18/06/2025
*الحمد لله و احده، والصلاة والسلام على رسول الله وعلى آله وصحبه ومن تبعهم بإحسان إلى يوم الدين وبعد!*السلام عليكم ورحمة الله وبركاته*
*Ana sanarwa Yan Uwa Cewa* *Malam Aliyu Mamman حفظ الله* *zai cigaba da karatun da *yake gabatar wa a ranakun* *Alhamis* *Na littafin* *حقبة من التاريخ* *(HIQBATU MINAT-TAARIKH)* *daga* *Masallacin Marigayi* *MODIBBO LAMIDO رحمه الله تعالى*. *Dafatan Allah yabada iKon halarta Amin
Sanarwa daga komitin Masallacin Marigayi Modibbo Lamido Dake cikin Garin Yola
04/06/2025
LOKACIN SALLAH EDI NA LAYYA A CAPITAL SCHOOL JIMETA - YOLA NORTH, NA SHEKARAR 2025/1445 (EDIL KABIR).
Inshaa Allah Ranan Jumma'ah 6th June, 2025 za'a gatabar da Sallar Edi Babba a Capital School kamar Yadda aka Saba.
Wuri: CGDSS Jimeta - Yola North Adamawa State.
Lokaci: 8:00am
Rana: Jumma'ah 6th June, 2025 Inshaa Allah.
Allah ya Nuna mana da rai da lafiya, ya kuma bamu ikon halarta. Ameen
Sanarwa
Jibwis Adamawa
Jibwis Social Media, Adamawa State Directorate.
4th June, 2025
14/05/2025
SANARWA TA MUSAMMAN
GAGARUMIN WA’AZI A KASASHEN CAMEROON, TOGO DA GHANA
Karkashin jagorancin:
Sheikh Dr. Abdullahi Bala Lau
(Shugaban Kungiyar JIBWIS Nigeria)
(Shugaban Kungiyar Hadakar Ahlussunnah na Afrika ta Yamma)
Za a gudanar da babban wa’azi daga ranar Jumu’a 16/5/2025 zuwa Lahadi 18/5/2025 a manyan biranen kasashen Cameroon, Togo da Ghana.
Tare da manyan malamai kamar su:
Sheikh Muhammad Kabiru Haruna Gombe
Engr. Mustapha Imam Sitti
Sheikh Mukhtar Yola
Alaramma Nasiru Salihu Gwandu
Jadawalin wa’azin:
Ranar Jumu’a: Bude sabon masallaci a birnin Duala, kasar Cameroon
Jumu’a da dare: Wa’azi a dare a birnin Duala, Cameroon
Ranar Assabar: Gagarumin wa’azi a Lome, kasar Togo
Ranar Lahadi: Gagarumin wa’azi a Masjidu Taqwa, kasuwa, Freetown, Ghana.
15/04/2025
JAMA’ATU IZALATIL BID’A WA IQAMATIS SUNNAH, JIBWIS NIGERIA, ƙarƙashin jagorancin Sheikh Dr Abdullahi Bala Lau
Matsayinmu dangane da hukuncin da kotun ECOWAS ta yanke kan sashi na 210 da 382(b) na dokar hukunta laifuka ta jihar Kano da dokar shari’ar Musulunci (2000)
Jama’atu Izalatil Bid’a Wa Iqamatis Sunnah, JIBWIS Nigeria, ƙarƙashin jagorancin Sheikh Dr Abdullahi Bala Lau, na bayyana matuƙar damuwa da ƙin amincewa da hukuncin da Kotun ECOWAS ta yanke a ranar 9 ga Afrilu, 2025, wanda ke buƙatar gwamnatin Tarayyar Najeriya ta soke ko ta gyara sashe na 210 da 382(b) na dokokin jihar Kano.
Wannan hukuncin, wanda ke cewa dokokin sun ci karo da haƙƙin ɗan adam, tsoma baki ne da bai dace ba cikin ikon kasa na Najeriya wajen tsara dokoki, kuma karan tsaye ne kai tsaye ga tsarkin addinin Musulunci musamman a jihar Kano, inda kashi 99% na al’ummar Musulmi ne.
Muna so mu bayyana abubuwan nan kamar haka:
1. Goyon bayan kundin tsarin mulki:
Sashe na 38(1) na kundin tsarin mulkin Najeriya na 1999 (wanda aka gyara) ya bayar da haƙƙin walwala da bin addini. Wannan ya haɗa da ‘yancin aiwatar da dokokin addini bisa ga abin da mutum ya yi imani da shi. Bugu da ƙari, sashe na 4(7) na kundin tsarin mulkin ya baiwa majalisun dokoki na jihohi damar tsara dokoki akan abubuwan da s**a shafi laifuka. Don haka, ƙirƙirar dokar shari’ar Musulunci ta jihar Kano da sashe na 382(b) ya yi daidai da kundin tsarin Mulki kuma ya dace da hakki da kuma damar kirkirar dokar data dace da alada da addini ga gwamnatin Jahar Kano
2. Tsarkin Addini:
Sashe na 382(b) na dokar shari’ar Musulunci wanda ke hukunta wanda ya zagi ko ya ɓata suna ga Annabi Muhammad (SAW) da hukuncin kisa ya samo asali ne daga Alƙur’ani mai girma da sunnonin Annabi (SAW). Kare mutuncin Annabi Muhammad (SAW) wani ɓangare ne da ba za a taɓa sassauci da shi ba a cikin addinin Musulunci. Zagin Annabi ba ‘yancin faɗar albarkacin baki ba ne babban laifi ne da ke barazana ga zaman lafiya da ɗorewar dangantakar addinai.
3. Yarda daga Jama'a:
Dokar shari’ar Musulunci ba an ɗora wa mutane ba ne, sai da amincewa da kuma goyon bayan al’umma da tsarin dimokuraɗiyya da kuma kundin tsarin Mulki. Duk wani yunkuri na gyara ko soke dokar yana ƙetare ‘yancin addini da tsarin mulki na mutanen Jahar Kano.
4. Girmama bambancin addinai:
Haƙƙin ɗan adam na gaskiya da ƙa’idodin ƙasa da ƙasa suna buƙatar a girmama bambancin addinai da ikon al’ummomin addini. Hukuncin kotun ECOWAS maimakon ya kare haƙƙi yana ƙarfafa tada hankali da rushe tsarin dokokin addini da ke daidaita da tsarin tarayya na Najeriya.
Saboda haka, muna roƙon gwamnatin Tarayyar Najeriya da ta ƙi amincewa da wannan hukunci tare da kare ‘yancin addini da tsarin mulki na mutanen jihar Kano da sauran jihohin da Musulunci ya fi rinjaye. Muna kuma kira ga dukkan Musulmai da su zauna lafiya, su bi doka, kuma su ci gaba da aiwatar da addinin Musulunci kamar yadda Allah (SWT) ya umarta a cikin Alƙur’ani da yadda Annabi Muhammad (SAW) ya nuna a rayuwarsa.
JIBWIS Nigeria, ƙarƙashin Sheikh Abdullahi Bala Lau, ta tsaya daram wajen kare addininmu, dokokinmu da Annabi Muhammad (SAW), kuma za mu ci gaba da ƙin yarda da duk wani yunkuri ko kokari da ke neman wulaƙanta imanimmu da kimarmu a matsayin Musulmai a Najeriya.
Sa hannu:
Sheikh Abdullahi Bala Lau, Shugaba
Sheikh Muhd. Kabiru H. Gombe, Sakatare
Jama’atu Izalatil Bid’a Wa Iqamatis Sunnah, JIBWIS Nigeria.
Jibwis Nigeria
11/04/2025
WA'AZIN GORON SALLAH !🕋🕋🕋
Shugaban Ƙungiya Alh. Yusuf Muhammad Maigoro da shugaban majalisar malamai Sheikh Ali Mamman Shu'aibu da Shugaban Agaji Abubakar Sahabi (Sabo) na farin cikin gayyatarmu zuwa WA'AZIN GORON SALLAH wanda za a gabatar kamar haka :
RANA : Juma'ah 11/04/2025
WURI : 🕌Masjidu Bilal dake unguwar Rumde Chochi street.
LOKACI : Tsakanin Magrib da Isha'i 🕣
Allah yabamu ikon zuwa.
SANARWA !📢
Yusha'u Babayo
PRO JIBWIS ULAMA' COUNCIL YOLA NORTH.
11th, April, 2025
19/03/2025
Hotuna:
Shaikh Ali Mamman Shu'aib kenan, shugaban Majalisar Malamai JIBWIS Yola North a lokacin da yake gabatar da Ramadan Tafsir a FOMWAN dake nan cikin birnin Yola. Ramadan Day 19
Allah Ya ƙarawa Malam lafiya
14/03/2025
Hotuna
Wajen Tafsiri wadda Shugaba Shaikh Dr Abdullahi Bala Lau, Shugaban JIBWIS na ƙasa ke gabatarwa a Birnin Yola Jahar Adamawa tare da Alaramm Nasiru Gwandu.
Allah Ya ƙarawa shugaba lafiya da thabati
Jibwis Yola North