22/08/2026
TAYA MARYAM IBRAHIM DAN’AZUMI MURNA — Gwarzon Alƙur’ani na Najeriya
Ina miƙa saƙon taya murna na musamman ga Maryam Ibrahim Dan’Azumi bisa gagarumar nasarar da ta samu a Gasar Alƙur’ani ta Ƙasa da Ƙasa ta Sarki Abdulaziz karo na 46, wadda aka gudanar a Masarautar Saudiyya.
Samun nasara a irin wannan gasa, wadda ta ƙunshi mahalarta daga ƙasashe 132 na duniya, babbar nasara ce kuma abin alfahari. Ƙwarewar da Maryam ta nuna wajen haddar Alƙur’ani, karatunsa, Tajwidi da Tafsiri, sakamakon shekaru ne na jajircewa, sadaukarwa, himma da kuma dagewa wajen neman ƙwarewa.
Nasarar Maryam ta sake tunatar da mu irin gagarumin basira da damar da matasan Najeriya suke da ita wajen fafatawa da takwarorinsu na duniya da kuma samun nasara. Abin da ya ƙara ba da kwarin gwiwa shi ne irin abin koyi da iyalinta s**a samar. Babbar ’yar uwarta, Hajara Ibrahim Dan’Azumi, ita ma ta taɓa zama ta farko a wata gasar Alƙur’ani ta ƙasa da ƙasa da aka gudanar a Jordan a shekarar 2024. Nasarorin ’yan’uwan nan biyu sun nuna irin abin da za a iya cimmawa idan aka kula da baiwa, aka gina tarbiyya mai kyau, aka samu ilimi, jagoranci da tallafin iyali.
Ina taya iyayensu, malamansu da masu kula da tarbiyyarsu murna, tare da yaba musu bisa irin sadaukarwa, jagoranci da shawarwarin da s**a bayar, waɗanda s**a taimaka matuƙa wajen wannan gagarumar nasara.
A madadin Ma’aikatar Matasa ta Tarayya, ina taya Maryam murna da wannan nasara da ta kawo wa ƙasarmu Najeriya ɗaukaka da girma. Ina roƙon Allah Ya sanya wannan nasara ta zama abin ƙarfafa wa miliyoyin matasan Najeriya wajen neman ilimi, jajircewa da kuma ƙoƙarin samun nagarta da ƙwarewa.
Allah Ya ƙara wa Maryam ilimi da fahimta, Ya sanya Alƙur’ani Mai Girma ya zama tushen shiriya, rahama da albarka a rayuwarta.
Taya murna, Maryam! Najeriya na alfahari da ke.
Ayodele Olawande
Mai Girma Ministan Matasa