Alabbasiyya Qur'anic School Zaria
"The best of you is he who learns Alqur'an and teaches it’
11/06/2026
Masu Hidima ga Littafin Allah
Ya ku masu hidima ga Al-Qur'ani, Masu karatu da koyarwa dare da rana, Ku ne fitilun al'umma, Masu yada hasken shiriya a ko'ina.
Kun rungumi kalmar Allah, Kun sadaukar da lokaci da rayuwa saboda ta, Albarkar Al-Qur'ani na tare da ku, Kuma ladan Ubangiji na jiran ku.
Masu haddar Al-Qur'ani, masu koyarwa da masu aiki da shi, Ku ne taurarin shiriya ga al'umma, Allah Ya ƙara ɗaukaka ku, Ya sanya Al-Qur'ani hujja gare ku ba hujja a kanku ba.
إِنَّ الَّذِينَ يَتْلُونَ كِتَابَ اللَّهِ وَأَقَامُوا الصَّلَاةَ وَأَنفَقُوا مِمَّا رَزَقْنَاهُمْ سِرًّا وَعَلَانِيَةً يَرْجُونَ تِجَارَةً لَنْ تَبُورَ لِيُوَفِّيَهُمْ أُجُورَهُمْ وَيَزِيدَهُمْ مِنْ فَضْلِهِ ۚ إِنَّهُ غَفُورٌ شَكُورٌ
Ma'ana: “Lallai waɗanda suke karanta Littafin Allah, s**a tsayar da Sallah, kuma s**a ciyar daga abin da Muka azurta su da shi a asirce da bayyane, suna fatan wata kasuwanci wadda ba za ta taɓa yin asara ba. Domin Ya cika musu ladansu, kuma Ya ƙara musu daga falalarsa. Lallai Shi Mai yawan gafara ne, Mai yawan godiya (ga ayyukan bayinsa).”
09/06/2026
ALHAMDULILLAH! ALHAMDULILLAH!! ALHAMDULILLAH!!!
Muna farin cikin sanar da iyaye cewa, cikin ikon Allah, dalibai guda 7 sun samu nasarar kammala haddar Al-Qur'ani mai girma a wannan makaranta mai albarka.
Daliban sune kamar haka:
1. Zulaihat B. Salih
2. Maimuna Ahmad Sambo
3. Fatima Ibrahim
4. Aisha Qasim
5. Zainab Abubakar
6. Maryam
7. Marym
Haka kuma, muna taya Zulaihat B. Salih murna ta musamman bisa nasarar da ta samu na kammala Riwayar Shu'bah, bayan da ta riga ta kammala Riwayar Hafs a shekarar 2024.
Wannan wata babbar nasara ce ga wannan makaranta wanda ke nuna jajircewa, himma da dagewa wajen neman ilimin Al-Qur'ani.
Godiya ta musamman ga gwani Hussaini Hussaini bisa jajircewa da goyon baya da yake baiwa dalibai domin karkashin shi duka wainnan yara s**a kammala Haddansu, Allah ya saka mishi da alkhairi ya kuma jikan iyayenshi, Ameeen.
Godiya ta musamman ga iyayen wainnan dalibai bisa goyon baya da addu'o'i da kulawar da s**a nuna lokacin da yaransu ke wannan Hadda.
Muna roƙon Allah Ya sanya Al-Qur'ani ya zama hujja a gare mu, Ya albarkaci rayuwarmu, Ya ƙara mana ilimi mai amfani da aiki nagari.
Akwai wasu dalibai ma da suke gab da kammalawa wanda zamu sanar da ku da zarar sun kammala.
Barakallahu fihim wa fiina wa fiikum.
Mun gode.
Sanarwa: Mustapha Rabiu Bamally Mustapha Rabiu
19/05/2026
The C.E.O Alabbasiyya Qur'anic School Zaria, May Allah be with us in a all our affairs, Ameeen
14/04/2026
Assalamu Alaikum Warahmatullah
*NEMAN ADDU'A*
Amadadin dalibai da Malamai na wannan makaranta muna mika sakon gaisuwa da jajintawa bisa rashin lafiyan daya daga cikin dalibanmu.
Daliban mai suna HAUWA'U A RUFA'I tana asibitin shika tun kwanaki kadan da s**a wuce.
Don Allah muna baran adduoen iyaye da alumma gaba daya, muna rokon Allah ubangiji ya bata lafiya, Allah ya warkar da ita.
Daliba ce mai hazaqa da biyayya kwarai da gaske🥺
Allah ya bata lafiya.
Mun gode.
Sanarwa: Hukumar Makaranta
During our Hajj day.......
RABBI Taqabbal Minna
゚viralfbreelsfypシ゚viral
14/07/2025
Alhamdulillah! Sashin Matan aure na makarantan Alabbasiyya sun tabbatar da kammalawan SAUKAN ALQURANI NA DALIBAI GUDA UKU, DALIBAN SUNE SUKE SANYE DA FARAREN HIJAB.
Muna rokon Allah ya amsa, Ameeen Yaa Allah 🙏
Click here to claim your Sponsored Listing.
Location
Website
Address
Zaria