Aisha (Ra) bata aikata wannan abinda ake Fadi ba akanta ba a sak**akon Allah ya saukar da aya ya wanke ta, to su wadannan Suna da gafara ma'ana ai Allah ya gafarta musu sa'annan Kuma sunada wani arziqi ai gidan aljannah)
Wallahu a'alam.

SHARHI ATAQAICE.
wato su wadannan ayoyin Suna fadakarwa gare mu mu Al-ummar Annabi Muhammad SAW, musamman ita wannar aya ta Qarshen inda Allah yake buga mana misali cewa" mu sani Kuma lalle mu hankalta fa mu fahimci su matan kirki fa suna dacene da mazan kirki, Kuma bai yi yuwa ace matar Annabi Muhammad SAW ace anzargeta da aikata fasikanci.

Wato a qarkashin wannar maganar abaya akwai wani abunda ya faru ne awani lokaci sanda Annabi Muhammad SAW ya na tafiya da rundunar shi a domin zuwa daga kalmar Allah, to acikin wannan rundina akwai mata harda matarshi Nana Aisha (RA) se s**a yada zango awani waje a domin hutawa, to shikenan bayan sun huta se akata tashi domin anausa gaba, to ita Nana Aisha adede wannan Lokacin se wani uzuri ya k**ata akace ko zobenta ne ta yasar kode wani abun na lalura, ma'ana de kawai akwai wani uzuri da yasa har akabar Nana Aisha abaya, to dama kuma Idan aka fito da tawaga irin wannar tawaga akan bar wani mutum kuma abaya Wanda aikin shi shine ze ringa kula da abinda ka iya faduwa na jama'ar wannar rundina, to shikenan se shi wannan irin Mutumin da ake Bari abayan sai s**a hadu da ita sayyidina Aisha (Ra) a Sak**ako anbarta abaya.

To shine fa Bayanda s**a taho dashi wannan wanda ake Bari abayan a tare, To dagan shikenan shine fa se kawai munafukai s**a ringa yada jita jita akan cewa ai fasikanci Sukayi dashi wannan Mutumin da ake Bari abayan, daganan har maganar ta isa ga Annabi SAW wadda har shubuha ta sameshi a cikin lamarin, har seda aya ta sauko akayiwa Annabi Muhammad SAW wahayi aka wanke Aisha daga dukkan wani zargi ko shubuha.
Ataqaice taqaitawa de wannan shine abinda ya faru.
Har Allah yace an barranta nana Aisha daga maganar masu ƙazafin nan.

Wato Abin lura anan gabar shine ma'anar Da ita ayar take koyarwa ga Al-ummar Annabi Muhammad SAW, farko de Idan aka samu jarrabawa ta munafikai ko makaryata s**ayi magana akan wani bawa wanda shi bawan mai nagarta ne ansanshi, to tunanin farkode da Ya k**ata ayi akanshi shine k**ar yadda Allah ya buga mana misali acikin ayar, wato mazan kirki Allah yana basu matan kirkine, haka nan mutanen kirki Allah yana hadasu da na kirkine, haka nan idan ko na banza ne Allah yana hadasu dana banzane.

Ma'ana de kawai anasun mu musulmi muminai kasance masu kyautata zato ga junanmu da kyaky-kyawan fata tsakani.
Harsede Idan wani abi ya bayyane a garemu na zargi, to anan Kuma anaso muyi wa junanmu addu'a ta shiriya ba aikatawa ba.

Sai Kuma bayani akan Aya ta farko Wanda ayace da take yi mana Gargadi da Kuma tsorataswa akan cewa lalle Mu sani da akwai wata Rana da hannuwanmu da kafafunmu da harsunan mu zasu bada sheda akanmu a gaban Allah, matuqar de bamu sarrafasu ba ta Yadda Allah yace.

Kuma hakika musani cewa Lalle alkawarin Allah hakanan azaban Allah Gaskiya Kuma tabbas gaske babu ko kwanto a ciki.

Saide kawai mafita guda shine imani da tsayuwa akan imanin, da neman temakon Allah acikin lamuran mu , kana mu ringa yawan tuba da neman gafarar Allah tin kafin lokaci ya kure, wato tin kafin wata Rana tazo Mana wadda zamu koma ga mahaliccin mu shine Allah.
WALLAHU TA'ALA A'ALAM.

Ya Allah Kai ne mai afuwa Kuma kana son Afuwa, ya Allah ka mana afuwa. Ba dan halayyarmu ba, Allah ka tausayamana albarkacin Ramadan.
Amin.

+2348168311092
Tambayoyi akan darasi.

25/03/2022

FASSARAR AL-QUR'ANI.
Darasi Na Tara 009

Suratul Baqara/سورة البقرة
Chapter: 2 Verse 73-83.

بسم الله الرحمن الرحيم
Da Sunan Allah Mai Rahama Mai Jinqai.

Ci gaba da Bayanin irin ni'imomin da Allah yayi akan Banu isra'ila.

ثُمَّ قَسَتْ قُلُوبُكُمْ مِنْ بَعْدِ ذَلِكَ فَهِيَ كَالْحِجَارَةِ أَوْ أَشَدُّ قَسْوَةً وَإِنَّ مِنَ الْحِجَارَةِ لَمَا يَتَفَجَّرُ مِنْهُ الْأَنْهَارُ وَإِنَّ مِنْهَا لَمَا يَشَّقَّقُ فَيَخْرُجُ مِنْهُ الْمَاءُ وَإِنَّ مِنْهَا لَمَا يَهْبِطُ مِنْ خَشْيَةِ اللَّهِ وَمَا اللَّهُ بِغَافِلٍ عَمَّا تَعْمَلُونَ
MA'ANA:
San'nan kuma zukatanku, s**a ƙeƙashe daga bayan wancan(ai,daga bayan wancan ni'imomin da Allah yayi muku da Kuma ayoyin Shi da ya nuna muku abayyane yadda yadda yake rayar da matacce) Saboda haka (sai su yahudawan nan) s**a zamanto k**ar duwatsu (wajen kekashewar zuciya) Ko mafi tsananin ƙeƙashewa (ai, koma fiye da duwastu ma'ana ai zuciyar wadannan yahudawa tama fi duwastu kekashewa a domin kuwa) kuma (ana samu) lalle ga duwatsu, haƙika, akwai abin da maremari suke ɓuɓɓuga daga gare shi, kuma lalle ne daga gare su,(Duwatsun) haƙiƙa, akwai abin da yake tsatstsagewa har ruwa ya fita daga gare shi, kuma lalle ne, haƙiƙa, daga gare su,(duwatsun) haƙiƙa, akwai Wanda yake faɗowa domin tsoron Allah kuma Allah bai zama gafili ba daga barin abin da kuke aikatawa (ma'ana ai Ubangiji Allah bai manta irin abubuwan da kuke aikatawa ba na saba mishi da kafircewa da ayoyin shi, ku banu isra'ila).

أَفَتَطْمَعُونَ أَنْ يُؤْمِنُوا لَكُمْ وَقَدْ كَانَ فَرِيقٌ مِنْهُمْ يَسْمَعُونَ كَلَامَ اللَّهِ ثُمَّ يُحَرِّفُونَهُ مِنْ بَعْدِ مَا عَقَلُوهُ وَهُمْ يَعْلَمُونَ
MA'ANA:
Shin (Yanzu ku muninai) kuna tsammanin (su yahudawa) za su yi imani saboda ku, (ne) alhali kuwa, haƙiƙa, wata ƙungiya daga gare su sun kasance suna jin maganar Allah, sa'an nan kuma su karkatar (ai, sai su canza) da ita (da son zuciyar su) daga bayan sun gane ta (haƙiƙa maganar Allah ce), alhali (kuwa) su, suna sane (ma'ana ai su da hankalinsu kuma sun san abinda sukeyi da abinda Sukayi cewa ba dede bama amma kuma dukda haka suna ci gaba da aikatawa ko ajikin su)?

وإذا لقلو الذين ءامنوا قلوا ءامنا وإذ خلا بعضهم الى بعض قلو أتحدثونهم بما فتح الله عليكم ليحا جوكم به عند ربكم افلا تعقلون
MA'ANA:
Kuma idan (su yahudawa) sun haɗu da waɗanda s**a yi imani s**an ce: "Mun yi imani," kuma idan sashensu ya wofinta zuwa ga sashe, s**an ce (ga 'yan uwansu yahudawa cewa) "Shin, kuna yi musu (musulmi) magana da abin da Allah Ya buɗa muku ne (acikin attaura) domin su yi muku hujja da shi a wurin Ubangijinku?" Shin fa, ba ku hankalta (ne 'yan uwa yahudawa)?

Sai Allahu SWT yace"
أَوَلَا يَعْلَمُونَ أَنَّ اللَّهَ يَعْلَمُ مَا يُسِرُّونَ وَمَا يُعْلِنُونَ
MA'ANA:
Shin, kuma (su yahudawannan) ba su sanin cewa lalle ne Allah Yana sanin abin da suke ɓoyewa (na siffofin annabi Muhammad SAW acikin attaura) da (kuma) abin da suke bayyanawa (na cewa sunyi Imani abaki aboye kuwa qarya sukeyi, shin ashe basu san cewa Allah ya san komai ba da sukeyi)?

Sai Allah yace"

وَمِنْهُمْ أُمِّيُّونَ لَا يَعْلَمُونَ الْكِتَابَ إِلَّا أَمَانِيَّ وَإِنْ هُمْ إِلَّا يَظُنُّونَ
MA'ANA:
Kuma daga cikinsu (su yahudawa) akwai ummiyyai, ba su da sanin Littafi,(ai, basu amfanuwa da abinda yake cikin littafin attaura) face tatsuniyoyi (na wofi da s**a biyewa), kuma su ba kome suke yi ba face suna yin zato (ma'ana ai basuda wata hujja da s**a riqa daga Allah a cikin dukkan abubuwan da suke aikatawa saide zato da rayawar jahilcin su kawai, Kuma s**e ai hakan daga Allah ne).

Shine sai Allah yace"
فَوَيْلٌ لِلَّذِينَ يَكْتُبُونَ الْكِتَابَ بِأَيْدِيهِمْ ثُمَّ يَقُولُونَ هَذَا مِنْ عِنْدِ اللَّهِ لِيَشْتَرُوا بِهِ ثَمَنًا قَلِيلًا فَوَيْلٌ لَهُمْ مِمَّا كَتَبَتْ أَيْدِيهِمْ وَوَيْلٌ لَهُمْ مِمَّا يَكْسِبُونَ
MA'ANA:
To, bone ya tabbata ga waɗanda suke rubuta littafi da hannuwansu (ai suke furta magana da bakunan su) sa'an nan kuma su ce wannan daga wurin Allah yake, domin su sayi kuɗi kaɗan da shi (ai, a domin su samu wasu yan kudade a duniya) san nan bone (narkon azaba) ya tabbata a gare su daga abin da hannayensu ke rubutawa, kuma bone (Narkon Azaba) ya tabbata a gare su daga abin da suke sana'antarwa (wato littafin Allah).

وَقَالُوا لَنْ تَمَسَّنَا النَّارُ إِلَّا أَيَّامًا مَعْدُودَةً قُلْ أَتَّخَذْتُمْ عِنْدَ اللَّهِ عَهْدًا فَلَنْ يُخْلِفَ اللَّهُ عَهْدَهُ أَمْ تَقُولُونَ عَلَى اللَّهِ مَا لَا تَعْلَمُونَ
MA'ANA:
Kuma s**a ce (su yahudawa wai) Wuta ba za ta shafe mu ba, face, 'yan kwanuka ƙidayayyu. (Wai kkwanakinda iyayen su s**a bautatawa dan maraqi, Shine Sai Allah yace ya Muhammad SAW) Ka ce: (musu shin) "Ashe kun riƙi wani alkawari a wurin Allah (ne na cewa baze kona ku ba face na wassu kwanaki?), sa'an nan (Kuma) Allah ba zai saɓa wa alkawarinSa ba ko kuwa kuna faɗin abin da ba ku sani ba bisa ga Allah?" (Ma'ana su yahudawa bakomai bane face suna fadin abinda basu sani bane dangane da Allah).

Sai Allah kude sani da kyau, wato yace"

بَلَى مَنْ كَسَبَ سَيِّئَةً وَأَحَاطَتْ بِهِ خَطِيئَتُهُ فَأُولَئِكَ أَصْحَابُ النَّارِ هُمْ فِيهَا خَالِدُونَ
MA'ANA:
Na'am!(ma'ana a'a ba haka bade abin nufi kawai Shine duk) Wanda ya yi tsiwur-wurin mugun abu, (ai ya aikata mugun abu) kuma laifinsa ya kewaye shi,(ai ya zamo lefukan shi sun rinjayi alherin Shi) to, waɗannan su ne 'yan Wuta, su a cikinta madawwama ne.

وَالَّذِينَ آمَنُوا وَعَمِلُوا الصَّالِحَاتِ أُولَئِكَ أَصْحَابُ الْجَنَّةِ هُمْ فِيهَا خَالِدُونَ
MA'ANA:
Kuma waɗanda s**a yi imani (da Allah da manzon Shi) kuma s**a aikata ayyukan ƙwarai, waɗannan, 'yan Aljanna ne, su a cikinta madawwama ne.

Sai Allah yace ya Muhammad SAW kace ga Banu isra'ila"

وَإِذْ أَخَذْنَا مِيثَاقَ بَنِي إِسْرَائِيلَ لَا تَعْبُدُونَ إِلَّا اللَّهَ وَبِالْوَالِدَيْنِ إِحْسَانًا وَذِي الْقُرْبَى وَالْيَتَامَى وَالْمَسَاكِينِ وَقُولُوا لِلنَّاسِ حُسْنًا وَأَقِيمُوا الصَّلَاةَ وَآتُوا الزَّكَاةَ ثُمَّ تَوَلَّيْتُمْ إِلَّا قَلِيلًا مِنْكُمْ وَأَنْتُمْ مُعْرِضُونَ
MA'ANA:
Kuma (ku tina) a lokacin da Muka karɓi alkawarin Bani-Isra'ila:(ai al-kawarin ubanninku cewa) "Kada ku bauta wa kowa face Allah, kuma ga mahaifa ku kyautata (musu) da makusantan ku (Dangi da 'yan uwa) da marayu da matalauta, (dukkan wadannan ku kyautata musu) kuma ku faɗi magana mai kyau zuwa ga mutane, kuma ku tsayar da salla, kuma ku bayar da zakka, sa'an nan (Sai gashi Nan) kuka juya baya (akan dukkan al-kawarin dake Tsakanin ku da Allah), face kaɗan daga gare ku,(sune s**a riqe wannan al-kawarin) alhali kuwa (mafi yawanku) kuna masu bijirawa (alkawarin).

وَإِذْ أَخَذْنَا مِيثَاقَكُمْ لَا تَسْفِكُونَ دِمَاءَكُمْ وَلَا تُخْرِجُونَ أَنْفُسَكُمْ مِنْ دِيَارِكُمْ ثُمَّ أَقْرَرْتُمْ وَأَنْتُمْ تَشْهَدُونَ
MA'ANA:
(Kuma ku tina) Lokacin da Muka riƙi alkawarinku; (cewa) ba za ku zubar da jininku ba, kuma ba za ku fitar da kanku daga gidajenku ba; sa'an nan kuka tabbatar (ai, sai gashi kuna zubar da jinin junanku kuma kuna koyar 'yan uwanku daga gidajen su) alhali kuwa kuna bayar da shaida (a kanku).

ثُمَّ أَنْتُمْ هَؤُلَاءِ تَقْتُلُونَ أَنْفُسَكُمْ وَتُخْرِجُونَ فَرِيقًا مِنْكُمْ مِنْ دِيَارِهِمْ تَظَاهَرُونَ عَلَيْهِمْ بِالْإِثْمِ وَالْعُدْوَانِ وَإِنْ يَأْتُوكُمْ أُسَارَى تُفَادُوهُمْ وَهُوَ مُحَرَّمٌ عَلَيْكُمْ إِخْرَاجُهُمْ أَفَتُؤْمِنُونَ بِبَعْضِ الْكِتَابِ وَتَكْفُرُونَ بِبَعْضٍ فَمَا جَزَاءُ مَنْ يَفْعَلُ ذَلِكَ مِنْكُمْ إِلَّا خِزْيٌ فِي الْحَيَاةِ الدُّنْيَا وَيَوْمَ الْقِيَامَةِ يُرَدُّونَ إِلَى أَشَدِّ الْعَذَابِ وَمَا اللَّهُ بِغَافِلٍ عَمَّا تَعْمَلُونَ
MA'ANA:
Sa'an nan kuma, (Sai) ga ku, ya (ku) waɗannan! (Yahudawa) Kuna kashe kanku, kuma kuna fitar da wani ɓangare daga gare ku daga gidajensu, kuna taimakon juna a kansu da zunubi da zalunci kuma idan k**ammu s**a je muku kuna fansarsu (wato sai gashi kuna aikata wani bangare na alakwari shine fanso 'Yan uwanku, amma kuna sabawa wani bangare na alkawarin) alhali kuwa shi fitar da su ('yan uwanku daga gidajen) abin da aka haramta muku ne (amma kuna aikatawa). Shin fa, kuna imani da sashen Littafin ne, kuma ku kafirta da sashe? To, mene ne sak**akon wanda ke aikata wancan daga gare ku face wulakanci a cikin rayuwar duniya? Kuma a Ranar alqiyama ana mayar da su zuwa ga mafi tsananin azaba. Kuma Allah bai zama Mai gafala ba daga barin abin da kuke aikatawa.

Sai Allah yace toh"

أُولَئِكَ الَّذِينَ اشْتَرَوُا الْحَيَاةَ الدُّنْيَا بِالْآخِرَةِ فَلَا يُخَفَّفُ عَنْهُمُ الْعَذَابُ وَلَا هُمْ يُنْصَرُونَ
MA'ANA:
Waɗannan su ne waɗanda s**a sayi rayuwar duniya da Lahira (ai s**a zami Qarya a maimakon Gaskiya a), domin haka (Allah yace) ba za a sauƙaƙa azaba ba daga kansu, kuma su, ba ataimakonsu (ai babu mai temakon su akan azabar da Allah ze musu har abada).

SHARHI ATAQAICE:

Su wadannan ayoyi wadanda suke bamu labarin irin abubuwa na ni'imoni da Kuma abubuwa na kafirci da Banu isra'ila s**a aikata, kuma har kawo izuwa zamanin Annabi Muhammad SAW ga irin abubuwa da suke yi na munafirci da kafircewa ayoyin Allah.

Kuma ayoyi ne da nuna mana cewa su yahudawa mutane masu sonzuciya marasa Amana dan gane da maganar Allah, karya da yaudara sukeyi ga mabiyan su a domin samun abinda Duniya.

Kuma su yahudawa sune Wanda Allah ya basu dama ya musu ni'ima da ilimi ,amma se gashi suna saba alkawarin Allah, na cewa za suyi ibada gareshi ma'ana zasu bi abinda yake cikin attaura, Kuma za subi Annabin Qarshen zamani, sai kuma gashi sun saba alkawarin saboda hassada da zalunci irin na wasu daga cikin su.

Kuma ayoyi ne da s**a fallasa yahudawa maqiya Allah maqiya Manzon Allah Annabi Muhammad SAW Na irin abubuwa da s**a boye a cikin littafin attaura na siffofin annabi muhammad SAW da halayyan shi, s**a hana a bayyana su ga mabiyan su da sauran mutane, sai s**a caccanza abubuwa da yawa acikin Littafin attaura a domin su boye Gaskiya Kuma su samu abin Duniya.

Wadannan ayoyi ne da suke yi mana wa'azi da gargadi cewa kada mu sake mu fadi karyan akan Allah ,ko mu aikata wani abunda bamuda ilimi akanshi, a saboda ga irin Sak**ako da kaskanci da wulakanci da mutum ka iyi samu a saboda aikata hakan.

Kuma ayoyi ne da suke fadakar damu mu Al-ummar Annabi Muhammad SAW akan dukkan Wanda yayi Imani da Allah kuma yayi Imani da Manzon Allah kuma yayi aiki mai kyau, toh shi Kam yana a cikin aljannah.

Sa'annan Kuma dukkan Wanda yaqi Allah ya kauda da Kai ga abunda Annabi yazo dashi, yabi hanyar shedan ya zabi Qarya akan Gaskiya, toh haqiqa shikan ya halaka kuma Yana a wuta.

WALLAHU A'ALAM.

Ya Allah Ka tsaremu daga Azabar wuta, kasa mu a cikin aljannar fiddausi.

+2348168311092
Tambayoyi akan darasi.

13/03/2022

SURAH AL-AHZAF/سورة الأحزاب
Girma Da Hatsari Irin Na Amana.

Chapter:33 verse 72-73.

بسم الله الرحمن الرحيم
Da Sunan Allah Mai Rahama Mai Jinqai.

Allahu SWT Yana cewa"
إِنَّا عَرَضْنَا الْأَمَانَةَ عَلَى السَّمَاوَاتِ وَالْأَرْضِ وَالْجِبَالِ فَأَبَيْنَ أَنْ يَحْمِلْنَهَا وَأَشْفَقْنَ مِنْهَا وَحَمَلَهَا الْإِنْسَانُ إِنَّهُ كَانَ ظَلُومًا جَهُولًا
MA'ANA:
(Allah yace) Lalle Mu, Mun gitta amana ga sammai da ƙasa da duwatsu, sai s**a ƙi ɗaukarta kuma s**aji tsoro daga gare ta, (Sai) kuma mutum ya ɗauke ta, lalle shi (mutum) ya kasance mai yawan zalunci, mai yawan jahilci.

Wato abin nufi anan shine, Ubangiji Allah ne yake bamu labari tin kafin ya halicce mu, awani kauli kuma akace, bayan ya halicci adamu se akatara sama da Qasa da aljanu, gefe guda ga Annabi adam(A.s).
Shikenan sai Allah SWT ya cewa sama ga Amana, Sai sama tace menene a cikin ta? Se Allah yace idan kin kautata asakan ka miki da lada, idan Kuma kika munana ta sai ayi miki Azaba, sai sama tace a'a bazata iya ba daukar taba.

Haka nan aka gifta amana ga Qasa itama da taji asalin ma'anar Amana Sai tace ba zata iyi ba.

Hakanan aka gifta amana ga Duwatsu Suma da s**aji me cece amana, sai s**ace bazasu iyi kiyaye ta ba.

Toh, shikenan sai Allahu SWT ya yiwa Adam tayin Amana ko ze iya dauka, sai adamu yace me nene acikin ta, se akace dashi idan ka kiyayeta to Allah ze gafarta maka ya sanya ka arahama, idan Kuma ka munana ta, ai ka kafirce toh, Allah zaiyi maka Azaba.
Sai Adam ya Karbi Amana, domin shi Dan Adam ya kasance mai yawan zalunci ne da Jahilci, wato ma'anar ai sai Allah ya kallafawa dan adam, wassu abubuwa na Umarni da kuma wassu abubuwa Na Hani, a domin ya jarrabesu ya ga shin wa nene zai kyautata ayyukan Shi.

Muninai masu imani da Allah da manzannin Allah bil-haqqi da Gaskiya, to wadannan s**an Ubangijin su zai temakesu a Cikin lamuran su a domin su sauke amanar su lafiya.
Su kuma kafirai mushirikai munafukai saboda yawan zalunci su da kuma yawan jahilcin su akan girma da Hatsari Na amana, zasu wayi gari suna masu cin Amana suna masu mantawa da al-kawarin Yin biyayya tsakinin su da Allah.
To wadannan sune asalin masu yawan zalunci ga kawunansu da kuma Jahilci .

Sai gaba Allah yake cewa"
لِيُعَذِّبَ اللَّهُ الْمُنَافِقِينَ وَالْمُنَافِقَاتِ وَالْمُشْرِكِينَ وَالْمُشْرِكَاتِ وَيَتُوبَ اللَّهُ عَلَى الْمُؤْمِنِينَ وَالْمُؤْمِنَاتِ وَكَانَ اللَّهُ غَفُورًا رَحِيمًا
MA'ANA:
Domin Allah Ya azabta munafukai maza da munafukai mata (sune wa 'yanda suke nuna imanin su azahiri idan kuma s**a faku ga mutanen kirki ko s**a faku ga mutane, se su ringa aikata kafircin su abayya ne, sunci amanar Allah sunci amanar bayin Allah) da mushirikai maza da mushirikai mata (su Kuma sune wa 'yanda suke shirka da Allah da sabawa manzannin Allah, Suma sunci amanar Allah sunci amanar bayin Allah) kuma Allah Ya karɓi tuba ga muminai maza da muminai mata (ma'ana ai Kuma sai Allah ya Karbi tuban bayinshi muninai wa'yanda s**ayi kuskure ko s**ayi lefi alhalib basu san lefi bane). Kuma (ku ku sani ubangijin ku) Allah (shi) Ya kasance Mai gafara (ne, Kuma) Mai jin ƙai.

Wato ma'anar Shine da za'a samu wani daga cikin bayi sai yayi kuskuri akan Amanar da aka dauramishi ko yayi ragi ga amanar da aka bashi alhalin bai sani ba, da gabaya Kuma se ya fahimci kuskure ne toh irin wadannan idan s**a tuba haqiqa ubangiji Allah zai amshi tuban su ya Kuma gafarta musu laifukan su.

SHARHI ATAQAICE.
wato wadannan ayoyi ne Wanda suke karantar damu irin girma da Kuma Hatsari dake cikin amana cewa lalle ita Amana ba abun Wasa bace musamman ma ace Amanar da take a tsakanin Allah da bawa.
Misali: Ita de amana
Addini ce, ko kuma ace da ita kiyaye dukkanin wassu dokokin Allah k**ar yadda Al-qur'ani ya bayya mana su sa'annan Kuma Kuma Annabi Muhammad SAW ya aikata mana su daki daki kafin ya bar Duniya.
Wato amanar itace aiwatar da umarni da Allah yace ayi, da kuma nisantar abubuwan Hani da Allah yace kar ayi.

Sa'annan Kuma Mu sani cewa: Sallah,azumi,zakka,hajji, wanka janaba dukkan su Amana ne akan dan Adam.
Haka Nan Kuma farji,hanci, Baki,ido,kunne, dukkan su amana ne matuqar bawa bai sarrafasu ta Yadda ya daceba to tamkar yaci amana ne.

Kuma Manzon Allah SAW yana cewa"
(Duk wani dadi na) Duniya baze taba kubucewa bawa ba idan har ya iyi kiyake Amana (wadda take tsakinin shi da Allah, da amana ta tsakinin shi da mutane) sa'annan kuma yayi Gaskiya ga duk wani labari da ze furta, sa'annan kuma yayi mu'amala da mutane mu'amala mai kyau,wato bai cuci kowa ba"

Kuma kiyaye salloli biyar na farilla a kullum tareda inganta alwalansu da kuma ya kiyake yin su akan lokaci yana temakon bawa zuwa ga sauke ko wacce irin amana ce lafiya,musamman ma ace bawa zai lizimci Addu'a da Kuma yawan yin azkar safe da yammaci dare da Rana.

Ita amana ta kasu Kashi dabam-dabam kuma ko wacce da ciki abin tambaya ce akan mutum aranar gobe al-Qiyama.

Zance tsakanin aboki da aboki Amana takan iya shiga ciki, haka zama na aure tsakanin miji da mata, 'ya'ya da 'yan uwa Amana takan iya shiga ciki. Haka Kuma tsakin mai saye da mai sayarwa dama sauran Al-ummar gari duka amana takan iya shiga ciki tsakani, ilimi Shima amana ne.
Sai de kawai fatammu anan shine Allah ya Bamu ikon fahimtar dukkan amanonin dake a tsakaninmu tareda ikon iya sauke su lafiya.
Amma tabbas Akwai aiki babba akan mu.
Mu sani cewa Ita Rikon Amana da Kuma maida ita ga muhallinta yakan janyowa mutum arziqi na Duniya da kuma na lahira.
A soboda haka mu kula Amana tamkar ibadace wanda duk bashi da amana to hakika bashi da addini, Kuma yana daukan nawi ne akan nawi.

Sai Aya ta Qarshen a cikin surar wadda ita kuma isharar narkon azaba ne takeyi ga munafukai da kuma mushrikai Kafirai maqiaya Allah su sani cewa lalle Ubangiji Allah zai azabtar dasu Sak**akon kafirce kishi.

Su Kuma muninai masu imani da Allah da manzannin Allah da littatafen Allah, toh s**am haqiqa Allah Yana musu albishir cewa lalle zai gafarta musu idan s**a nemi gafarar shi, kuma zai sanyasu a rahamar shi.
WALLAHU A'ALAM.

+2348168311092
Tambayoyi akan darasi.

01/03/2022

Fassarar Al-qur'ani
SURAH AN-NABA'I.
Chapter: 78 Verse 1-30.

بسم الله الرحمن الرحيم
Da Sunan Allah Mai Rahama Mai Jinqai.

عَمَّ يَتَسَاءَلُونَ
MA'ANA:
A kan me suke tambayar juna? (ai ma'ana ya Muhammad SAW , wai akan me nene suke tambaya, su mushirikai)

Sai Ubangiji Allah ta'ala yaci gaba da cewa"

عَنِ النَّبَإِ الْعَظِيمِ
MA'ANA:
(ai, wai) A kan muhimmin labari mai girma (wato Alƙur'ani shin Gaskiya ne labarin dake cikin shi, ko Kuma shin Gaskiya ne kuwa za'a tashi mutum bayan ya mutu a ranar al-Qiyama)?

Shine Allah yace"

الَّذِي هُمْ فِيهِ مُخْتَلِفُونَ
MA'ANA:
(Gaya musu ya Muhammad SAW, Ku sani Ita de wannan ranar ta al-Qiyama) Wanda (mutane) suke saɓa wa juna a cikinsa (ciki Da masu cewa lalle ranar zatazo, sune muminai, da Kuma masu Qaryata ta sune kafirai da mushrikai)

Sai Allah yace"

كَلَّا سَيَعْلَمُونَ
MA'ANA:
A'aha! (da sannude su wadannan masu Qaryata tan) Za su sani.

ثُمَّ كَلَّا سَيَعْلَمُونَ
MA'ANA
Kuma, a'aha! Za (de) su sani (ma'ana ai zasu ganta domin tabbas me zuwa ce)

Allah ta'ala yace"

أَلَمْ نَجْعَلِ الْأَرْضَ مِهَادًا
MA'ANA:
Ashe, ba Mu sanya ƙasa shimfiɗa ba (agareku, ya ku 'ya'yan adam?).

وَالْجِبَالَ أَوْتَادًا
MA'ANA:
Da (Kuma) duwatsu (a domin su zama) turaku (ga riƙe ƙasa, Saboda ita kasar ta zamo saukakka ce a gareku wajen gudanar da harkokin ku na rayuwa)?

وَخَلَقْنَاكُمْ أَزْوَاجًا
MA'ANA:
Kuma, Mun halitta ku maza da mata (ma'ana ai, munyi muku ni'ima a tsakan kanin ku na maza su aure mata a domin samun natsuwa gare su da kauna tsakani, haka mata su zama tufafi ga maza, suma maza su zama tufafi ga mata)?

وَجَعَلْنَا نَوْمَكُمْ سُبَاتًا
MA'ANA:
Kuma, (ashe ba mu) Muka sanya barcinku da kuke yi din nan da dare ya zamo) hutawa (ne ga gajiyar ku da Rana ba?).

وَجَعَلْنَا اللَّيْلَ لِبَاسًا
MA'ANA:
Kuma, Muka sanya dare (ya zama) sutura? (ai, ya zama rufin asiri ne da hutu a gare ku)

وَجَعَلْنَا النَّهَارَ مَعَاشًا
MA'ANA:
Kuma, Muka sanya yini (wato Rana, yazama) lokacin neman abinci?

وَبَنَيْنَا فَوْقَكُمْ سَبْعًا شِدَادًا
MA'ANA:
Kuma, Muka gina, a samanku, sammai bakwai masu ƙarfi? (Ma'ana ai, ita sama mu mukayi mata ado da taurari, Kuma ta zamo rumfa ne ita a gare ku)

وَجَعَلْنَا سِرَاجًا وَهَّاجًا
MA'ANA:
Kuma, (ashe ba mu) Muka sanya fitila mai tsanin haske (akan ku ba, wato ita ce rana)?

وَأَنْزَلْنَا مِنَ الْمُعْصِرَاتِ مَاءً ثَجَّاجًا
MA'ANA:
Kuma, (ba mu) Muka saukar daga cikakkun giragizai (nan ba) ruwa mai yawan zuba? (ai, ruwan sama lokaci zuwa lokaci a domin ku sha, a domin Kuma shayar gonakan ku)

لِنُخْرِجَ بِهِ حَبًّا وَنَبَاتًا
MA'ANA:
Domin, Mu fitar da ƙwaya (ata dalilin ruwan sama, kwayar abinci ga dabbobi mu Kuma fitar) da tsirrai game da shi wannan ruwan? (ai, mu fitar muku da wasu korayen stirrai a domin ku kuci Kuma kusha)

وَجَنَّاتٍ أَلْفَافًا
MA'ANA:
Da itacen lambuna masu lillibniya? (Wato su Masu ni'ima a gare ku)

Allah ta'ala yace ashe a yanzu ba nine nayi dukkan wadannan ni'imomin ba agare ku yaku 'ya'yan Adam? amma Kuma ace yau anwayi gari kune zaku manta da ayoyi na.

Sai Allah yace
Toh, ku sani"

إِنَّ يَوْمَ الْفَصْلِ كَانَ مِيقَاتًا
MA'ANA:
Lalle ne, ranar rarrabewa (wato ranar al-Qiyama tana nan tafe) ta kasance (domin kuwa ita Rana ce) abin ƙayyadewa (mai) lokaci (ubangiji Allah ne kadai yasan lokacin da zata afku, saboda haka ku kafirai kubar wani hanzari ga ita ko tambayar yau yaushe ne za'ayita, domin kuwa alkawarin Allah Gaskiya ne ya rigada ya Qayyade lokacinta)

يَوْمَ يُنْفَخُ فِي الصُّورِ فَتَأْتُونَ أَفْوَاجًا
MA'ANA:
(Alqiyama) Rana (ce) da za a yi busa a cikin ƙaho, sai ku zo, jama'a jama'a.(wato da anyi busa sai kaga mutane matattu suna ta tasowa daga cikin qasa mutanen tin zamanin farko har na Qarshe, a domin zuwa gaban Allah ayi hisabi)

Allah yace"

وَفُتِحَتِ السَّمَاءُ فَكَانَتْ أَبْوَابًا
MA'ANA:
(Sai) Kuma, aka buɗe sama (ai, za'a bude sama) sai ta kasance ƙofofi (a domin mala'ikun Allah su sassauko Qasa ayi Hisabi)

وَسُيِّرَتِ الْجِبَالُ فَكَانَتْ سَرَابًا
MA'ANA:
Kuma, aka tafiyar da duwatsu (ma'ana ai, za'a diddigar da duwatsu) sai (duwatsun) s**a kasance ƙura (abin shekarwa).

Allah yace"

إِنَّ جَهَنَّمَ كَانَتْ مِرْصَادًا
MA'ANA:
Lalle ne, Jahannama ta kasance madakata (ma'ana ai babu wani Mai shiga Aljanna se ya ketareta, idan ka kyautata aiki sai ka qetareta lafiya, idan kuma ka munana aiki, sai ka afka a cikin ta)

Allah ta'ala yace"

لِلطَّاغِينَ مَآبًا
MA'ANA:
(Ita wutar jahannama zata zamo azaba ce) Ga masu ƙetare iyakoki (na ubangiji Kuma) ta zama makoma (ce, a gare su).

لَابِثِينَ فِيهَا أَحْقَابًا
MA'ANA:
(Ya zamto su kafirai) Suna, masu zama a cikinta, zamunna (wato zama na dawwama)

لَا يَذُوقُونَ فِيهَا بَرْدًا وَلَا شَرَابًا
MA'ANA:
(Kuma) Ba su ɗanɗanawar wani (na) sanyi a cikinta (ma'ana ai, ita wannar wuta) kuma ba (za) su ɗanɗana abin sha (ba, ai wani abu mai kyau ba acikin ta)

إِلَّا حَمِيمًا وَغَسَّاقًا
MA'ANA:
Face tafasasshen ruwa da ruɓaɓɓen jini (wato abin sha mai wari ga kuma Muni wajen sha a cikin ta)

Allah yace"

جَزَاءً وِفَاقًا
MA'ANA:
(Wannan) Sak**ako (ne) mai dacewa (da irin munanan ayyukan su da s**a aikata a Duniya)

إِنَّهُمْ كَانُوا لَا يَرْجُونَ حِسَابًا
MA'ANA:
Lalle ne, su, sun kasance ba su fatar sauƙin wani hisabi (ma'ana su sun kasance a Duniya mutane Wanda ayyukan su na Qaryata Ranar Hisabi ranar gamuwa da Allah)

وَكَذَّبُوا بِآيَاتِنَا كِذَّابًا
MA'ANA:
Kuma, s**a ƙaryata game da ayoyinMu (bayyanannu) ƙaryatawa! (ai, Kuma s**a Qaryata Manzon Allah SAW, da abinda yazo musu dashi wato Al-qur'ani)

Sai Allah ta'ala yace"

وَكُلَّ شَيْءٍ أَحْصَيْنَاهُ كِتَابًا
MA'ANA:
Alhali (ku 'ya'yan adam baku San cewa ubangijin ku Allah ya sane da dukkan wani ayyukan ba na boye da na bayyane, ku sani) kowane abu Mun ƙididdige shi, a rubuce (ma'ana duk wani motsin bayi da duk wani tunanin bayi yana nan arubuce awajen Allah, Wanda ya aikata alkairi ya ga Sak**ako na alkairi, Wanda kuma ya aikata sharri ya ga Sak**ako na sharri)

Sai Allah yace"

فَذُوقُوا فَلَنْ نَزِيدَكُمْ إِلَّا عَذَابًا
MA'ANA:
(a) Saboda haka, ku (kafirai da munafikai ku) ɗanɗana (Azaba) domin haka (ne ya dace da irin ayyukan munana da kukayi aduniya, Kuma ku sani) ba za Mu ƙara muku kome ba (acikin wannar wuta) face azaba (akan azaba har abada).

SHARHI ATAQAICE.
da farkode su wadannan ayoyin suna Banu labari ne yadda ubangiji SWT zeyi da kafirai Arna maqiya Allah, Sak**akon Irin ayyukan su na sabo da Qaryata ayoyin shi da manzannin shi da Sukayi a nan gidan Duniya.

Sa'annan Kuma ayoyi ne Wanda suke nuna isa,Izza, girma, da buwayar Ubangiji Allah mahaliccin kowa da komai.

shi-shikadai ya San halittar shi ciki da bai kuma yayi mata ni'imomi daban daban, a saboda haka kuwa shine yafi can-canta da abutata mishi, a kuma nuna godiya agare shi, Wanda yin hakan biyayya ne agare shi, Kuma alkairi ne ga bawa.

Sa'annan Kuma su Wadannan ayoyi ne da suke nuna irin matsayi da isan daraja ga fiyayyen halitta Annabi Muhammad SAW, a domin kuwa littafin da Allah ya bashi shine Littafi mafi girman daraja a littatafen Allah, Kuma Annabi Muhammad shine shugaban manzannin da Allah ya aiko Duniya, saboda da haka duk wanda ya rayu dashi ko Kuma yazo abayan shi to dole ne Sai ya bishi sa'annan ya zamo Mai Imani Kuma ya samu tsira a wajen Allah.
WALLAHU A'ALAM.

Dafatan Allah ya tseratar damu, ya Kuma karemu daga sharrin shedan, ya tabbatar damu akan imani ya kashemu muna musulmai.

+2348168311092
Tambayoyi akan darasi.

Want your school to be the top-listed School/college in Gombe?

Click here to claim your Sponsored Listing.

Location

Category

Telephone

Website

Address


Layin Mele Jekadafari
Gombe