Yadda Ake niyya guda daya ta azumin kwana 30.
_
Idan yaji labarin ganin wata. To idan lokacin sahur yayi, sai mutum yace : Ya ubangiji Nayi niyar yin azumin da ka umarceni na dukkan wannan wata, domin neman kusanci gareka.
Koda azuciya mutum zai iya fadi, ba sai ya furta da baki ba.
_
Idan mutum yayi wannan niya ta wadacesa duka watan, koda bacci ya kwashesa bai tashi lokacin sahur ba, dan yin niyyar azumi, to ita wannan niya ta kwana 30 da yayi ranar farko ta wadacesa. Amma babu laifi kullum lokacin sahur ya kara wata, idan kuma baiyiba azuminsa yayi.
ilimi kogi
Contact information, map and directions, contact form, opening hours, services, ratings, photos, videos and announcements from ilimi kogi, Education Website, maiduguri, Maiduguri.
KO CIWO BAYA HANA SALLAH BARE ......
In Aka Tashi Bacci Da Janaba, Kuma Lokacin Sallah Zaifita, Sannan Bazai Yuyu Ayi Wanka Ba, Saboda Tsoron Ciwo Ko Wani Abun Daban,
Wajibine Ayi Taimama Maimakon Wanka Ayi Alwala Ayi Sallah,
Inshima Alwalan Bazai Yuyuba Wajibine Ayi Taimama Maimakon Alwala Ayi Sallah.
= Haramunne Jinkirta Sallah A Lokacin Ta.
Duk wani haɗari da mutum ke shiga a wannan duniyar na ruɓewar jiki sabida rashin lfy shanyewarsa ko mummunar buguwa mai tarwatsa gaɓɓai ko tsinkewar jijiya ko hatsarin mota ko karaya ko bugawar zuciya ruɓewar ƴaƴan hanji kai duka waɗannan ha ɗurran da wasunsu walanda s**a fisu haɗari bas**ai haɗarin zunubi guda ɗayaba
Zunubi ƴan uwa yana rusa ɗan Adam yana lalatashi yana wulaƙantashi
Astagfirullahal Azeem.
ABU UKU BASU TARE DA TAƁEWA !
1-Wanda Yake Kyautatawa Iyaye Ba Zai Taɓa Taɓewa Ba !
2- Wanda Yake Yin Addu'a Ba Zai Taɓa Taɓewa Ba !
3-Wanda Yake Tare da Alƙur'ani Ba Zai Taɓa Tabewa Ba !
Ya Allah Ka Samu Cikin Masu Kyautatawa Iyaye Masu Yawaita Yin Addu'a Da Kuma Lizimtar Alƙur'ani A Rayuwar Mu Baki ɗaya.
TAMBAYA
Menene Hukuncin Wanda Yana Wankan Janaba Sai Yayi Wani Abunda Ke Karya Alwala, { Hadasi Ƙarami } Kamar Fitsari Ko Tusa Ko ....
AMSA
Ƙaramin Hadasi { Fitsari, Tusa, ... } Basu Ɓata Wankan Janaba Ko Waninsa, Koda Yayi Abu Mai Ɓata Alwala Wankansa Ya Inganta,
Saidai Wankan Janaban Da Hakan Yakasance Baya Dauke Alwala, Zai Kammala Wankansa Amma Inzaiyi Sallah Sai Yayi Alwala.
✍️ Sheikh Abdullahi Dahiru
Kashe ƙimar mutaneda zargi ko ɓata masu suna yafi kashesu da takubba.”
Saboda kisa yana kawo ƙarshen rayuwar mutum ta jiki, amma kisan mutunci yana kashe shi a zuciya da al’umma yana hana shi ɗaukar amana, ɗaukaka kalmar gaskiya, da kwanciyar hankali sabida shi Abun zargine a wurin mutane.
A taƙaice, zargi, ɓatanci da ƙarya su ne makaman masu rauni da marasa gaskiya. Su kan kashe mutunci da suna na mai gaskiya suna kiran mutane dasunaye mabanbanta.
A hakikanin gaskiya, duk wata tafiyar addini ko al’umma da ma’abotanta s**a fara rushe ƙimar junansu, s**a mayar da ɗan’uwa wanda yake da ra’ayi ko matsayi daban a matsayin abokin gaba kuma Abun tuhuma, to wannan tafiyar ta fara rushewa daga ciki.
Saboda ba za a sami masu ɗaukar amanar gaskiya da amincin ci gaba ba, idan aka kashe ƙimar masu gaskiya da zargi, s**a zama abin tsoro maimakon abin koyi
Idan mutun yazo da ra'ayi nadaban Ana tsayawane a saurara da kwakwalwar basira Abada Amsa ta hankali ga gareshi cikin ruwan sanyi zata iya yuwuwa rashin fahimtane daga gareshi kokuma shiya fahinci Abinda ba'a fahimtaba hakan yana ƙara bayyana gaskiyar tafiya da irin salon Annabawa wajan shiryarda mutane
Tafiya ba ta rushewa da ƙarfin makiya daga waje kaɗai amma da rashin adalcin ’yan cikinta da kashe juna da harshe da zargi.
TAMBAYA
Shin Yahalatta Mutum Yana Cikin Alwala Batareda Yagamaba, Kuma Bawai Yayi Wani Abu Mai Karya Alwala Bane, Yabar Wannan Alwalan Yasako Wata Alwalan Daga Farko. ?!
AMSA
Bai Halattaba.
✍️ Sheikh Abdullahi Dahiru
“Talaucin da yake cikin al’umma ba ƙaddarar Allah ba ce,
sakamakone na tsarin zalunci da ke hana masu haƙƙi hakkokinsu.
Adalcin da addinin Musulunci ya zo da shi ba ya tabbata da furuci kawai,
sai an kafa tsarin tattalin arziki da zai tabbatar wa talaka mutuncinsa,
kamar yadda yake ɗora wa mai arziki alhakin da ya rataya a wuyansa.”
Ayatullah Sayyid Shahid Muhammad Bāqir al-Ṣadr (Allah ya jiƙansa da rahama)
Sheikh Hussaini mukhtar
Tasirin kallon macen daba takaba a halinda bai hallata garekaba yafi tasirin buga ƙusa a cikin idanunka illa ga rayuwarka
Ko Ancire ƙusa makanta tana ragewa haka ko Angafarta zunubi tasirin wannan zunubi yana ragewa
Dan Gusarda wannan tasiri kana buqatar luɗufin ubangiji dakuna tasiri na Aikin Alkhairi da idanunka
Kallon fuskar malami dan soyayya gareshi sabida Allah yana daga cikin da malamai s**a Ambata sai kuna kallon rubutun Alkur'ani da kallon matarka ta halal kallon tausayi da ƙauna duka waɗan suna warkarda makantar sukuma gusarda tasirin.
Sheikh Hussaini mukhtar
TAMBAYA
Shin In Mace Tabar Farcenta Yayi Tsawo Hakan Zai Shafi Ingancin Alwalanta Ko Wankan Tsarki. ?
AMSA
Barin Farce Yayi Tsawo Bamatsala Bane, Saidai Intsawonsa Yawuce Yadda Aka Saba, To Dolene Tatabbatar Cewa Bawani Abunda Yamanne A Jikin Farcen Dayawuce Tsawon Yatsan, Wanda Zaihana Ruwa Isa Jikin Farcen, Kamar Dattin Dake Tatuwa Aqasan Farce.
✍️ Sheikh Abdullahi Dahiru
Click here to claim your Sponsored Listing.
Location
Category
Website
Address
Maiduguri