Ka saki kowa ka k**a Allah ya isheka komai
Subulas Salam Islamic School Umarari, Maiduguri
He who refuse to cut down the timber of illiteracy He would definitely die in the forest of ignoranc
27/01/2021
*WATAN ALLAH*
🌴BALLIGU ANNI no. 199🌴 02/Muharram/1441 (02/09/2019)
1. Wani mutum ya zo gurin Manzon Allah (s.a.w) sai yace: "Wane azumi ya fi falala bayan na Ramadan?" sai Annabi (s.a.w) yace: "(wanda akayi a) watan Allah da kuke kira da Muharram".
2. Manzon Allah (s.a.w) yace: "Mafi falalan azumi bayan Ramadan, shine (wanda akayi a) watan Allah na Muharram, kuma mafi falalan sallah bayan ta farilla itace sallar dare".
1. 📚 Sahihu Ibn Majah, Hadisi na 1427
2. 📚 Sahihu Muslim, Hadisi na 1163
👉🏼 Alhafiz Ibn Rajab (RH) yace: "Annabi (s.a.w) ya kira Muharram da watan Allah, sannan ya jingina watan ga Allah, wannan na nuna girma da falalan wannan watan, domin Allah ba'a jingina masa wani abu face zababbe daga cikin halittunsa".
📚 Lada'iful Ma'arif pg. 90-91
SAMUN LADA WADDA BATA DA IYAKA
Daga Ubbadatu bn Samit رضـي الله عـنه yace;
"Manzon Allah صـلى علـيه وسـلم yace;
*(Wanda ya nemawa masu imani maza da mata gafara,Allah zai rubuta ladar kyakkyawan aiki ga kowane mai Imani namiji da mace da ya nemawa gafara)*
@حـسنه الألبانـي فـي صحـيح الجامـع6020 مـجمع الزوائـد2101/10
الشَّيخ عَبدُ الرزَّاق البَدْر حفِظَهُ الله-:
Yana cewa;
"Kayi dubi ga wannan Rahama ta Allah da lada mai girma,idan musulmi ya fada acikin adduarsa;
*اللهـم اغفـر للمسـلمين والمـسلمات والمـؤمنين والمـؤمنات الأحيـاء منـهم والأمـوات*
Ya Allah kayi gafara da jin kai ga dukkan masu Imani maza da mata,masu rai da matattu.
Zai sami ladar ga kowane musulmi namiji da mace da ya roqawa gafara,ya da dana yanzu masu rayayyu da matattu.
Dan haka sai sami lada wadda bata da iyaka.
@فـقه الأدعـية والأذكار2/229
Ya Allah muna tawallasi da sunanka AL-GHAFFAR da Sunanka AR-RAHMANIR RAHEEEM ya Allah kayi rahama da gafara da jin kai ga dukkan Masu Imani maza da mata,masu rai da wandanda s**a rasu.
Allah ka biya masu buqatun su na alkhairi.
*اللهـم اغفـر للمسـلمين والمـسلمات والمـؤمنين والمـؤمنات الأحيـاء منـهم والأمـوات*
*Dr. Mansur Sokoto*✍🏻
,
*Bala'i* ya tashi zai yi tafiya, sai ya nemi abokin tafiya.
*Ciwo* ya ce zan bi ka. Bala'i ya ce ban yarda da kai ba. Domin kai da an sha magani sai ka bace, kuma wanda duk ka shafe shi, zai samu lada.
*Gobara* tazo ta ce za ta bi shi, sai ya ce, ban aminta da ke ba. Domin ke idan kin gama aiki sai a sake share wuri aci gaba da rayuwa.
Sai ga *Bashi* ya iso yana yi wa kansa kirari: Ni ke hana mutum barci, in hana shi zuwa masallaci, in sakar masa ciwo marar dalili, in sa shi karya da saba alkawari, in jefa shi gidan kaso, in ya mutu in gaji gidansa da iyalinsa, sannan ba zan barshi ba sai na tsaya da shi wurin hisabi a gaban Allah.,
Nan take Bala'i ya ce zo mu tafi tare, tabbas kai ne abokin tafiyata. Babu abokin tafiya in ba kai ba.
Ya *Allahu* Ya *Ar-razzaku* Ya *Al-wahhabu* ka raba mu da musibar bashi.
*HUKUNCIN YIN HARAMA DAGA TAN'IM (MASALLACIN NANA A'ISHA)*
*Tambaya*
Assalamu Alaikum
Malam Mun kammala aikin hajji, kuma har yanzu muna makka, Mun shiga sabon wata, shin zan iya kara yin UMARA? Nagode
*Amsa*
Wa alaikum assalam
Za ka iya yin sabuwar Umara, amma sai ka je Mikati ka dauko a zance mafi inganci, k**ar Zulhulaifah Mikatin mutanen Madina.
Tan'im (Masallacin Nana A'isha) ba ya cikin Mikatai guda hudu da Annabi (SAW) ya kayyade, wannan yasa irinka da ya yi hajji da Umara ba zai dauko Hajji daga wurin ba.
Duk da cewa wasu malaman sun halatta dauko Umara daga Tan'im, saboda hadisin Bukhari lokacin da Nana A'isha ta yi haila bayan ta yi niyyar Tamattu'i, Annabi (SAW) ya umarci dan'uwanta Abdurrahman ya kai ta wajan Haramin Makka ta dauko Umara saboda nuna damuwarta da ta yi na rashin samun Umara kebabbiya, Saidai ba'a samu sahabbai suna dauko harama daga wurin ba, hakan nan magabata nagari, hakan sai ya nuna hukuncin ya kebanta da ita da masu lalura irin tata.
Alhajin da bai samu maimaita Umara ba daga Mikati zai iya shagaltuwa da Dawafi da Addu'o'in neman gafara da Fatahi a wajan Allah.
Allah ne mafi sani.
*Dr. Jamilu Yusuf zarewa*
01/09/2019
*AZUMI NAWA AKE YI A WATAN MUHARRAM?*
*Tambaya:*
Don Allah malam azumi nawa akeyi a wannan watan ?
*Amsa:*
To 'yar'uwa ana so mutum ya zage dantse wajan yin Azumi a wannan watan, saboda fadin Annabi (SAW) : "Mafificin Azumi bayan Ramadhana shi ne Azumi a watan Muharram" k**ar yadda Muslim ya rawaito
Amma Wanda ya fi muhimmanci shi ne na ranar goma ga wata, sai kuma na ranar tara, Annabi S.A.W yana cewa: "Azumin ranar goma ga wata yana kankakare zunubin shekara daya" k**ar yadda Muslim ya rawaito a hadisi mai lamba ta: (1162), sannan yana cewa: "Idan na rayu zuwa badi zan azumci ranar ranar tara ga MUHARRAM".
Allah ne mafi sani.
31/08/2019.
*Dr. Jamilu Zarewa*
*ANA GINA RAYUWAR AURE NE AKAN GIRMAMA MIJI DA KIMANTA SHI!!*
*Tamabaya*
Assalamu alaikum Malam menene matsayin canjen abinci da mata keyi k**ar mijinta ya ajiye mata semonvita ita kuma tafison masara sai ta canza.
*Amsa*
Wa'alakum assalam, ya k**ata ya zama da iznin miji saboda hakan zai iya kawo rikici a tsakaninsu, tun da zai iya fahimtar rainuwa da rashin wadatar zuci.
Rayuwar aure tana tsayuwa akan girmama miji da nuna ba ki da sama da shi, da kimanta shi, Annabi ﷺ yana cewa inda zan umarci wani ya yiwa wani sujjada da na umarci mace ta yiwa MUJINTA sujjada.
Kamar yarda Ibnu Hibban ya rawaito a Sahihinsa a hadisi mai lamba ta: 4162 kuma shuaibu Al'arna'ud ya inganta.
Wannan yake nuna girman da muhimmanncin rashin Saba masa.
Allah ne mafi sani.
14/02/2017
*Dr. Jamilu Zarewa.*
28/08/2019
🌺 *ARIKA KAI ZUCIYA NESA {109}* 🌺
Bayan da Furai'ah ta kammala baiwa Nisreen labari, tare da dalilin da yasa ta dainayin social media gaba daya, sai Nisreen taja kuma ta hadiyi wani irin numfashi tace : _Hmmm, Allah ya kyauta._
Aka iso inda Furai'ah zata sauka, tayi godiya ga Nisreen sosai akan rage mata hanyar da tayi. Nisreen taja motar ta tayi gaba, amma inaa jikinta yayi sanyi tukin ma yana mata nauyi.
Sak**akon mutuwar da jikinta yayi, saboda labarin da Furai'ah taba ta akan Kawarta, Nisreen dai ta paka motar gefe, ta kafa goshinta akan sitiyarin motar tana ta nazari ita kadai tana cewa:
_" Wai yanzu ace komai aka dauko sai akan kawata Ruwaihah zai kare, irin abinda Raihaan tafadamin gashi kuma itama Furai'ah ta fada min haka, amma inajin abayane s**a santa da wannan halin, da kyar ne idan yanzu tana da shi saboda nidai banga wata alama ba."_
*"Nisreen dai kam ta kasayin karatun ta nutsu akan lamarin Ruwaihah, kodai shaidanune s**a zamto kawayenta sakamokon yin watsi da Azkaar da tayi."* _Allah ya kyauta._
_"Idan har mutum ya kauracewa yin Azkaar na safiya da maraice, da sauran mu'amilolinsa na yau da kullu, ya kauracewa sauraron maganar Allah da manzon sa, sai kuga shaidanun Aljanu da na mutane sun zama sune abokansa, kuma surika yin tasiri akanshi"._
Nisreen dai takara jan motar ta tawuce makaranta, ta makara Sosai amma ahakan dai ta tafi, kuma ta kasa amincewa da abinda Ruwaihah akace takeyi, saboda shaidanu sun fitsare mata kunnuwa ba ta jin gaskiya, da zuciyarta tayadda ba ta yarda da gaskiya. Allah ya kyauta.
Bayan ankwana biyu, Sai *Ummu Nisreen* ta hadu da Kawarta *Ummu Waraqa* (wacce ta taba neman agajinta akan ta bata yadda zatayi ta turawa fa NNufail sako) a wani wuri tace da ita:
_"Haba Ummu Waraqa, na turo miki sako akan kibani mafita amma shiru nakejin ki, k**ar na shuka dusa."_
*"Wato Ita Ummu Waraqa, ganin tayi gwamma ta zo su fattauna ido na ganin ido, ta bata shawarwari tare da tsoratar da ita Illar yin hakan, akan ce
*ZAN IYA AURAN JIKAR YAYATA ?*
*Tambaya*
Assalamu Alaikum, Allah yasa Malam yana cikin koshin lafiya. Malam Ina neman a warware mun wata matsala ne, Akwai aure tsakanina da jikar yayata? Wato dani da kakar yarinyan mahaifinmu daya.
*Amsa*
Wa alaikum assalam, Babu aure a tsakaninku mutukar mahaifiyarku daya da kakarta, saboda aya ta (23) a suratun Nisa'i ta haramta auran 'yar 'yar'uwa wacce kuke uwa daya ko uba daya ko kuma shakikai.
'Yar 'yar'uwa a wannan ayar ta hada da Jikarta da jikar jikarta har zuwa can kasa k**ar yadda malaman Fiqhu su ka yi karin bayani.
Don neman karin bayani duba babun NIKAH a Fiqhul Muyassar da tafsiran malamai ga aya ta (23) a Suratun Nisa'i.
Allah ne mafi Sani.
*Amsawa*✍🏻
*DR. JAMILU YUSUF ZAREWA*
19/08/2017
Click here to claim your Sponsored Listing.
Location
Category
Website
Address
Maiduguri