27/05/2026
SAKON BARKA DA SALLAH
Assalamu Alaikum wa Rahmatullahi wa Barakatuh.
Ina miΖa saΖon barka da Sallah ga Ιaukacin alβummar Musulmi, musamman malamai, Ιalibai, iyaye da dukkan masu neman ilimi da kyawawan Ιabiβu.
Ina roΖon Allah MaΙaukakin Sarki Ya karΙi ibadunmu, Ya gafarta mana kura-kuranmu, Ya sanya wannan Sallah ta zama sanadin zaman lafiya, haΙin kai, da yalwar arziki a tsakaninmu.
Mu ci gaba da riΖo da koyarwar addinin Musulunci, da nuna Ζauna, tausayi, haΖuri da taimakon juna, domin waΙannan su ne ginshiΖan alβumma ta gari.
Allah Ya maimaita mana wata Sallah Babba cikin Ζoshin lafiya, imani da kwanciyar hankali.
Barka da Sallah.
Taqabbalallahu minna wa minkum
βοΈDr. Abdurrahman Sani Yakubu
26/05/2026
πβ¨ RANAR ARFA β¨
1. Ranar Arfa rana ce ta gafara da βyanta bayin Allah daga wuta. Kada ka bari zuciyarka ta shagaltu da duniya, alhali Ζofofin rahama a buΙe suke.
2. A ranar Arfa, adduβar bawa mai gaskiya ba ta dawowa banza. Ka Ιaga hannuwanka da zuciya mai tawakkali ga Allah.
3. WataΖila hawaye Ιaya na nadama a ranar Arfa ya fi shekaru na sakaci amfani.
4. Ranar Arfa dama ce ta gyara zuciya kafin rayuwa ta Ζare. Ka nemi gafarar Ubangijinka tun kafin lokaci ya kure.
5. Mafificin abin da zaka yi a ranar Arfa shi ne yawaita ambaton Allah da salati da istigfari.
6. Ka tuna: ba kowa ne zai sake ganin ranar Arfa ta gaba ba. Ka yi anfani da wannan rana wajen neman rahama da gafara.
7. Idan kana son nutsuwar zuciya, ka kusanci Allah a ranar Arfa da adduβa da tawaliβu.
8. Ranar Arfa rana ce da ake goge zunubai, kuma ake Ιaukaka matsayi. Kada ka kasance cikin masu gafala.
9. Ka bar korafi, ka rungumi adduβa. Domin a ranar Arfa, Allah yana karΙar roΖon bayinsa masu tawakkali.
10. Ka azumci ranar Arfa idan ba mahajjaci ba ne, domin tana kankare zunuban shekara biyu da yardar Allah.
11. Duk wanda ya cika ranar Arfa da zikiri da adduβa, zuciyarsa zata cika da hasken imani.
12. Ranar Arfa tana tunasar da mu cewa rahamar Allah ta fi girman zunubanmu.
13. Ka yi sulhu da Allah a ranar Arfa, domin babu rabon da ya fi samun yardarsa.
14. Adduβar iyaye, hawaye na tuba, da zikiri a ranar Arfa β duk suna daga cikin taskokin da ba sa Ιacewa.
15. Ranar Arfa ba ranar wasa ba ce; rana ce ta neman gafara, rahama, da canjin rayuwa zuwa alkhairi.
π€² Allah Ya sanya mu cikin bayinsa na gari, Ya karΙi ibadunmu da adduβoβinmu. Ψ’Ω
ΩΩ
βοΈ Dr. Abdurrahman Sani Yakubu
25/05/2026
1.βKada ka bari kwanakin Zul-Hijja su wuce babu canji a rayuwarka. WataΖila wannan ce damar da Allah ya buΙe maka domin kusantar Sa.β
2. βAyyukan alkhairi a kwanakin Zul-Hijja sun fi daraja a wajen Allah fiye da sauran kwanaki.β
3.βKa cika bakinka da tasbihi, tahmidi da tahlili; domin kwanakin Zul-Hijja kwanaki ne na rahama.β
4. βWanda ya yi anfani da Zul-Hijja yadda ya kamata, zai girbi nutsuwa a duniya da lada a Lahira.β
5. βKar ka raina Ζaramin alkhairi a Zul-Hijja; wata kalmar zikiri na iya zama sanadin gafarar zunubanka.β
6. A kwanakin Zul-Hijja, ka gyara tsakaninka da Allah kafin ka nemi duniya ta gyaru gare ka.β
7. βYawaita istigfari, domin zukata suna rayuwa ne da neman gafarar Allah.β
8. βWanda ya rasa anfani da kwanaki goma na Zul-Hijja, ya rasa wata babbar kasuwa ta lada.β
9. Zul-Hijja wata dama ce ta sabuwar rayuwa ga mai neman gafarar Ubangiji.β
βοΈDr. Abdurrahman Sani Yakubu