Dr. Abdurrahman Sani Yakubu Zaria.

Dr. Abdurrahman Sani Yakubu Zaria.

Share

(𝐀 𝐍𝐒𝐠𝐞𝐫𝐒𝐚𝐧 𝐚𝐜𝐚𝐝𝐞𝐦𝐒𝐜 𝐫𝐞𝐬𝐞𝐚𝐫𝐜𝐑𝐞𝐫 𝐖𝐑𝐨 𝐑𝐨π₯𝐝𝐬 𝐚 𝐝𝐨𝐜𝐭𝐨𝐫𝐚𝐭𝐞 𝐝𝐞𝐠𝐫𝐞𝐞 𝐒𝐧 𝐭𝐑𝐞 𝐟𝐒𝐞π₯𝐝 𝐨𝐟 𝐜𝐫𝐞𝐞𝐝 (𝐀πͺ𝐒𝐝𝐚𝐑) 𝐚𝐭 𝐭𝐑𝐞 𝐈𝐬π₯𝐚𝐦𝐒𝐜 π”π§π’π―πžπ«π¬π’π­π² 𝐨𝐟 𝐌𝐚𝐝𝐒𝐧𝐚𝐑).

27/05/2026

SAKON BARKA DA SALLAH

Assalamu Alaikum wa Rahmatullahi wa Barakatuh.

Ina miΖ™a saΖ™on barka da Sallah ga Ι—aukacin al’ummar Musulmi, musamman malamai, Ι—alibai, iyaye da dukkan masu neman ilimi da kyawawan Ι—abi’u.

Ina roΖ™on Allah MaΙ—aukakin Sarki Ya karΙ“i ibadunmu, Ya gafarta mana kura-kuranmu, Ya sanya wannan Sallah ta zama sanadin zaman lafiya, haΙ—in kai, da yalwar arziki a tsakaninmu.

Mu ci gaba da riΖ™o da koyarwar addinin Musulunci, da nuna Ζ™auna, tausayi, haΖ™uri da taimakon juna, domin waΙ—annan su ne ginshiΖ™an al’umma ta gari.

Allah Ya maimaita mana wata Sallah Babba cikin Ζ™oshin lafiya, imani da kwanciyar hankali.

Barka da Sallah.
Taqabbalallahu minna wa minkum

✍️Dr. Abdurrahman Sani Yakubu

26/05/2026

πŸŒ™βœ¨ RANAR ARFA ✨
1. Ranar Arfa rana ce ta gafara da β€˜yanta bayin Allah daga wuta. Kada ka bari zuciyarka ta shagaltu da duniya, alhali Ζ™ofofin rahama a buΙ—e suke.

2. A ranar Arfa, addu’ar bawa mai gaskiya ba ta dawowa banza. Ka Ι—aga hannuwanka da zuciya mai tawakkali ga Allah.

3. WataΖ™ila hawaye Ι—aya na nadama a ranar Arfa ya fi shekaru na sakaci amfani.

4. Ranar Arfa dama ce ta gyara zuciya kafin rayuwa ta Ζ™are. Ka nemi gafarar Ubangijinka tun kafin lokaci ya kure.

5. Mafificin abin da zaka yi a ranar Arfa shi ne yawaita ambaton Allah da salati da istigfari.

6. Ka tuna: ba kowa ne zai sake ganin ranar Arfa ta gaba ba. Ka yi anfani da wannan rana wajen neman rahama da gafara.

7. Idan kana son nutsuwar zuciya, ka kusanci Allah a ranar Arfa da addu’a da tawali’u.

8. Ranar Arfa rana ce da ake goge zunubai, kuma ake Ι—aukaka matsayi. Kada ka kasance cikin masu gafala.
9. Ka bar korafi, ka rungumi addu’a. Domin a ranar Arfa, Allah yana karΙ“ar roΖ™on bayinsa masu tawakkali.

10. Ka azumci ranar Arfa idan ba mahajjaci ba ne, domin tana kankare zunuban shekara biyu da yardar Allah.

11. Duk wanda ya cika ranar Arfa da zikiri da addu’a, zuciyarsa zata cika da hasken imani.

12. Ranar Arfa tana tunasar da mu cewa rahamar Allah ta fi girman zunubanmu.

13. Ka yi sulhu da Allah a ranar Arfa, domin babu rabon da ya fi samun yardarsa.

14. Addu’ar iyaye, hawaye na tuba, da zikiri a ranar Arfa β€” duk suna daga cikin taskokin da ba sa Ι“acewa.

15. Ranar Arfa ba ranar wasa ba ce; rana ce ta neman gafara, rahama, da canjin rayuwa zuwa alkhairi.

🀲 Allah Ya sanya mu cikin bayinsa na gari, Ya karΙ“i ibadunmu da addu’o’inmu. Ψ’Ω…ΩŠΩ†

✍️ Dr. Abdurrahman Sani Yakubu

25/05/2026

1.β€œKada ka bari kwanakin Zul-Hijja su wuce babu canji a rayuwarka. WataΖ™ila wannan ce damar da Allah ya buΙ—e maka domin kusantar Sa.”

2. β€œAyyukan alkhairi a kwanakin Zul-Hijja sun fi daraja a wajen Allah fiye da sauran kwanaki.”

3.β€œKa cika bakinka da tasbihi, tahmidi da tahlili; domin kwanakin Zul-Hijja kwanaki ne na rahama.”

4. β€œWanda ya yi anfani da Zul-Hijja yadda ya kamata, zai girbi nutsuwa a duniya da lada a Lahira.”

5. β€œKar ka raina Ζ™aramin alkhairi a Zul-Hijja; wata kalmar zikiri na iya zama sanadin gafarar zunubanka.”

6. A kwanakin Zul-Hijja, ka gyara tsakaninka da Allah kafin ka nemi duniya ta gyaru gare ka.”

7. β€œYawaita istigfari, domin zukata suna rayuwa ne da neman gafarar Allah.”

8. β€œWanda ya rasa anfani da kwanaki goma na Zul-Hijja, ya rasa wata babbar kasuwa ta lada.”

9. Zul-Hijja wata dama ce ta sabuwar rayuwa ga mai neman gafarar Ubangiji.”

✍️Dr. Abdurrahman Sani Yakubu

24/05/2026
23/05/2026

Wa'azi Daga Garin Makkah

Dr. Abdurrahman M. Sani Yakubu

23/05/2026

Wa'azi Daga Garin Makkah

Dr. Abdurrahman M. Sani Yakubu

23/05/2026

Nasiha akan hanyar zuwa Makkah

Dr. Abdurrahman M. Sani Yakubu

23/05/2026

Labarin wani mahajjaci

Dr. Abdurrahman M. Sani Yakubu

19/05/2026

Lokacin da Sheikh Dr Abdurrahman M. Sani Yakubu yake gabatar da karatu daga cikin littafin adda’u waddawa’ a garin Azare.

Want your school to be the top-listed School/college in Abuja?

Click here to claim your Sponsored Listing.

Location

Category

Telephone

Website

Address


Plot, 120 Nile Street Maitama FCT Abuja
Abuja