29/04/2026
CHAKWAKIYA A JAMIYAR APC JAMA'ARE ITAS GADAU
Hajiya Bilkisu Haruna
“Ban ɗauki wannan mataki cikin gaggawa ba. Na zauna da wakilaina daga kowane lungu da saƙo na Jama’are domin jin ra’ayinsu da koken al’umma.
Wannan ba lamari na kaina ba ne—ina siyasa ne saboda al’umma. Idan ina son ci gaba da mutunci da amincewar da aka ba ni a matsayin Chairlady, dole ne in saurari muradunsu kuma in tsaya a inda za a ba su daraja.
Saboda haka, ina kira ga daukacin al’umma da su bude ido, su yi zaɓi cikin basira, su kuma goyi bayan waɗanda suke da tabbataccen tarihin aiki da gaskiya irin su SULEIMAN SAAD SULGAD . Su ne kaɗai za su iya kawo cigaba mai dorewa da walwalar Mata”
29/04/2026
🌙 TUNAWA DA MALAMI…
A yau mun tsaya muna tuna da wani gwarzon malami,
Malam Yakubu Ustaz Jama'are
Ko da yake lokaci ya ja tun bayan rasuwarsa, amma tasirinsa bai gushe ba. Har yanzu ilimin da ya koyar da tarbiyyar da ya shimfiɗa suna rayuwa a cikin al’umma.
Malami ne da ya sadaukar da rayuwarsa wajen: 🕌 Koyar da addini
📖 Tarbiyyar matasa
🤲 Shiryar da al’umma
Irin waɗannan mutane ba su gushewa a zukatan mutane…
📿 Yau muna roƙon al’ummar Jama’are da kewaye:
Mu tuna da shi da addu’a, domin shi ne abin da ya fi amfanar da mamaci.
🤲 Allah Ya gafarta masa,
Ya yalwata kabarinsa da rahama,
Ya sa Aljannah Firdausi ta zama makomarsa.
💬 Ka rubuta addu’a a comment domin ƙara masa lada
❤️ Ka yi share domin wasu su tuna su masa addu’a
28/04/2026
Muna Taya Kumgiyar kwallon kafa ta Marai Academy Jama’are da samun wannan Kyauta
Congratulation 🎊 Auwal Boka
28/04/2026
Jama’ar Jama’are… lokaci ya yi!
Lokaci ya yi da za mu zaɓi wakili nagari, wanda yake da kishinmu kuma yake tare da matasa a kowane lokaci.
Hon. Alhaji Aminu Isah — jagora mai gaskiya, mai hangen nesa, kuma mai son ci gaban al’umma.
Yana tafe da shirye-shiryen ƙarfafa matasa, inganta ilimi, da kawo sauyi na gaskiya a Jama’are.
Kada mu bari a sake wuce mu!
Mu haɗu mu bada goyon baya…
Mu zaɓi nagari…
👉 Hon. Aminu Isah — domin Member, House of Assembly!
🗳️ Fatan Alkhairi 2027!
27/04/2026
Jama’are… Jama’are… Jama’are!
Har yaushe za mu ci gaba da zama a baya?
Har yaushe matasanmu za su ci gaba da jiran dama?
Har yaushe za mu riƙa jin alkawari ba tare da aiki ba?
Lokaci ya yi!
Lokacin canji na gaskiya ya zo!
Ga mutum da ya zo da sabuwar manufa…
Mutum mai kishin jama’a…
Mutum mai aiki, ba mai magana kawai ba…
👉 Hon. Alh. Aminu Isah Jama’are!
Zai kawo:
✔️ Ingantaccen ilimi
✔️ Damar aikin yi ga matasa
✔️ Tallafin sana’o’i
✔️ Wakilci nagari mai anfani ga kowa
Wannan ba siyasa ta baka ba ce… siyasa ce ta aiki!
👉 2027 — Lokacin Jama’are ne!
👉 2027 — Lokacin Matasa
ne!
Ka tashi! Ka fito! Ka zaɓa da hikima!
🗳️ Zaɓi Hon. Alh. Aminu Isah Jama’are
Domin wakilci nagari… domin ci gaban Jama’are… domin makoma mai haske
27/04/2026
DA DUMI-DUMI: Gwamnan Jihar Taraba, Dakta Agbu Kefas, ya kaddamar da aikin t**i mai tsawon kilomita 5, da ya lakume Naira biliyan uku (N3bn) kamar yadda kuke gani.
Me za ku ce?
27/04/2026
📺 SANARWA DAGA CLASSIC TV
Assalamu alaikum wa rahmatullahi wa barakatuhu.
Muna miƙa gaisuwa tare da fatan alheri ga daukacin mabiya wannan shafi.
Muna sanar da ku cewa, duk wani rubutu ko bayani da ya shafi wani mutum ko ƙungiya da ake wallafawa a wannan shafi, ana yin sa ne da cikakken izininsu da amincewarsu. Ba mu wallafa wani abu sai wanda aka turo mana domin a yaɗa shi.
Haka kuma, duk wani abu da aka kawo domin a wallafa, yana tafiya ne bisa tsarin aikinmu na kasuwanci, domin tabbatar da cewa an yi komai cikin tsari da yardar mai shi.
A gefe guda kuma, muna ƙara jaddada cewa ba ma amincewa da wallafa zagi, cin mutunci, ko ƙage ga kowane mutum ko ɓangare. Muna ƙoƙarinmu gwargwadon iko wajen kare martabar kowa da kowa.
Sai dai hakan ba zai hana mu isar da sahihin bayani da gaskiya ga al’umma ba, cikin ladabi da mutunta juna.
An buɗe wannan kafar ne domin kusantar da ku da sahihan bayanai, abubuwan da ke faruwa, da kuma waɗanda watakila ba ku samu damar sani ba.
Muna kuma roƙon fahimta cewa mu ma ‘yan Adam ne, muna iya yin kuskure, kuma a kowane lokaci muna maraba da gyara cikin ladabi.
Mun gode da goyon bayanku da amincewarku.
– Classic TV 📺
26/04/2026
Da Dumi-Dumi: Cikin kasa da kwana biyu (awa 48) matasa maza da mata da Professor Isa Ali Pantami ya samawa aiki wasu ya koya musu sana'o'in zamani da kuma wa yanda ya karantar da sauran masoyansa sun hada gudumawar sama da Naira million 50 domin saya masa Form din tsayawa takarar Gwamna a Jihar Gombe a 2027 in Allah Ya yarda.
Wannan gudumawa sun yi ne domin godiya ba tare da nema daga gare shi.
Cikakken bayani kan kudin zai zo daga baya In Allah ya yarda.
26/04/2026
Hassan Jama'are ga mutanen ku
Koda Da jìnì Ake Zabe Zamu Ýånkā Jikin Mu Mu Zabi TINIBU Cewar Matashin Dan Gwagwarmaya Aminu Bello .
Me zaku ce ?
26/04/2026
Mai Girma.
WAMBAN JAMA'ARE,(Hakimin kasar jama'are)
Alh. Abubakar Muhammad wabi🙏
Photo Saleem Mahmood (smash)
26/04/2026
Anata Ruwan Appointments a Jahar Bauchi,
Alummar Jamaare Shuru
Meke Faruwa ne
Kufada mana a comment Section