06/08/2025
An bayyana matakan da Bello Turji ya dauka domin tabbatar da cewa da gaske ya ke kan alkawarin ajiye makamai da ya yi. Karanta cikakken rahoton a sashen sharhi.
Hoto: Defence Headquaters
06/08/2025
Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya fitar da gargaɗi mai tsanani ga dukkan jami’an gwamnati bayan murabus ɗin Kwamishinan Sufuri, Alhaji Ibrahim Namadi Dala, wanda ya yi murabus biyo bayan cece-kuce kan belin wanda ake zargi da safarar miyagun ƙwayoyi.
A cikin wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sunusi Bature Dawakin Tofa, ya fitar, Gwamna Yusuf ya bayyana haka ne yayin taron majalisar zartarwa na 30 da aka gudanar a gidan gwamnati a ranar Laraba.
Gwamnan ya jaddada cewa gwamnatinsa ba za ta lamunci duk wani hali da zai lalata ƙimar da ta gina ba, yana mai cewa duk jami’in da ya kasa riƙe amana ya fi dacewa da ya ajiye aikinsa.
Ya ce yaƙi da miyagun ƙwayoyi da sauran munanan dabi’u na daga cikin ginshiƙan gwamnatinsa, tare da gargadin cewa duk wanda aka samu da hannu kai tsaye ko a kaikaice wajen irin waɗannan laifuka zai fuskanci hukunci.
Gwamnan ya kuma yi kira ga masu rike da mukamai su gudanar da ayyukansu bisa gaskiya, rikon amana da kima, domin kare mutuncin gwamnatin da suke wakilta.
06/08/2025
Akasarin masu aikin gwamnati a Najeriya ba su da tarbiyya - Muhammadu Sanusi II
Ƙarin bayani: https://bbc.in/45oMnRJ