29/11/2024
NEWS:---
GOVERNOR AMADU OF SOKOTO STATE, WILL PAY A MINIMUN OF 70K AS THE LOWEST SALARY.
CONGRATULATIONS TO ALL SOKOTO STATE WORKERS.
YOURS!
Comrd Isma'ila Abubakar Isa
NUT Chairman, Isa Branch.
Juma'at! 20th, November, 2024
16/08/2024
ISA LGEA:—
DLS ISSUES, PLEASE 🙏 CONTACT 08088281340 OR
07087073782 FOR ANY COMPLAINTS.
THANKS 🙏.
20/01/2024
KIRA GA MALAMMAN FURAMARE NA MA’AIKATAR HUKUMAR ILIMI TA ISA LGEA…
Manzon Allah sallallahu alaihi wasallam yace “DUKKANIN KU MAKIYAYANE ZA’A TAMBAYE KU ABUNDA AKA BAKU KIYO A GOBE QIYAMA” Dayawan mutane suna yiwa wannan hadisin gurguwar dauka, wasu tunanin su kawai akan iyalin mutum ne, wasu kuma sun fahimce shi akan jagoranchi, koma dai ya muka doke shi mu sani Allah zai tambaye mu din ko shakka babu.
Cikin kashi 70 cikin 100 nadaga malamman furamare na ma’aikatar hukumar ilimi ta Isa, basu wuraren ayukkansu a halinda ake ciki yanzu, wannan abune karara ga hilin Allah!
Wasu suna unguwa (Chirani), wasu kuma suna cikin gari zanninsu dangal-gal! ba tareda sunje wuraren ayukkansu ba, dalillansu wai sunyi siyasar jam’iyyar Apc kuma tachi, yayinda wasu kuma ke ikirarin ai har yanzu kotu ake ba’ayanke shari’a ba b***e asan matsayin kowa.
Duk kuma wannan, rashin sanin darajjar ilimine da rashin kishin kasa tareda karanchin jin tsoron Allah!
A takaiche, matsayina na wakili ga dukkanin ma’aikatan (Malamman) hukumar ilimi ta karamar hukumar mulkin Isa, danku, kanenku, wasu kuma yayansu, ina kira ga wadanda s**a bar gari da niyar kasuwanchi ko neman kudi, kai harma da wadanda ke zaune gida ba tareda komawa wuraren ayukkansu ba, cewa dan Allah! da darajjar Annabi Muhammadu sallallahu alaihi wasallam, kowa yadawo wurin aikinsa dan tabbatar da ingancin ilimin yaran mu.
Ta fannin sha’anin samarda wal-wala ko jin dadin malammai, ba karya ba ko dadin baki, wannan gwamnati mai albarka, karkashin jagorancin mai girma gwamna Dr. Ahmad Aliyu Sokoto Fcna, insha Allahu zata farfado da darajjar ilimi da malammai a fadin jahar nan.
A yanzu haka, nan da ‘yan satukka kalilan, kowane asusun ajiya na malammai sai yaji kudaden da yaiyi shekaru bai ji su ba da yardar Allah! Haka zalika kuma, duk malaminda yaiyi karatun gaba ga sakandire sai ya amfanu da karatunsa matukar ya nemi takarardar karin girma (Promotion) koda kuwa yana rike da ta karshe ne.
Zamu kula tareda dokar matakin tsarin dokar aiki ga duk wanda yasso yiwa malami ba dai-dai ba (Chin hakkinsa) ko wanene insha Allahu! Haka zalika kuma ba zamu lamunchi duk malamin da zaiyi wasa da aikinsa ba ko wanene da yardar Allah!
Allah ta’ala yakara daukaka darajjar malami kuma yacilastawa mai girma gwamna akan gaggauta maida hankali kan malammai amin.
JIYA BA YAU BA………
Naku!
Comrd Isma'ila Abubakar Isa
NUT Chairman, Isa Branch.
Secretary, 23 Local Government NUT Chairmen Forum, Sokoto State.
20th January 2024
01/12/2022
AMADADIN MALAMMAN FURAMAREN HUKUMAR ILIMI TA ISA LGEA.......
Amadadin Qungiyar malamman furamare (NIGERIA UNION OF TEACHERS) da kuma s**ansu malamman furamaren na hukumar ilimi, reshen karamar hukumar mulkin Isa, muna matukar nuna alhinin mu, damuwa da kuma takaichin abunda yasamu dan uwan mu kana abokin aikin mu dake wannan ma'aika tamu ta LGEA, wato Comrd. "YUSUF B. AHMED" Bargaja, Principal kuma Auditor na NUT, wanda 'yan ta'adda makiya Allah s**a halba ga kafa akan hanyarsa ta dawowa daga wurin aiki.
Yusuf dai mutum ne jajirtacce akan aikinsa, kana kuma mutum ne mai neman nakansa dan biyan bukatar kansa data iyalansa, sai gashi ya hadu da iftila'i har yarasa kafarsa gabaki daya, muna jajintawa ahalinsa damu kan mu abokanin aikinsa, Allah ta'ala yakawo masa mafita kuma yabashi ikon cinye wannan jarabawar dan girman zati da Al'arshinka Allah!
Ya ubangiji kakawo muna dauki akan wadannan kaskantattu, fajirrai makiya Allah! tareda dukkanin wani mai hannu cikin wannan masifar, Allah kai ne Al'azizu! Allah kayi muna maganinsu dan soyaiyarka da ma'aiki s.a.w. amin.
Naku Akullum!
Comrd. Isma'ila Abubakar Isa
NUT Chairman, Isa LGEA.
02/12/2021
SANARWA TA MUSAMMAN GA MA'AIKATAN HUKUMAR ILIMI TA ISA (LGEA)......
Sanarwa ta musamman kuma mai matuƙar mahimmanci ga ma'aikatan mu na hukumar ilimi reshen ƙaramar hukumar mulkin Isa, wato "LGEA".
Kamar dai yada munka sani, gwamnatin jahar sakkwato ƙarƙashin jagorancin mai girma gwamna Rt. Hon. Aminu Waziri Tambuwal cfr. Matawallen sakkwato, tana kan gudanar da bin ciken ma'aikatanta dan tanttance halattattun ma'aikata da nuhin samar masu da jin daɗi nan gaba da yardar Allah!
Bin ciken dai kusan ince yanzu yayi nisa, ma'ana an kammala bin ciken ma'aikatan jaha yayinda ake kusan ƙarshen na ƙananan hukumomi ahalin yanzu, wanda shima dai kamar an kammala saidai matsalolin dake ciki, muna kuma fatan Allah ta'ala yabasu ikon gyara kura-kurran da acciki dan darajjar sunayen Allah tsalkaka amin.
Ahalin yanzu dai, mu ma ma'aikatan hukumar ilimin furamare "LGEA" bin ciken yazo kan mu, sannan kuma bin ciken yazo da salo daban dana baya, dan kuwa kusan irinsu ɗaya da wanda anka gudanar ga ma'aikatan ƙananan hukumomi, wato za'a bamu forms mai ɗauke da sunan kowane ma'aikaci dan cikewa.
Abubuwan lura da kuma la'akari anan, yanada kyau! ga kowane ma'aikaci yayi kokari bayanukkansa suzama iri ɗaya da kowace takarda, abunda nike nuhi anan shine, sunanka yayi dai-dai da sunan daka buɗa asusun ajiyarka dashi, shekarun haihuwar ka daka buɗe asusun ajiyarka, suma suzama dai-dai da shekarun takardar haihuwar ka, sai kuma sauran takar dunka da aka baka a ma'aikatar ka suma ka tabbatar da sunyi dai-dai da yanda yaddace suzama.
Tunatarwa, mu ma'aikatan hukumar ilimin furamare wato "LGEA" tabbas! muna da bam-bamci da sauran ma'aikata musamman na ƙananan hukumomi, haƙiƙa babu daɗi ko kaɗan kana ansar koda naira gudace ga wata Ace yau an wayi gari karasata, wannan ba ƙaramar hitina bace gaskiya, dan kuwa yakan iya jefaka cikin wani mugun yanayi musamman irin matsanan cin halin rayuwar da muke ciki ayanzu, lalle duk ma'aikacin da yassan ya tanadi waɗannan abubuwan dana lissafa Insha Allahu ta'ala bamu tunanin wata matsala atare dashi saidai ƙaddarowa ta ubangiji.
Muna fatan Ubangiji madaukakin sarki yashige muna gaba, duk abubuwan da zasu kawo muna cikas! Allah ta'ala yakuranye muna su, muna kuma rokon Allah daya hitar da 'yan uwan mu da daga cikin jarabawar rashin albashin da sunka shiga dan darajjar ANNABI MUHAMMADU S.A.W. Amin.
Wannan Saƙone daga mai girma jagoran ma'aikatar ilimi ta hukumar mulkin Isa Dr. Nuradeen Shehu Malami (Bunun Isa) ta hanyar Shugaban malammai na ma'aikatar ilimi ta Isa Comrd Isma'ila Abubakar Isa "NUT CHAIRMAN ISA LGEA"
Domin neman ƙarin bayani, ana iya tuntuɓar wannan lamba:--- 08088281340.
Allah ta'ala yaceci malamman furamare da sauran ma'aikata baki ɗaya amin.
Ya Ubangiji kakawo muna kwanciyar hankalin junan mu dama ƙasar mu baki ɗaya amin.
Naku Akullum!
Comrd. Ismaila Abubakar Isa
1st December 2021
15/05/2021
ZIYARAR BARKA DA SALLA DAGA QUNGIYAR MALAMMAI (NUT) A KOFAR GIDAN SHUGABAN KARAMAR HUKUMAR MULKIN ISA...
Qungiyar Malammai Reshen Karamar Hukumar Mulkin Isa, Nigeria Union Of Teachers (NUT), Karkashin Jagorancin Comrd Isma'ila Abubakar Isa, Sunkai Ziyarar Barka Da Sallah A Kofar Gidan Mai Girma Shugaban Karamar Hukumar Mulkin Isa Hon. Abubakar Yusuf Dan'ali Domin Tayashi Murnar Kammala Azumin Watan Ramalana Lafiya.
Yayinda Kai Tsaye, S**a Wuce Kofar Gidan Mai Girma Kwamishinan Tsaro Na Jahar Sakkwato Kanal. Garba Moyi Isa Mai Ritaya Domin Tayashi Murnar Zagayowar Babbar Sallah Lafiya.
Hakama Qungiyar Malamman, Tayi Tattaki Zuwa Gidan Mai Girma Shugaban Hukumar Ilimin Furamare Dama Na Sakandire Dr. Nura Usman (Bunun Isa) Domin Tayashi Murnar Ganin Wannan Babbar Ranar.
Alhamdulillahi! An Gudanar Da Addu'oi Na Musamman, Kamada Neman Saukin Halinda Muke Ciki Da Kuma Neman Hadin Goyon Bayan Juna Dan Ciyarda Kasa Da Al'umma Gaba.
Allah Ta'ala Yakarbi Ibadodin Mu Kuma Yakawo Muna Zaman Lafiyar Yankunan Mu Dama Kasar Mu Baki Daya Amin.
Naku Akullum!
Comrd. Ismaila Abubakar Isa
Jama'a Barkar Mu Da Sallah!
07/07/2020
HUKUMAR MULKIN ILIMI TA ISA, ISA LGEA NA CIKIN TASHIN HANKALI.....
La ilaha illa anta subahana inni kuntu minazzalumin!
Cikin bakin ciki da juyayi, muke sanarda ku itfila'in daya afkawa wasu daga cikin malamman mu na Isa Lgea adaren jiya litinin, kan hanyarsu ta dawowa daga sakkwato bayan kammala taron wayarwa jama'a kansu akan mahimmancin ilimin yaran mu.
Wadannan bayun Allah dai sun baro sakkwato da misalin karfe shidda da rabi na yamma, yayinda s**a biyo hanyarsu ta zuwa Isa, kwatsam! sai s**aci karo da miyagun hanya wato masu garkuwa da mutane, ba shiri b***e wata-wata kawai s**a bude masu wuta da halbin bindiga, Innalillahi wa inna ilaihi raji'un!
Mun samu asarar rayukka har guda biyu, Allah yajikansu da rahama, biyu kuma suna hannun wadannan miyagun mutanen, bayan mutane guda biyar da suke kwance dumu-dumu da raunukka ajikinsu, wadanda ahalin yanzu! Muna nan assibitin koyarwa ta jahar sakkwato dasu (UDUTH).
Alhamdulillahi kuma Insha Allahu muna kyautata masu kyakkyawan zaton suma zasu rayu da yardar Allah!
Muna matukar jinjina ga uwar Qungiyar mu ta jaha, karkashin kulawar Comr. Mai damma Alkammawa tareda hazikin gwarzon mataimakin sa Comrd. Babangida Nut, hakika wadannan jagororin namu, sun taka rawar azo agani dan ganin samuwar lafiyar wadannan bayun Allah!
Sai kuma jinjina ga mai girma SUBEB Chairman Hon. Shu'aibu Gwanda Gobir, bisa gudummuwar daya baiwa wadannan bayun Allah! Muna yimasa matukar godiya da fatan alheri, ubangiji Allah yasaka masa da mafificin alkhairi amin.
Indan jagoran ilimi na Isa Lgea, Dr. Nura Usman Malami (Bunun Isa) Abun saida yakusa taba lafiyarsa kasan cewar irin shakuwarsa da wadannan bayun Allah!
Daga karshe muna jinjinawa mai girma shugaban wannan Qungiyar mai albarka Comrd Isma'ila Abubakar Isa, akan hwadi tashin dayakeyi akan ganin samun lafiyar wadannan bayun Allah! tareda dukkanin ilahirin 'yayan wadannan Qungiyar tamu mai tarin albarka.
Allah ta'ala yasakawa jama'a da alheri, amin.