29/07/2022
‘KUNGIYAR ‘KWADAGO TA ‘KASA (NLC) TANA FAKEWA DA JAHILCIN AL, UMMA TA INGIZA SU YIWA GWAMNATI BORE
Ha’ki’ka gaskiya ne.Naijeriya ta ratta’ba hannu kan dokar ‘Kungiyar ‘Kwadago ta duniya (wato ILO) ta shekara 1998 mai ‘kudirori k**ar haka;
i) ‘Yancin kafa ‘kungiya da kuma ‘kulla yarjejeniya akan hakkokin ma,aikata
ii) Kawo ‘karshan duk wani aikin tilas da ake sa mutane
iii) Kawo ‘karshan aikin wahala da ake sa ‘kananan yara
iv) Cire banbanci wajan aiki da sana,a
Ba zai yiwu ayi amfani da wa’dannan ‘kudirori ba, ba tare da la,akari da dokokin ‘kasa ba. Kundin tsarin mulki na Naijeriya (wato Constitution) na 1999, shine mafi girman doka ta ‘kasa da ake amfani da ita.
Kuma sashi na 1(3) na wannan kundin ya tabbatar da cewa duk lokacin da wata doka da taci karo da wani sashi a wannan kudurin, to wannan doka jefar da ita ake.
Wasu ‘kudirori na kundin mulkin Naijeriya akan dokar ‘kwadago ta ‘kasa sune;
Sashi na 40 ya bawa ko wanne mutum ‘yancin shiga ‘kungiyar da ransa yake so, domin kare muradun sa.
Sashi na 45 ya ‘kwace wannan ‘yancin kai tsaye, idan ‘kudiri yaci karo da matsala ta tsaro, zaman lafiya, mutuncin al,umma wanda ya shafi ‘yanci da walwalar jama,a.
Ita kanta ‘Dokar ‘Kwadago ta ‘kasa, ta ta,alla’ka ne akan wannan sashi na 45.
Abin takaici shine, ‘kungiyar NLC ta maida kanta tamkar ‘kungiyar ‘yan sanda ta ‘kasa (wato Nigerian Police), inda take fidda dokoki, amma masu barazana wajan wargaza zaman lafiyar ‘kasa. A irin haka ne, shugabar ‘kungiyar ‘kwadago ta Jihar Legas, Mrs Agnes Sessy, tayi barazanar cewa, “idan Gwamnatin tarayya bata sasanta da ‘kungiyar ASUU ba cikin sati biyu, za,a yi mummunar zangazanga a ‘kasa, wacce zata mayar da zangazangar da aka yi ta “ENDSARS” wasan yara.
Wannan mummunan firice, wanda zai haifar da tashin hankalin da zai kawo ta’bar’barewar doka da oda. Dan haka Gwamnati tayi gaggawa wajan k**a wannan mata, a tuhume ta da laifin cin amanar ‘kasa.
Ina kira ga Gwamnati da ta saurari ASUU akan bu’katun da s**a shafi i) ‘Karin albashi da kyautata yanayin aiki na dukkan ma,aikatan Jami,a. ii) Biyan ku’da’dan alawus na ayyukan da malamai s**a yi.
Ban goyi da bayan Gwamnati ta yarda da matakin bawa malamai ‘kudurin biyan albashi da suke so a ‘dauke daga ofishin ‘Babban Akanta’ na Naijeriya zuwa ‘Hukumar Jami,o,i ta ‘kasa (wato NUC),wanda ake kira ‘UTAS’, domin yin hakan ya karya ‘kudurin cin gashin kai na Jami,o,i na shekara 2007 (wato, “2007 University Autonomy Act”).Wannan ‘kudurin, ASUU ta wahala ‘kwarai kafin Gwamnati ta sakar mata. To, yaya kuma ASUU za ta fito ta ya’ki ‘kudurin da ta sha wuya ta samo?
Wannan yajin aiki na ASUU, ya kawo matsaloli ainun ga ‘dalibai da iyayan su da su kansu malaman. Ga bayanin yadda wasu malaman s**a shiga cikin takaici sak**akon wannan yajin aikin;
- A wani rahoto na BBC Hausa, wasu malamai a Jami’ar Ahmadu Bello ta Zariya, sun shiga aikin leburanci domin biyan bu’katun su na yau da kullun, sak**akon matsalolin rayuwa da s**a shiga.
- Bayanin da wasu malamai s**a yiwa jaridar ‘Thisdaylive’
John Bardi (Malami a Jami,ar Benin):”Na dogara ne kacokan akan iyali na, wajan tallafi na ku’di. Na kar’bi bashi daga wajan abokai na, iyali na, da niyyar biyan bashin, idan an biya mu albashin mu da aka ri’ke. Tsofin ‘daliban mu, kuma abokai na suma sun taimaka min.”
Dr. Akpughe Ohenemudiaga (Malami a Jami,ar Benin): Rayuwa ba albashi, bata da sau’ki. Da farko, duk mun ‘dauka, yajin aikin ba zai da’de ba. Muna tunanin Gwamnatin tarayya ba zata bari ‘daliban Jami,o,in ta su wahala ba.”
Dr (Mrs.) Shalom Israel (Malami a Jami,ar Benin): “A yanzu dai rayuwa sai dai muyi rance da ro’ko. Wa’danda s**a fi shan wahala sune wa’danda suke kan magani – wato masu hawan jinni da ciwon s**ari. Ni kaina sai da na garzaya Minna wajan ‘yan uwa neman agaji. Kai sai da ta kaini da rancan ku’di a wurin wani ‘kanina rabaran na coci.”
Dr Tayo Popoola (Malami a Jami,ar Legas): “Muna nan muna rayuwa cikin ikon ALLAH. To, amma dole in fa’di gaskiya. Ba wani malamin Jami,a a yanzu da baya jin jiki, sak**akon tsayar da albashi da aka yi.”
A maimakon ASUU ta ci gaba da fito na fito da Gwamnati, ya k**ata ta zubar da mak**ai ta rungumin sulhu. Ta tattauna da Gwamnati akan ‘kuduranta muhimmai, domin ‘daliban mu su koma ajijuwan su.