Nurul-Huda Islamiya Sabuwar Kofa

Nurul-Huda Islamiya Sabuwar Kofa

Share

To Educate Muslim Ummah

05/06/2026

Inna Lillahi Wa Inna Ilaihi Raji'un😭💔

​"Hukumar makarantar mu tana cikin babban alhini da jimamin rashin daya daga cikin hazikan dalibanmu..."
​ kuma jajirtacciyar malama mai koyar da ilimin Hadith da Fiqhu, wadda ta koma ga Allah a yau Juma'a bayan ta shafe tsawon shekaru biyu tana jinya.

​Shaidar Alherinta:💯😍
Muna shaida cewa ta kasance malama kuma daliba abar koyi. Ta kasance mai kyakkyawan hali, cike da kirki, da kuma fadin gaban da yake sanya ta kauda kai ga duk wani abin da aka mata. Ko a cikin tsananin jinyarta, ba ta kasance mai yawan korafi ba, sai ma nuna juriya da tawakkali ga Allah.

​Addu'ar Mu Gare Ta:🤲🏻😭
Muna rokon Ubangiji Allah ya karbi jinyar da ta yi a matsayin kaffara da kuma silar daukaka darajarta a gidan gaskiya. Ya Allah ka gafarta mata, ka haskaka kabarinta, ka sanya karatuttukan da ta koyar da wadanda ta koya su zama mata sadakatul jariyah. Allah ya hada mu a Aljannar Firdausi.🤲🏻📿

​Don Allah ku taya mu yi mata addu'a a wannan rana mai albarka ta Juma'a.

Maintenance... ✍️

05/06/2026

SANARWAR DAWOWA MAKARANTA 📣

​Hukumar makaranta tana sanar da dukkan malamai da iyayen yara cewa: Za a koma makaranta ranar Asabar, 6 ga watan Yuni, 2026.

​🤲 Allah ya dawo da kowa makaranta lafiya,

30/05/2026

Daga cikin abunda Allah ya jarabci ustazai mata, sanya hijab da niqab masu daukan hankali akan hanya 🫩

29/05/2026
27/05/2026

Warm greetings to the entire Muslim Umma on the occasion of Eid Mubarak.

24/05/2026

SANARWA! SANARWA!! SANARWA!!!

​Hukumar wannan makaranta na sanar da dukkanin malamai da ɗalibai cewa za a tafi hutun Babbar Sallah kamar haka:
​🔵 RANAR HUTU: Lahadi, 24 / 05 / 2026
(Daidai da 7 / 12 / 1447AH)
​🔴 RANAR DAWOWA: Asabar, 06 / 06 / 2026
(Daidai da 20 / 12 / 1447AH)

​Hukumar makaranta tana yi wa kowa fatan Sallah lafiya. Allah ya karbi ayyukanmu na alkhairi,

​EID MUBARAK! 🎉
Kullu 'Am Wa Antum Bi Khair! 🎉

18/05/2026

*GOMAN FARKON ZHUL-HIJJA, KAKAR ZIKIRI (1)*

An karɓo daga Abdullahi ɗan Umar Allah ya yarda da shi cewa, Manzon Allah sallallahu alaihi wa sallama ya ce: *"Babu wasu kwanaki (yini) da s**a fi girma a wurin Allah, sannan kuma ayyuka a cikinsu (na alkhairi) s**a fi soyuwa a gare Shi sama da waɗannan kwanaki goma (goman farko na Zhul-hijja), dan haka ku yawaita a cikinsu daga Hailala da Hamdala da Kabarbari"*. Imamu Ahmad ya fitar da shi, 5446.

Daga cikin salon yin waɗannan zikirai:
*اللهُ أكبرُ اللهُ أكبرُ، لا إلهَ إلَّا الله، واللهُ أكبر اللهُ أكبر، ولله الحَمد.*
* *الله أكبر الله أكبر الله أكبر، لا إله إلا الله، الله أكبر الله أكبر الله أكبر ولله الحمد.*
*An rawaito cewa Abdullahi ɗan Umar da Abu Hurairah* Allah Ya ƙara yarda a gare-su, sun kasance suna fita kasuwanni a kwanaki goman farko na Zhul-hijja suna Kabarbari, sai mutane su yi Kabarbari sakamakon jin ta su. Dan haka mu tunatar da juna wannan alkhairi.😊

*🖊Malama Zainab Ja'afar Mahmud.* Hafizahallah
1st Zhul-hijjah 1447A.H.

WhatsApp channel👇

https://whatsapp.com/channel/0029Vb8EE4lKgsNwnyI48h2f

page👇

https://www.facebook.com/profile.php?id=61588516355888

WhatsApp Group👇

https://chat.whatsapp.com/CH66YvhzjRD8ZoPVYDkWDJ?mode=gi_t

Want your school to be the top-listed School/college in Katsina?

Click here to claim your Sponsored Listing.

Location

Website

Address

Farin Yaro Quarters
Katsina
820101