Celebrating my 4th year on Facebook. Thank you for your continuing support. I could never have made it without you. 🙏🤗🎉
Mallam umar badeggi ta'alimat.
The page is about Huduba juma'a and tafsir of Ramadan
SHARHU SUNNAH
Sharhu Sunnah( 1)
Assalamu Alaikum Warahmatullahi Wabarakatuh,
All praise is due to Allah who has spared our lives to witness another blessed month.
May Allah make it a month of forgiveness, mercy, and spiritual upliftment for us all.
Allah says:
يَا أَيُّهَا الَّذِينَ آمَنُوا كُتِبَ عَلَيْكُمُ الصِّيَامُ كَمَا كُتِبَ عَلَى الَّذِينَ مِن قَبْلِكُمْ لَعَلَّكُمْ تَتَّقُونَ
“O you who believe, fasting has been prescribed upon you as it was prescribed upon those before you that you may attain Taqwa.”
— Surah Al-Baqarah (2:183)
Let us maximize this month through:
Sincere fasting
Increased Qur’an recitation
Night prayers (Taraweeh)
Charity and good character
Avoiding sins and distractions
May Allah accept our fasting and عبادات.
Ramadan Mubarak 🌙
Signed:
Abdulsamad Umar badeggi
*Duk wanda ya bar sallah – ya rasa komai.🕌* 001.
*Ya ku bayin Allah!* Sallah ba kawai farilla bace – *ita ce mafitar duk wata matsala.* Duk wanda ya gina rayuwarsa akan sallah, to ya gina rayuwa akan tubali mai ƙarfi.
*Allah (SWT) ya ce:*
﴿وَأَقِمِ ٱلصَّلَوٰةَ ۖ إِنَّ ٱلصَّلَوٰةَ تَنْهَىٰ عَنِ ٱلْفَحْشَآءِ وَٱلْمُنكَرِ﴾
*_Ka tsayar da sallah. Lallai sallah tana hana alfasha da mummunan aiki._* – [Al-Ankabut: 45]
*🔥 illolin barin sallah....*
- Barin sallah babban zunubi ne.
- abinda yake raba tsakanin musulmi da kafiri shine sallah.
- Sallah ita ce tambaya ta farko a ranar kiyama.
*Annabi (SAW) ya ce:*
> *Farkon abu da za a fara tambayar bawa a ranar kiyama – shine sallarsa. Idan ta gyaru, sauran ayyukansa zasu gyaru.”* – [Tirmidhi]
*💔 Idan baka sallah...*
- Kana yanke alaƙarka da Allah.
- Kana barin ƙofa buɗe ga sharrin shaiɗan.
- Kana wulaƙanta kanka a lahira.
> *Ka rike sallah, ko da duniya tana rugujewa.”*
> *Kada ka bari wani abu ya fi muhimmanci fiye da sallar ka.”*
> *Ka koma ga Allah kafin ka dawo gare shi babu damar gyara.”*
*Ya Allah!* Ka sa mu cikin masu tsayar da sallah, ka karɓi sallolinmu, ka tsare mu daga gafala da sakaci.
*الله تعالى أعلم*
*_AYYUKAN ‘YAN ALJANNA_* 001.
_*TSARKAKE TAUHIDI DA IKHLASI GA ALLAH*_
_‘Yan Aljanna su ne wadanda s**a tsarkake bautarsu ga Allah Shi kaɗai, s**a kebance niyyarsu gare Shi, ba su haɗa Allah da kowa ba, kuma ba sa yin aiki sai domin yardar Allah._
_Ya ku bayin Allah! Ku ji tsoron Allah matuƙar jin tsoronsa. Ku sani cewa babban aikin da ya fi dukkan ayyuka daraja, wanda babu ‘yan Aljanna sai da shi, shi ne *Tauhidi tare da Ikhlasi.*_
Allah madaukakin Sarki yana cewa
> وَمَا أُمِرُوا إِلَّا لِيَعْبُدُوا اللَّهَ مُخْلِصِينَ لَهُ الدِّينَ
[البينة: 5]
*_(Ba a umarce su da komai ba face su bauta wa Allah suna tsarkake masa addini)._*
_‘Yan Aljanna sun fahimci cewa duk wani aiki *—sallah, azumi, sadaka, jihadi, karatun Alƙur’ani* idan babu ikhlasi, aikin ya rushe._
Allah Ta’ala yana cewa:
> قُلْ إِنِّي أُمِرْتُ أَنْ أَعْبُدَ اللَّهَ مُخْلِصًا لَّهُ الدِّينَ
[الزمر:
_*(Ka ce: Lallai an umurce ni ne da in bauta wa Allah ina tsarkake masa addini).*_
_Yaku bayin Allah! Annabi ﷺ ya bayyana mana tushen karɓuwar aiki inda ya ce_
> “Lallai ayyuka suna tare da niyya, kuma kowane mutum yana da abin da ya yi niyya.”
(Bukhari da Muslim s**a ruwaito shi).
_‘Yan Aljanna basa neman yabo, basa neman suna, basa yin aiki don a ce musu *waliyyai ko malamai ko masu ibada.* Allah suke nema, Allah suke so, Allah suke tsoro._
_Allah Madaukakin Sarki yana cewa a cikin Hadisi Qudsi_
> Ni ne mafi wadatar abokan tarayya. Duk wanda ya yi aiki ya haɗa Ni da wani a cikinsa, Na bar shi da wanda ya haɗa Ni da shi.”
(Muslim ya ruwaito shi).
_Yaku bayin Allah! Ku sani cewa shirka da riya su ne mafi hatsarin abin da ke rushe aiki. Saboda haka ‘yan Aljanna suna tsananin tsoron aikata aiki ba don Allah ba._
Daga Mahmud bn Labid (RA), Annabi ﷺ ya ce:
> “Abin da nake fi tsoro a kanku shi ne shirka ƙanana.” Sahabbai s**a ce: “Menene shirka ƙanana ?” Sai ya ce: “Riya.”
(Ahmad ya ruwaito shi).
_‘Yan Aljanna suna yawaita duba zuciyarsu kafin aiki, a yayin aiki, da bayan aiki. Suna roƙon Allah Ya tsarkake niyyarsu, domin sun san Allah ba ya karɓar aiki sai wanda aka yi don Shi kaɗai._
Allah Madaukakin Sarki yana cewa:
> فَمَن كَانَ يَرْجُو لِقَاءَ رَبِّهِ فَلْيَعْمَلْ عَمَلًا صَالِحًا وَلَا يُشْرِكْ بِعِبَادَةِ رَبِّهِ أَحَدًا
[الكهف: 110]
*_(Duk wanda yake fatan haɗuwa da Ubangijinsa, to ya aikata aiki nagari, kuma kada ya haɗa kowa da bautar Ubangijinsa)._*
_Ya kai bawan Allah! Ka tambayi kanka...._
_Shin sallah da nake yi don Allah nake yi ?_
_Shin sadakar da nake bayarwa don Allah nake yi ?_
_Shin abin da nake aikawa mutane don gani ne, ko don Allah ne ?_
*Da Tauhidi da Ikhlasi kaɗai ake shiga Aljanna.*
*الله تعالى أعلم*
You can join our WhatsApp chat for more lectures and don't forget to follow and like too
https://chat.whatsapp.com/GPhYoq8X6GzIvWH6NBcnLw
*اللهم صل وسلم على سيدنا وحبيبنا ونبينا محمدا صلى الله عليه وآله وسلم....*❤️
Last week Friday
Abu-khadijah
Abu-khadijah
Mal.Umar Badeggi Hafizahullah
*سلسلة الأحاديث النبوية الشريفة*
*بسم الله، والصلاة والسلام على رسول الله وعلى آله وصحبه ومن تبعهم بإحسان إلى يوم الدين، وبعد.*
*We present to brothers and sisters in Islam today 🔷 today Eid Khutubah
Maudui: Khutubah akan laiya
🎤🎤🎤🎤🎤🎤🎤🎤🎤
✳️ In Hausa language
Daga Fillin Eid ah garin Agaie ,Agaie local government Niger state*
By⤵️*
*Abu-khadijah, Mallam Umar
Muhammad badegg*
*زاده الله الاستقامة*
WhatsApp group link⤵️⤵️🌏🌎🔗🔗🔗
https://chat.whatsapp.com/GPhYoq8X6GzIvWH6NBcnLw
Facebook group link⤵️⤵️🌏🌎🔗🔗🔗
https://www.facebook.com/100079626432411/videos/
1488675968494940/?mibextid=rS40aB7S9Ucbxw6v
https://t.me/+Fi0cTttHi3lkMTg0
Click here to claim your Sponsored Listing.
Location
Category
Contact the school
Telephone
Address
Old Bank
Agaie
911104