16/12/2020
KANKARA KATSINA
In dai jira za’a cigaba da yi har sai sun kawo hari sannan aje a rama, to hakan zai cigaba da fito da gazawar gwamnati kenan.
Ina tabbas za’a iya kawar dasu.
Yan bindiga a jiya daddare jiya sun shiga Wata makaranta a kankara ta jihar Katsina da muggan makamai. Bayan hallaka mai lura da makarantar sun sace dalibi masu yawa sun yi gaba dasu.
Ku saurari wani Video da WD Hausa s**a saki, Kaji muryoyin iyayen yaran da aka dauka, kaji abin tada hankali.
Jami’an tsaronmu a da, har wasu kasashen makotanmu suke kai agajin zaman lafiya. Saboda karfinsu da kwarewar aiki. Abin mamaki ga wuta ta tashi tana neman cinye mutane da dukiyoyi da zaman lafiya. Kisan wutar na neman zama siyasa.
SIYASA DA RAYUKAN mutane ba zai haifar mana Abin alkairi ba fa.
Wai ya alamarin yake ne?
BARI IN MAIMATA
Masu satar mutane dai yanzu basa tsoron kowa. Duk inda s**a ga dama shiga suke su dauka su fita. Wannan kamar sako ne aka aikawa
Mr President domin sai da s**a ji ya shiga garin s**ai wannan aikin.
Allah muna kara tuba, muna neman afuwarKA, AgajinKa, ka kawo mana karshen wannan MASIFA. Amin.
15/12/2020
21/05/2020
05/11/2019